Sashe 22
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daren data dawo mummy tayi kiranta
"Aisha...gobe da wuri nakeso ki tashi zamuyi baqi kaman sha daya na safe,a hada musu breakfast da dan sauran abun tabawa,duka kayan snacks na gidan nan sun qare tun tafiyarki,su lantana ba iyawa sukai ba haka freezer din ke zaune babu komai ciki....amma dai a soma wannan din daga baya kyayi na gidan baki daya"
"Toh" kawai tace ta miqe ta fice,tana mamakin yadda ko a fuska bata ga alamun mummy tasan meke faruwa ba,hutunta ba damuwarta bane bare tace ta huta tunda a yau yau din ta dawo daga tafiya,baqinta na gobe sune kawai damuwarta,zata iga ba zata iya ba,yata baro qauyen duka ba'a gabanta yake ba.
***************
Goma na safe ta kammala dukkan abinda ya kamata tare da taimakon lantana,a bakinta taji cewa magabatan hamid ne zasu zo neman auren asma'u,sun gama komai sun killace waje daya,tana shirin barin kitchen din asma'u ta shigo,sanye take da kayan bacci tana amsa waya murya qasa qasa,ko ba'a gaya mata ba tasan da hamid take wayar,a haka ta qaraso inda kayan suke killace ta soma bubbudawa tana gani daya bayan daya,kashe wayar tayi sannan ta dauki plate daya cikin ma'ajiyar farantai ta soma diban duk abinda taga yayi mata,aysha bata tanka ba tunda tasan ta gama nata,sai ta saka kai kawai ta fice ta bar mata kitchen din,a nan asma'u ta zauna ta cika cikinta,cikin ranta tana yaba dadi da tsaruwar girkin,saidai koda wasa ko sau daya bata taba daga baki ta furtawa wadda ke bautar ba.
Daga nan dakinta ta koma ta fesa wanka sa kwalliya,yau jinta take kamar mai yawo cikin duniyar sama,ji take duk duniya a yau babu wata halitta data kaita farinciki,mallakar hamid shine cikar mafarkin rayuwarta,ita kanta batasan irin son da take masa ba,bata kuma tsammaci zata so wani namiji irin haka ba.
Sha daya na safiya da minti bakwai motocin gidansu hamid suka soma jerin gwano a harabar gidan daddy,a sannan aysha na tsaka da karyawa,duk sa cewa ba wani abun arziqi take iya ci ba tub da can ma bare yanzu da maganar ta mata karan tsaye cikin rayuwarta,take kwana ta tashi da ita,kullum kwanan duniya maimaita shawarar mero take cikin zuciyarta,ko yaushe gwada yadda zata doshi daddy take,saidai har yanzu ta kasa samun qwarin gwiwa,dalili kenan da ya sanyata ta duqufa da yin istihara,don bata fatan ko dai dai da sau daya a rayuwarta ta biyewa son zuciyarta da zai sanyata nadama a gaba.
Iya motocin da suka jere kawai ya isa ya gaya maka lallai ba qananun mutane bane,irin buri da mafarkin asma'unne.
Kiran da mummy ke qwala mata ya sanyata aje cup din tea da tun dazun take qoqarin tursasa kanta taga ta shanyeshi kosa bata ci komai ba saidai yaqi tafiya,a hanzarce ta sauko ta tadda mummyn cikin kitchen tana duban kayan da asma'u ta bubbude ta diba
"Wanne irin abu ne haka?" Mummyn ta fada fana hade rai
"Anty asma'u ce ta diba" ta fada cikin sassanyar muryarta dai dai sanda asma'un ta sake dawowa tana naeman mummy cikina adon da tasha tamkar yaune bikin nata
"Wanne irin shashanci ne wannan,ayiwa baqi abu ki bude ki diba?,ce miki akai su qananun mutane ne.....lantana....ku dauka ku kai musu hakan tunda raini kikeson siya mana" a shagwabe ta dira qafa tana hade hannayenta waje guda
"Am sorry mummy....wallahi sha'awa suka bani shi yasa na diba"
"Ja'irar yarinya" ta fada tana jifanta da harara ita kuma tana dariya
"Aysha ku gyara kayan su lantana su dauka su miqa" ta fada tana juyawa ta wuce asma'u tabi bayanta,tsayawa tayi ta sake gyarawar kamar yadda ta umarceta sannan ta koma dakinta ta bar su lantana suna kwashe kayan zuwa babban falon baqi na gidan.
Zuwa azahar tana iya jiyo maganganun asma'u cikin farinciki,jifa jifa da maganar mummyn tana ta waya tana sanarwa,an kawo kudin asma'u naira miliyan daya,bakin mummy kam yaqi rufuwa,zallaf farincikinta yaqi ya qare.
*****************
Qarfe bakwai na daren ranar jirginsu ya sauka daga qasar china,ya tsuke yayi kyau sosai cikin suit dinshi baqaqe baki daya,idanunsa saye da sun glases daya sake fitar da hancinsa daga tsakiya,ga kuma sajensa daya kwanta yayi kyau ya sake fidda adon fuskar tashi,sati biyar din da yayi sai yaji kaman ya jima sosai baiga anninsa ba,hakan ya qara masa daukin zuwa ya ganta.
*****************
Tara na dare yana gaban anninsa,daga shi sai ita a parlourn,sau tari idan suna irin wannan zaman baka ganin kowa daga shi sai ita,saika rantse sa Allah shine auta ba sulaiman ba,tsabar shaquwa ce da qauna ta musamman da Allah ya sanya tsakaninsa sa ita fiye da duka sauran yaranta.
Abinci yake ci yana bata labarin yadda tafiyar tasu ta kasance har ya kammala cin abincin nasa wanda yayi dai dai da shigowar sulaiman cikin kwalliya da alamu daga wani waje ya dawo
"Daga ina kake haka?,ya zaku fita ku barta ita kadai cikin gida daga ita sai masu aiki?" Cewar khalipha
"Ban jima da fita ba ma,tunda ka tafi idan muka fita ita kadai take zama"
"Inasu amal din?" Ya tambaya yana dubanshi
"Washegarin tafiyarka suka tafi suma"
"Ohk....ohk..." Ya fada yana kada kai tare da hasashen wani abu,tabbas yasa ba yadda barewa zatayi gudu danta yayi rarrafe,saboda shi kenan suke zaune cikin gidan hakan ya sake tabbata ba domin mahaifiyarsa ba kaman yadda zeenart tasha nunawa
"Yanzun daga ina kake?" Khalipha ya fadabyana kurban tataccen ruwan inibi
"Ni yaya?" Ya fada yana shafa kanshi,murmushi anni tayi
"Kai din ga,nima so nake insan ina kaje" ta fada cikin salon zolaya
"Anni...kinfa sani...wata 'yar unguwa ce"
"Kadai fadi gaskiya....muhammadu idan bakai da gaske bafa 'yan uwanka zasu rigaka tashi....ya kamata dai ka maida kai,shekaru jaa suke,hakanan lokaci baya jira".maganarta ita ta sake tuna masa da case din daya tafi ya bari bai kashe ba
"Kwanan nan in sha Allahu anni....kici gaba da yimin addu'a" ya fada cikin sanyin murya,yana jin ya kamata ya kawo qarshen komai matuqar ya kashe wannan matsalar yana jin dama kawai zai bata ta zaba masa matar aure,yana da yaqinin ba zata zaba masa baragurbi ba,yana kuma saka ran cewa zaiyi dace.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*GA MAI BUQATAR SIYA ZATA TUNTUBI WANNA NUMBER*
0803811300
*DB*
15
Qarfe takwas da rabi na daren ranar yana tsaye farfajiyar gidan,cikin sanyin san nan mai cike da nutsuwa yake qarewa wajen kallo tamkar mai wani nazarin abu na daban,sanye da shadda wannan karon sabon dinki daya siya ready made fara qal wanda kudinta bazai wuce naira dubu takwas ba baki daya,saidai kayan sun masa kyau ainun,haka Allah ya halicceshi wani irin jiki ne da shi mai kyau,komai arahar kaya ya saka suna amsarsa.
"Ah,muhammad ya ka tsaya daga nan?,kaifa dan gida ne daga yanzu ko ka manta?" Daddy da yayo tattaki tun daga parlournsa ya fito tarbarsa yake fadin haka,murmushi khalipha yayi,sai yaji kunya ta kamashi,ya dan sadda kanshi qasa yana shafa qeyarsa
"A'aha....kodai ba wajena akazo bane na koma?" Ya fada cikin zolaya yana murmushi
"A'ah....a'ah daddy" ya fada cikin yanayin kunyar,yana tuna karamcin mutumin wanda ya sani tun wasu shekaru baya da suka shude,da alama har kwanan gobe haka yake yana nan da karamcinsa,ba abinda ya sauyashi
"Ba damuwa ma koba wajena aka zo ba,muje ciki mu gaisa tukunna" a baya yabi daddyn suka taka har zuwa cikin parlournsa,cikin girmama juna suka gaisa ya tambayeshi anninsa da jikinta,ya amsa mishi lafiya lau take yanzu
"Ina fata dai komai lpy babu wata matsala ko?" Nauyi da kunya suka hanashi furta dukkan abinda yayi niyya,duk wani plan dinsa sai yaji ya ruguje,ya nemi dukkan hanzarinsa ya rasa shi,sai a sannan ya dinga tuna waye daddyn,wane irin halacci yayi musu a rayuwa?,banda shi da ya tabbatar ya rasa anninsa,banda shi a wannan rana da tuni yanzu yana gidan prison,banda shi da tuni yanzu bai a wannan bigiren da yake kai a yanzu,zaiyi wuya ya iya furta masa buqatarsa,idan da amana ruwa bazai dafa kifi ba,kuma rama halacci sai dan halak,bashi da manta alkhairin mutum a gareshi komai qanqantarsa
"Babu daddy alhamdulillah"ya ambata yana son tursasawa kanshi amsar duk wata qaddara da zata fadowa rayuwarsa
"To ma sha Allah...ni bari na kira maka indon da kaina" ya sake fada cikin zolaya yana ciro wayarsa daga aljihu ya lalubi mummy yace ta turo ayshan falon baqi.
Lantana ce ta shigo ta shaida mata lokacin da take tashi saman abun sallarta bata kai ga ko ninkewa ba,hakanan ta samu faduwar gaba duk da batasan dalilin kiran ba,kwanaki biyun hankalinta ya soma kwanciya kadan saboda ganin babu ta inda maganar aurenta ta sake tasowa,kowa harkar gabanshi yake,abun sallar ta aje hakanan ta fito da hijabin sallarta a jikinta tana takawa a hankali cikin fargaba.
Cikin sanyin nan nata da nutsuwa ta kutsa kai falon muryarta dauke da sallama,dukkansu suka amsa saidai khalipha bai iya dagowa ya dubeta ba saboda taraddadin wace ce indo,gefe guda ta samu ta gaida daddyn da baqonsa,baqon da bai dago ya kalleta ba,koda ya dago din batajin zata gane wane
"Ga baqonki nan indo.....kinsan da zuwanshi kika barshi tsaye a waje?...next time idan kika sake saikin bani ladar shigo miki da shi" ya fada da tsokana cikin amonsa sannan ya miqe yayi hanyar fita yana cewa
"Toh malam muhammadu...a gaida gida"
"Na gode daddy" abinda ya iya cewa kenan daddyn ya fice a falon aka barsu iya su biyu,shuru na ratsa falon,kowa najin baqunta tattare da shi,kowa da abinda zuciyarsa ke kai komo a kai.
"Aisha...gobe da wuri nakeso ki tashi zamuyi baqi kaman sha daya na safe,a hada musu breakfast da dan sauran abun tabawa,duka kayan snacks na gidan nan sun qare tun tafiyarki,su lantana ba iyawa sukai ba haka freezer din ke zaune babu komai ciki....amma dai a soma wannan din daga baya kyayi na gidan baki daya"
"Toh" kawai tace ta miqe ta fice,tana mamakin yadda ko a fuska bata ga alamun mummy tasan meke faruwa ba,hutunta ba damuwarta bane bare tace ta huta tunda a yau yau din ta dawo daga tafiya,baqinta na gobe sune kawai damuwarta,zata iga ba zata iya ba,yata baro qauyen duka ba'a gabanta yake ba.
***************
Goma na safe ta kammala dukkan abinda ya kamata tare da taimakon lantana,a bakinta taji cewa magabatan hamid ne zasu zo neman auren asma'u,sun gama komai sun killace waje daya,tana shirin barin kitchen din asma'u ta shigo,sanye take da kayan bacci tana amsa waya murya qasa qasa,ko ba'a gaya mata ba tasan da hamid take wayar,a haka ta qaraso inda kayan suke killace ta soma bubbudawa tana gani daya bayan daya,kashe wayar tayi sannan ta dauki plate daya cikin ma'ajiyar farantai ta soma diban duk abinda taga yayi mata,aysha bata tanka ba tunda tasan ta gama nata,sai ta saka kai kawai ta fice ta bar mata kitchen din,a nan asma'u ta zauna ta cika cikinta,cikin ranta tana yaba dadi da tsaruwar girkin,saidai koda wasa ko sau daya bata taba daga baki ta furtawa wadda ke bautar ba.
Daga nan dakinta ta koma ta fesa wanka sa kwalliya,yau jinta take kamar mai yawo cikin duniyar sama,ji take duk duniya a yau babu wata halitta data kaita farinciki,mallakar hamid shine cikar mafarkin rayuwarta,ita kanta batasan irin son da take masa ba,bata kuma tsammaci zata so wani namiji irin haka ba.
Sha daya na safiya da minti bakwai motocin gidansu hamid suka soma jerin gwano a harabar gidan daddy,a sannan aysha na tsaka da karyawa,duk sa cewa ba wani abun arziqi take iya ci ba tub da can ma bare yanzu da maganar ta mata karan tsaye cikin rayuwarta,take kwana ta tashi da ita,kullum kwanan duniya maimaita shawarar mero take cikin zuciyarta,ko yaushe gwada yadda zata doshi daddy take,saidai har yanzu ta kasa samun qwarin gwiwa,dalili kenan da ya sanyata ta duqufa da yin istihara,don bata fatan ko dai dai da sau daya a rayuwarta ta biyewa son zuciyarta da zai sanyata nadama a gaba.
Iya motocin da suka jere kawai ya isa ya gaya maka lallai ba qananun mutane bane,irin buri da mafarkin asma'unne.
Kiran da mummy ke qwala mata ya sanyata aje cup din tea da tun dazun take qoqarin tursasa kanta taga ta shanyeshi kosa bata ci komai ba saidai yaqi tafiya,a hanzarce ta sauko ta tadda mummyn cikin kitchen tana duban kayan da asma'u ta bubbude ta diba
"Wanne irin abu ne haka?" Mummyn ta fada fana hade rai
"Anty asma'u ce ta diba" ta fada cikin sassanyar muryarta dai dai sanda asma'un ta sake dawowa tana naeman mummy cikina adon da tasha tamkar yaune bikin nata
"Wanne irin shashanci ne wannan,ayiwa baqi abu ki bude ki diba?,ce miki akai su qananun mutane ne.....lantana....ku dauka ku kai musu hakan tunda raini kikeson siya mana" a shagwabe ta dira qafa tana hade hannayenta waje guda
"Am sorry mummy....wallahi sha'awa suka bani shi yasa na diba"
"Ja'irar yarinya" ta fada tana jifanta da harara ita kuma tana dariya
"Aysha ku gyara kayan su lantana su dauka su miqa" ta fada tana juyawa ta wuce asma'u tabi bayanta,tsayawa tayi ta sake gyarawar kamar yadda ta umarceta sannan ta koma dakinta ta bar su lantana suna kwashe kayan zuwa babban falon baqi na gidan.
Zuwa azahar tana iya jiyo maganganun asma'u cikin farinciki,jifa jifa da maganar mummyn tana ta waya tana sanarwa,an kawo kudin asma'u naira miliyan daya,bakin mummy kam yaqi rufuwa,zallaf farincikinta yaqi ya qare.
*****************
Qarfe bakwai na daren ranar jirginsu ya sauka daga qasar china,ya tsuke yayi kyau sosai cikin suit dinshi baqaqe baki daya,idanunsa saye da sun glases daya sake fitar da hancinsa daga tsakiya,ga kuma sajensa daya kwanta yayi kyau ya sake fidda adon fuskar tashi,sati biyar din da yayi sai yaji kaman ya jima sosai baiga anninsa ba,hakan ya qara masa daukin zuwa ya ganta.
*****************
Tara na dare yana gaban anninsa,daga shi sai ita a parlourn,sau tari idan suna irin wannan zaman baka ganin kowa daga shi sai ita,saika rantse sa Allah shine auta ba sulaiman ba,tsabar shaquwa ce da qauna ta musamman da Allah ya sanya tsakaninsa sa ita fiye da duka sauran yaranta.
Abinci yake ci yana bata labarin yadda tafiyar tasu ta kasance har ya kammala cin abincin nasa wanda yayi dai dai da shigowar sulaiman cikin kwalliya da alamu daga wani waje ya dawo
"Daga ina kake haka?,ya zaku fita ku barta ita kadai cikin gida daga ita sai masu aiki?" Cewar khalipha
"Ban jima da fita ba ma,tunda ka tafi idan muka fita ita kadai take zama"
"Inasu amal din?" Ya tambaya yana dubanshi
"Washegarin tafiyarka suka tafi suma"
"Ohk....ohk..." Ya fada yana kada kai tare da hasashen wani abu,tabbas yasa ba yadda barewa zatayi gudu danta yayi rarrafe,saboda shi kenan suke zaune cikin gidan hakan ya sake tabbata ba domin mahaifiyarsa ba kaman yadda zeenart tasha nunawa
"Yanzun daga ina kake?" Khalipha ya fadabyana kurban tataccen ruwan inibi
"Ni yaya?" Ya fada yana shafa kanshi,murmushi anni tayi
"Kai din ga,nima so nake insan ina kaje" ta fada cikin salon zolaya
"Anni...kinfa sani...wata 'yar unguwa ce"
"Kadai fadi gaskiya....muhammadu idan bakai da gaske bafa 'yan uwanka zasu rigaka tashi....ya kamata dai ka maida kai,shekaru jaa suke,hakanan lokaci baya jira".maganarta ita ta sake tuna masa da case din daya tafi ya bari bai kashe ba
"Kwanan nan in sha Allahu anni....kici gaba da yimin addu'a" ya fada cikin sanyin murya,yana jin ya kamata ya kawo qarshen komai matuqar ya kashe wannan matsalar yana jin dama kawai zai bata ta zaba masa matar aure,yana da yaqinin ba zata zaba masa baragurbi ba,yana kuma saka ran cewa zaiyi dace.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*GA MAI BUQATAR SIYA ZATA TUNTUBI WANNA NUMBER*
0803811300
*DB*
15
Qarfe takwas da rabi na daren ranar yana tsaye farfajiyar gidan,cikin sanyin san nan mai cike da nutsuwa yake qarewa wajen kallo tamkar mai wani nazarin abu na daban,sanye da shadda wannan karon sabon dinki daya siya ready made fara qal wanda kudinta bazai wuce naira dubu takwas ba baki daya,saidai kayan sun masa kyau ainun,haka Allah ya halicceshi wani irin jiki ne da shi mai kyau,komai arahar kaya ya saka suna amsarsa.
"Ah,muhammad ya ka tsaya daga nan?,kaifa dan gida ne daga yanzu ko ka manta?" Daddy da yayo tattaki tun daga parlournsa ya fito tarbarsa yake fadin haka,murmushi khalipha yayi,sai yaji kunya ta kamashi,ya dan sadda kanshi qasa yana shafa qeyarsa
"A'aha....kodai ba wajena akazo bane na koma?" Ya fada cikin zolaya yana murmushi
"A'ah....a'ah daddy" ya fada cikin yanayin kunyar,yana tuna karamcin mutumin wanda ya sani tun wasu shekaru baya da suka shude,da alama har kwanan gobe haka yake yana nan da karamcinsa,ba abinda ya sauyashi
"Ba damuwa ma koba wajena aka zo ba,muje ciki mu gaisa tukunna" a baya yabi daddyn suka taka har zuwa cikin parlournsa,cikin girmama juna suka gaisa ya tambayeshi anninsa da jikinta,ya amsa mishi lafiya lau take yanzu
"Ina fata dai komai lpy babu wata matsala ko?" Nauyi da kunya suka hanashi furta dukkan abinda yayi niyya,duk wani plan dinsa sai yaji ya ruguje,ya nemi dukkan hanzarinsa ya rasa shi,sai a sannan ya dinga tuna waye daddyn,wane irin halacci yayi musu a rayuwa?,banda shi da ya tabbatar ya rasa anninsa,banda shi a wannan rana da tuni yanzu yana gidan prison,banda shi da tuni yanzu bai a wannan bigiren da yake kai a yanzu,zaiyi wuya ya iya furta masa buqatarsa,idan da amana ruwa bazai dafa kifi ba,kuma rama halacci sai dan halak,bashi da manta alkhairin mutum a gareshi komai qanqantarsa
"Babu daddy alhamdulillah"ya ambata yana son tursasawa kanshi amsar duk wata qaddara da zata fadowa rayuwarsa
"To ma sha Allah...ni bari na kira maka indon da kaina" ya sake fada cikin zolaya yana ciro wayarsa daga aljihu ya lalubi mummy yace ta turo ayshan falon baqi.
Lantana ce ta shigo ta shaida mata lokacin da take tashi saman abun sallarta bata kai ga ko ninkewa ba,hakanan ta samu faduwar gaba duk da batasan dalilin kiran ba,kwanaki biyun hankalinta ya soma kwanciya kadan saboda ganin babu ta inda maganar aurenta ta sake tasowa,kowa harkar gabanshi yake,abun sallar ta aje hakanan ta fito da hijabin sallarta a jikinta tana takawa a hankali cikin fargaba.
Cikin sanyin nan nata da nutsuwa ta kutsa kai falon muryarta dauke da sallama,dukkansu suka amsa saidai khalipha bai iya dagowa ya dubeta ba saboda taraddadin wace ce indo,gefe guda ta samu ta gaida daddyn da baqonsa,baqon da bai dago ya kalleta ba,koda ya dago din batajin zata gane wane
"Ga baqonki nan indo.....kinsan da zuwanshi kika barshi tsaye a waje?...next time idan kika sake saikin bani ladar shigo miki da shi" ya fada da tsokana cikin amonsa sannan ya miqe yayi hanyar fita yana cewa
"Toh malam muhammadu...a gaida gida"
"Na gode daddy" abinda ya iya cewa kenan daddyn ya fice a falon aka barsu iya su biyu,shuru na ratsa falon,kowa najin baqunta tattare da shi,kowa da abinda zuciyarsa ke kai komo a kai.