Sashe 69
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Atika ta samu a kitchen tana yunqurin hada abincin dare,da fara'a ta tari ayshan
"Habawa,shi yasa tun yau naji gidan ya saki,ashe uwar masu gida ce ta iso" dariya tayi tana zama kan kujerar dake kitchen din
"Baaba atika kina kaini inda banje ba"
"Ai gaskiya ce,na jima banga mutum kamarki ba,Allah ya baki dama kina gida kamar wannan amma baki dauki kanki a bakin komai ba,magana ta Allah ba ganin ido ba halayenki masu kyau ne"idanu ta lumshe,tana qissima inama ace ita da mahaifiyarta ke wannan hirar?,inama ace itace ke yabonta kamar haka?
"Allah ya sanyani na zama mafi alkhairin abinda kuke zato,kuma ina roqon Allah karya kamani da abinda kuke fadi....me zan samu baba banci komai ba"
"Yau dai sinasir na yiwa hajiya,kinsanta da son sinasir,zakici ko a dafa miki wani abun?" Kaita kada
"A'ah baba karki wahal da kanki,kai bawa duk abinda ka samu aici kake,bani sinasir din" murmushi baba atika ta saki ta soma zuba mata,halayyar aysha na burgeta qwarai,kusan tayi gadon anni(kira da jan hankali a gareku masu 'yan aiki a gida ko gurin aikin da kake da wasu a qarqashinka,abinda ke qarawa mutum girma farinjini da kwarjini shine ka nuna qasqantar da kai dakai da tawali'u a inda ka isa kuma kake da girma ka nuna kai ba mai girma bane dai dai kake da kowa dake wajen,wannan abun na qaramin qara soyayyarka yake a zuciyar na qasa da kai ba,kuma dabi'ace mai kyau,koyi ne da halin ma'aiki,yadda yaje zama cikin sahabbansa kai bakace shine ba banda haiba kwarjini cikar zati da kyan da babu mai yashi da Allah S W T ya bashi,Allah yasa mu dace).
A kitchen din ta cinye abincin tas,tana ci suna hira,muryar Aliya data jiyo a parlour ya sata fitowa,tana zaune suna hira da anni da alama bata jima da shigowa ba,amal na zaune gefensu tana chart saidai rabin hankalinta na kansu,bayan sun gama gaisawar anni ta miqe ta koma samanta ta basu waje,dab da aliya aysha ta zauna tana dala mata duka a cinya
"Autar mama....kinga yadda kika koma me mama ke baki kina cinyewa ke kadai saboda rashin amana koki ragen?" Dariya aliyan ta saki
"Wai don karna tambayeki shine kikai riga malam masallaci,me kuke ci a wudil,koda yake nasan aikin anni ne wannan,wannan ai saikisa angon ya kasa shaidaki idan ya dawo" baki aysha ta rufe da hannunta
"Wallahi sashen masharranciya ce ke"
"Errrrhmm....nikam inason tambayarki dama wanne mai kike amfani da shi yanzu,naga kanki kamar ba haka yake ba sanda kikazo gidan nan" cewar amal bayan tayi gyaran murya,duban jelar gashin ayshan take har tasa aliya ta kalla itama
"Ba wani mai,kawai na samu gidan gyaran gashi mai kyau ne"
"Kuma ma dai abun sa'a ne" aliyan ta fada ba tare data dubi amal ba,tunda aysha taga haka tasan neman magana ne ya motsa da biyu aliyan ta fada,kama hannun aysha tayi
"Muje ciki don Allah kisha labari" miqewa tayi suka wuce dakin ayshan,suna shiga aliyan ta dubeta
"Wai har yanzu wannan 'yan zaman kisan daben suna zuwa dama?" Baki ayshan ta tabe
"Eh,ina ruwanki dasu?" Dariya ta saki,tasan halin ayshan sarai da rashin son yin zancan wani
"Tabdi,ai wallahi da nice da tuni na saita musu hanya,suna zaune ina da miji kamar khalipha yana giftasu?" Dariya ta bata sosai saboda yadda ta gwada da hannunta,jan hannunta tayi ta zaunar bakin gado
"Ce miki akayi mijina ne,yayana ne" wata harara aliya ta watsa mata taja tsaki
"Kici gaba da fadin haka,kina zaune zw'a farauce miki shi zakice na gaya miki" dariya ce ta subucewa aysha ganin yadda aliyan ta haqiqance bilhaqqi,aliyan zata maida mata amsa ta katseta ta hanyar daga mata hannu
"Yi haquri anty aliya ina zuwa" ta fada tana dariya sannan ta fice ta samo mata abin motsa baki ta dawo
"rannan naje imam wali dubiya....kinsan wa na gani?" Kai aysha ta girgiza tana zubawa aliya lemo sannan ta miqa mata,amsa tayi tana qunshe dariya
"Wai asma'u a third gate tana jiran adaidata sahu,dama tana hawa motar haya a rayuwarta?" Aliya ta qarashe tana bushewa da dariya,kallonta aysha take sosai,labarin bai mata dadi ba saidai bata ma tunanin asma'un ce
"Anya ko sashen?,anty asma'un,kai hamid ma bazai barta ta hau abun hawa na haya ba" ta fada tana girgiza kai
"Wallahi karkiji zancan wasa ita ce,kinsan muna hada ido tayi maza ta dauke kao kaman bata ganni ba,nayi nayi mu hada ido amma taqi" zungurinta aysha tayi
"Kinga kisha lemonki,banson qarya,wai aliya yaushe kika baci da gulma"
"Allah indai gulmar asma'u ce saina kawo miki,don na tabbata itama tana maraba da taki da zata samu wanda zai kai mata,ban taba ganin mugu maqetacin mutum da baison ci gaban kowa ba sai ita" sai data kai nan ta kurbi lemon sannan ta aje
"Kinsan ma Allah labarin da nake ji cikin BUK?,wai reshe ya juye da mujiya,hamid gasata yake"
"Nikam.ban sani ba,Allah ya shiryeki sashen tunda haka kika koma" dariya take sosai,har ga Allah bawai tana jin dadin halin da ake rade radin asma'un na ciki bane,a'ah,sakayya da isharar da Allah ya soma gwada mata ne ta dace da ita,yadda asma'un tayi qaurin suna wajen wulaqanci da yanqwana jama'a a fadin makarantar,hakan ya sanya labarin halin data fada baiyi wuyar isa kunnuwan Al'umma ba,dama ance idan ka shuka alkhairi shi zaka tsinta a gaba,Allah ya bamu ikon aikata mai kyau.
Har akayi sallar magariba basu sani ba saida suka duba agogo sannan suka tashi sukayi,a nan aliya ke bata labarin soyayyar ta da mahmoud yake nema,duk da batasan mahmoud ba bata taba mu'amala da shi ba,amma ance idan kanason sanin waye mutum ka kallo abokinsa sai tayi mata fatan alkhairi ta kuma ji dadi har zuciyarta,har bakin gate ta rakota bayan anni tayi mata kyautar turare suka rabu suna begen juna.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Washegari ta tashi da gyaran sashen khalipha kamar yadda ta yiwa kanta alqawari duk asabar din qarshen wata idan tazo zata dinga yi.
Gyara na musamman tayi masa,ta share ko ina fes,tsayawa tayi tana kallon wajen yadda ya dauki qyalli tana maida numfashi,klien take buqata kuma babu sashen,don haka ta maida hijabinta ta kona sashen anni ta samo.
Da sallama ta shiga duk sai suka juyo suka kalleta,mus'ab dake saman dining ya gama cin abincin rana yana saukowa ya qarasa saukowa da dan gudu gudu zuwa wajen anni tun kafin ya qaraso yake cewa
"Suprise,suprise please anni" yana isa kusa da ita ya mata rada sannan yace da haidar
"Zomu tafi" binsu sukayi da kallo,sai da sukazo gab da aysha qasa qasa tace dasu
"Adai qulla alkhairi"
"Babban alkhairi kuwa zaki gani anty" cewar mus'ab,shidai haidar dariya yake suka rankaya suka fice,qarasowa tayi anni tace
"Sannu aysha,aiki dai aiki dai bakya gajiya,ki dakata hakanan ki samu abinci kici kiyi wanka maza" murmushi tayi
"Ai na kusa gamawa anni,klien zan dauka toilet kawai ya rage"
"To Allah yayi albarka,madalla"
"Amin anni" ta fada tana wucewa store don ta dauki klien din,a duk sanda annin ta sanya mata albarka tana jin dadi har cikin ranta,har cikin zuciyarta tana jin wani sanyi,sai taga kamar umminta ce.
Sai data ga komai yayi mata yadda takeso,don karambani har wasu abubuwan ta sauyawa waje sannan ta cire kayanta cikin bedroom ta daura guntun towel ta shiga wanka bayan ta bar duka sashen na fidda qamshin irin turarukan wutar da take siya wasu ta baiwa anni,wasu ta aje wajenta.
Fuskarsa qunshe da murmushi yake takowa zuwa sashen nasa,fes yake jin zuciyarsa,tunda ya shigo gidan fushin daya tsammaci gani wajen anni saiya samu akasin hakan,cike yake da zumudin yin wanka ya koma wajen anninsa kamar yadda ta hanashi zama yace yaje ya watsa ruwa tukun,don na qaramar rana ake ba ranar,sauqinta ma cikin raba yake amma duk da haka shima yana da buqatar watsa ruwan.
Ba wani shakka ko fargaba ta fito daga wankan abinta,ta isa gaban mudubi wanda yake kallon qofa ta baiwa qofar baya,ta zare ribbom din kanta ta tsiyayi mai ta soma shafawa kanta,hade haden mayuka ne wanda suka qarawa kanta kyau baqi da sheqi,ba wani kudi mai yawa ta kashe masa ba amma duk wanda ya kalli kan sai ya tsammaci da wani mai me tsada take amfani,tana shafawar tana rera waqar joeboy ta begining to fall in love jifa jifa,sai data tabbatar ya ratsa ko ina man ta feshe kan da turaren kai ta dauko comb ta soma tajewa.
Daddadan qamshin da falon keyi ya sheqa ya lumshe idanunsa,yasan aikin anni ne ita tasa aka masa wannan gyaran duk da baisan waye yayi ba,tasan yadda yakeson qamshi da tsafta wanda daga gareta ya gada,kyakkyawar jakar hannunsa ya aje saman kujera ya nufi bedroom dinsa,saidai dan motsin da yake jiyowa ciki sai ya bashi mamaki,a hankali ya dora hannunshi saman mabudin qofar ya tura qofar dakin.
_Ya Allah ka karemu daga sharrin mutum da aljan_🙏🏽
38
Farin bayanta yake iya gani wanda dogon gashinta ya sauka,tana ci gaba da tajeshi yana miqewa,da fari ya danyi mamaki yayi tsammanin jinnu ne sukeso masa yawo da hankali,saida ya saukar da idanunsa zuwa santala santalan cinyoyinta zuwa qafarta ya tabbatar ba aljana bace amma kuma wacece?,bai gama wannan tunanin ba ta ankara da mutum a bayanta can bakin qofa a tsaye cikin baqaqen suit,wani irin kadawa hantar cikinta tayi,ta zabura gami da qwalla qara ta shige bayi ta danna key tana karanto addu'o'in tsari,ba inda ajikinta baya rawa yana kakkarwa,kasa tsaiwa tayi saboda tsabar tsoro da rudewa saida ta samu gefan bathtube ta zauna,tuni hawaye suka fara tsatstsafo mata,yau ta shiga uku ta lalace,dama akwai aljannu a gidan?,don ta tabbatar tayi imanin babu mai shigowa inda take,bugu da qari ma waye zai iya shigowa dakin da tun daga falo ta sanya mauqulli har dakin gadon,saita barke da kuka mai sauti tana ci gaba da addu'a gami da qanqame jikinta waje daya.
Daga inda yake tsaye haushi ya cikashi taf,wannan wanne irin abu je?,daga ganin mutum shine zata wani zabura kamar taga aljani ta shige bandaki?,wai wace ma har ta samu lasisin shigo masa daki ta bararraje haka?,anya anni ta sani?,Allah yasa ba daya daga cikin yarancan bane da suke addabarsu da bibiyar rayuwarsu.
"Habawa,shi yasa tun yau naji gidan ya saki,ashe uwar masu gida ce ta iso" dariya tayi tana zama kan kujerar dake kitchen din
"Baaba atika kina kaini inda banje ba"
"Ai gaskiya ce,na jima banga mutum kamarki ba,Allah ya baki dama kina gida kamar wannan amma baki dauki kanki a bakin komai ba,magana ta Allah ba ganin ido ba halayenki masu kyau ne"idanu ta lumshe,tana qissima inama ace ita da mahaifiyarta ke wannan hirar?,inama ace itace ke yabonta kamar haka?
"Allah ya sanyani na zama mafi alkhairin abinda kuke zato,kuma ina roqon Allah karya kamani da abinda kuke fadi....me zan samu baba banci komai ba"
"Yau dai sinasir na yiwa hajiya,kinsanta da son sinasir,zakici ko a dafa miki wani abun?" Kaita kada
"A'ah baba karki wahal da kanki,kai bawa duk abinda ka samu aici kake,bani sinasir din" murmushi baba atika ta saki ta soma zuba mata,halayyar aysha na burgeta qwarai,kusan tayi gadon anni(kira da jan hankali a gareku masu 'yan aiki a gida ko gurin aikin da kake da wasu a qarqashinka,abinda ke qarawa mutum girma farinjini da kwarjini shine ka nuna qasqantar da kai dakai da tawali'u a inda ka isa kuma kake da girma ka nuna kai ba mai girma bane dai dai kake da kowa dake wajen,wannan abun na qaramin qara soyayyarka yake a zuciyar na qasa da kai ba,kuma dabi'ace mai kyau,koyi ne da halin ma'aiki,yadda yaje zama cikin sahabbansa kai bakace shine ba banda haiba kwarjini cikar zati da kyan da babu mai yashi da Allah S W T ya bashi,Allah yasa mu dace).
A kitchen din ta cinye abincin tas,tana ci suna hira,muryar Aliya data jiyo a parlour ya sata fitowa,tana zaune suna hira da anni da alama bata jima da shigowa ba,amal na zaune gefensu tana chart saidai rabin hankalinta na kansu,bayan sun gama gaisawar anni ta miqe ta koma samanta ta basu waje,dab da aliya aysha ta zauna tana dala mata duka a cinya
"Autar mama....kinga yadda kika koma me mama ke baki kina cinyewa ke kadai saboda rashin amana koki ragen?" Dariya aliyan ta saki
"Wai don karna tambayeki shine kikai riga malam masallaci,me kuke ci a wudil,koda yake nasan aikin anni ne wannan,wannan ai saikisa angon ya kasa shaidaki idan ya dawo" baki aysha ta rufe da hannunta
"Wallahi sashen masharranciya ce ke"
"Errrrhmm....nikam inason tambayarki dama wanne mai kike amfani da shi yanzu,naga kanki kamar ba haka yake ba sanda kikazo gidan nan" cewar amal bayan tayi gyaran murya,duban jelar gashin ayshan take har tasa aliya ta kalla itama
"Ba wani mai,kawai na samu gidan gyaran gashi mai kyau ne"
"Kuma ma dai abun sa'a ne" aliyan ta fada ba tare data dubi amal ba,tunda aysha taga haka tasan neman magana ne ya motsa da biyu aliyan ta fada,kama hannun aysha tayi
"Muje ciki don Allah kisha labari" miqewa tayi suka wuce dakin ayshan,suna shiga aliyan ta dubeta
"Wai har yanzu wannan 'yan zaman kisan daben suna zuwa dama?" Baki ayshan ta tabe
"Eh,ina ruwanki dasu?" Dariya ta saki,tasan halin ayshan sarai da rashin son yin zancan wani
"Tabdi,ai wallahi da nice da tuni na saita musu hanya,suna zaune ina da miji kamar khalipha yana giftasu?" Dariya ta bata sosai saboda yadda ta gwada da hannunta,jan hannunta tayi ta zaunar bakin gado
"Ce miki akayi mijina ne,yayana ne" wata harara aliya ta watsa mata taja tsaki
"Kici gaba da fadin haka,kina zaune zw'a farauce miki shi zakice na gaya miki" dariya ce ta subucewa aysha ganin yadda aliyan ta haqiqance bilhaqqi,aliyan zata maida mata amsa ta katseta ta hanyar daga mata hannu
"Yi haquri anty aliya ina zuwa" ta fada tana dariya sannan ta fice ta samo mata abin motsa baki ta dawo
"rannan naje imam wali dubiya....kinsan wa na gani?" Kai aysha ta girgiza tana zubawa aliya lemo sannan ta miqa mata,amsa tayi tana qunshe dariya
"Wai asma'u a third gate tana jiran adaidata sahu,dama tana hawa motar haya a rayuwarta?" Aliya ta qarashe tana bushewa da dariya,kallonta aysha take sosai,labarin bai mata dadi ba saidai bata ma tunanin asma'un ce
"Anya ko sashen?,anty asma'un,kai hamid ma bazai barta ta hau abun hawa na haya ba" ta fada tana girgiza kai
"Wallahi karkiji zancan wasa ita ce,kinsan muna hada ido tayi maza ta dauke kao kaman bata ganni ba,nayi nayi mu hada ido amma taqi" zungurinta aysha tayi
"Kinga kisha lemonki,banson qarya,wai aliya yaushe kika baci da gulma"
"Allah indai gulmar asma'u ce saina kawo miki,don na tabbata itama tana maraba da taki da zata samu wanda zai kai mata,ban taba ganin mugu maqetacin mutum da baison ci gaban kowa ba sai ita" sai data kai nan ta kurbi lemon sannan ta aje
"Kinsan ma Allah labarin da nake ji cikin BUK?,wai reshe ya juye da mujiya,hamid gasata yake"
"Nikam.ban sani ba,Allah ya shiryeki sashen tunda haka kika koma" dariya take sosai,har ga Allah bawai tana jin dadin halin da ake rade radin asma'un na ciki bane,a'ah,sakayya da isharar da Allah ya soma gwada mata ne ta dace da ita,yadda asma'un tayi qaurin suna wajen wulaqanci da yanqwana jama'a a fadin makarantar,hakan ya sanya labarin halin data fada baiyi wuyar isa kunnuwan Al'umma ba,dama ance idan ka shuka alkhairi shi zaka tsinta a gaba,Allah ya bamu ikon aikata mai kyau.
Har akayi sallar magariba basu sani ba saida suka duba agogo sannan suka tashi sukayi,a nan aliya ke bata labarin soyayyar ta da mahmoud yake nema,duk da batasan mahmoud ba bata taba mu'amala da shi ba,amma ance idan kanason sanin waye mutum ka kallo abokinsa sai tayi mata fatan alkhairi ta kuma ji dadi har zuciyarta,har bakin gate ta rakota bayan anni tayi mata kyautar turare suka rabu suna begen juna.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Washegari ta tashi da gyaran sashen khalipha kamar yadda ta yiwa kanta alqawari duk asabar din qarshen wata idan tazo zata dinga yi.
Gyara na musamman tayi masa,ta share ko ina fes,tsayawa tayi tana kallon wajen yadda ya dauki qyalli tana maida numfashi,klien take buqata kuma babu sashen,don haka ta maida hijabinta ta kona sashen anni ta samo.
Da sallama ta shiga duk sai suka juyo suka kalleta,mus'ab dake saman dining ya gama cin abincin rana yana saukowa ya qarasa saukowa da dan gudu gudu zuwa wajen anni tun kafin ya qaraso yake cewa
"Suprise,suprise please anni" yana isa kusa da ita ya mata rada sannan yace da haidar
"Zomu tafi" binsu sukayi da kallo,sai da sukazo gab da aysha qasa qasa tace dasu
"Adai qulla alkhairi"
"Babban alkhairi kuwa zaki gani anty" cewar mus'ab,shidai haidar dariya yake suka rankaya suka fice,qarasowa tayi anni tace
"Sannu aysha,aiki dai aiki dai bakya gajiya,ki dakata hakanan ki samu abinci kici kiyi wanka maza" murmushi tayi
"Ai na kusa gamawa anni,klien zan dauka toilet kawai ya rage"
"To Allah yayi albarka,madalla"
"Amin anni" ta fada tana wucewa store don ta dauki klien din,a duk sanda annin ta sanya mata albarka tana jin dadi har cikin ranta,har cikin zuciyarta tana jin wani sanyi,sai taga kamar umminta ce.
Sai data ga komai yayi mata yadda takeso,don karambani har wasu abubuwan ta sauyawa waje sannan ta cire kayanta cikin bedroom ta daura guntun towel ta shiga wanka bayan ta bar duka sashen na fidda qamshin irin turarukan wutar da take siya wasu ta baiwa anni,wasu ta aje wajenta.
Fuskarsa qunshe da murmushi yake takowa zuwa sashen nasa,fes yake jin zuciyarsa,tunda ya shigo gidan fushin daya tsammaci gani wajen anni saiya samu akasin hakan,cike yake da zumudin yin wanka ya koma wajen anninsa kamar yadda ta hanashi zama yace yaje ya watsa ruwa tukun,don na qaramar rana ake ba ranar,sauqinta ma cikin raba yake amma duk da haka shima yana da buqatar watsa ruwan.
Ba wani shakka ko fargaba ta fito daga wankan abinta,ta isa gaban mudubi wanda yake kallon qofa ta baiwa qofar baya,ta zare ribbom din kanta ta tsiyayi mai ta soma shafawa kanta,hade haden mayuka ne wanda suka qarawa kanta kyau baqi da sheqi,ba wani kudi mai yawa ta kashe masa ba amma duk wanda ya kalli kan sai ya tsammaci da wani mai me tsada take amfani,tana shafawar tana rera waqar joeboy ta begining to fall in love jifa jifa,sai data tabbatar ya ratsa ko ina man ta feshe kan da turaren kai ta dauko comb ta soma tajewa.
Daddadan qamshin da falon keyi ya sheqa ya lumshe idanunsa,yasan aikin anni ne ita tasa aka masa wannan gyaran duk da baisan waye yayi ba,tasan yadda yakeson qamshi da tsafta wanda daga gareta ya gada,kyakkyawar jakar hannunsa ya aje saman kujera ya nufi bedroom dinsa,saidai dan motsin da yake jiyowa ciki sai ya bashi mamaki,a hankali ya dora hannunshi saman mabudin qofar ya tura qofar dakin.
_Ya Allah ka karemu daga sharrin mutum da aljan_🙏🏽
38
Farin bayanta yake iya gani wanda dogon gashinta ya sauka,tana ci gaba da tajeshi yana miqewa,da fari ya danyi mamaki yayi tsammanin jinnu ne sukeso masa yawo da hankali,saida ya saukar da idanunsa zuwa santala santalan cinyoyinta zuwa qafarta ya tabbatar ba aljana bace amma kuma wacece?,bai gama wannan tunanin ba ta ankara da mutum a bayanta can bakin qofa a tsaye cikin baqaqen suit,wani irin kadawa hantar cikinta tayi,ta zabura gami da qwalla qara ta shige bayi ta danna key tana karanto addu'o'in tsari,ba inda ajikinta baya rawa yana kakkarwa,kasa tsaiwa tayi saboda tsabar tsoro da rudewa saida ta samu gefan bathtube ta zauna,tuni hawaye suka fara tsatstsafo mata,yau ta shiga uku ta lalace,dama akwai aljannu a gidan?,don ta tabbatar tayi imanin babu mai shigowa inda take,bugu da qari ma waye zai iya shigowa dakin da tun daga falo ta sanya mauqulli har dakin gadon,saita barke da kuka mai sauti tana ci gaba da addu'a gami da qanqame jikinta waje daya.
Daga inda yake tsaye haushi ya cikashi taf,wannan wanne irin abu je?,daga ganin mutum shine zata wani zabura kamar taga aljani ta shige bandaki?,wai wace ma har ta samu lasisin shigo masa daki ta bararraje haka?,anya anni ta sani?,Allah yasa ba daya daga cikin yarancan bane da suke addabarsu da bibiyar rayuwarsu.