Sashe 94
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Ke...wato saboda wuyanki yayi kauri kina ganin mutane baki iya musu sannu da zuwa ba ko?,kuma saboda rashin tarbiyya a gaban babarki amma bata tsawatar miki kota nuna miki rashin dacewar abinda kika aikata ba" abinda bai sani ba shine,ita kanta asma'un dama hanya take nema,saboda hama ta miqe a fusace cikin daga murya tace dashi
"Dakata hamid,karka sake kiran uwata saboda ita din ba sa'arka bace,sannan rashin tarbiyya aikao za'a tambaya wannan,tunda baka iya zama da matarka ba kaga kuwa daga wajen tsoho aka...." Bata kai aya ba ya wanketa da wani lafiyayyen mari
"Karki sake ki qarasa,wanda kike shirin zagi shi ya bada kudin da kika gani kika maqale min"
"Ni ka mara hamid?,...."
"An marekin ko kina da abinda zakiyi?"kai take kadawa kuka kamar zai qwace mata
"wallahi zakasan ka mareni,ka mari aurenka,yau saika sakeni,saika bani takardata" wata wawiyar dariya ya saki yana jan tsaki,komawa yayi ya zauna saman kujerar daya tashi a kai yana kwance agogon hannunsa mai tsada ya sanya hannunshi cikin abincinsa
"Aikin auru kenan har abada,idan ma kina mafarkin zan sakeki ne to kinyi kuskure,don ni ba shashasha bane,nasan ciwon kudina" daga haka yakai abincinsa baki ba tare daya sake bi ta kanta ba.
Dakinta ta shige cikin kuka ta dauko jakarta da mayafinta ta fito,ko kallonta baiyi ba,itama hakan yayi mata dadi,saidai bata gane manufar sharetan da yayi ba sai data je bude qofa taqi buduwa,sai daga bisani ta gane muqulli ya saka mata,dawowa tayi gabanshi cikin hargagi ta tsaya
"Ka tashi malam ka budemin qofa,don wallahi daga yau na gama aurenka na gaji"
"Ni kuma yanzu na fara aurenki wlh,don ba more komai cikin abinda na kashe miki ba" wani qululun baqinciki ne ya taso ya tokareta,me yake nufi kenan?,yana son yayi mata qwalelen rayuwar da ta shiryawa kanta samu a gaba?,yana nufin fa bazai saketa ba,wanda hakan dai dai yake da cewa haramiyarta rayuwar da takewa kanta hasashe.
51
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
A hankali yake ratsawa ta cikin layin nasu har zuwa qofar gidan da yake mallakinshi ne,kuma a halin yanzu yake zaune a ciki,yayi kyau sosai cikin qananun kaya wanda ya dira jibgegiyar rigar sanyi a kai,yana saka key yana shirin bude qofar gidan wayarshi tayi qarar shigowar saqo,basu jima da gama waya da anni ba wadda ta tashi zuwa saudiyya don tayi umara,wayar ya zaro daga aljihunsa yana dubawa,murmushi ya saki a hankali yana karanta abinda saqon ya qunsa,a qalla ya dauki wasu kwanaki bai.maida.mata da amsa,yayi kuma hakanne saboda ya auna yadda ta damu dashi,shin abinda zuciyarsa take raya masa haka ne?,wani irin yanayi da bai taba hasashen shiga irinsa ba akanta ya samu kansa,bashi da shakku kuma ko kokwanton cewa wannan ba komai bane soyayya ce,yadda yake ji din ya tabbatar da cewa ba qaramin kamu tayi masa ba,yaushe hakan ta kasance duka bazaice ba,yana tsoron kar yayi zurfi da yawa abun ya zame masa matsala,ya kasa samun goyon baya yadda ya kamata daga gareta.
Sosai saqon yayi masa dadi,don har ya shiga parlour din gidan maimaita karanta saqon yake yana murmushi kafin daga bisani ya samu wajen zama.
Daga bangarenta kuwa tana zaune gefan gadon anni bayan sun dawo daga rakiyarta airphort,wadda ta bar mata muqullin dakin nata a hannunta saboda ta tashi ne ran asabar sanda ayshan ke zuwa gida hutu,kasa aje wayar tayi daga hannunta sai juyata take tana jin wani iri babu dadi a ranta,batasan me yasa a duk sanda ta tura mishi saqo take kasa samun amsar sa ba,batasan dalili ba tana jin babu dadi sosai cikin ranta,ko wani laifi tayi masa?,damuwarta tana ganin ko bata rasa nasaba da qoqarin kyautata matan da yake yasa batason itama tayi masa wani abu da yake ba dai dai ba?,duk dai bata sani ba.
Gauruwar ajiyar zuciya ta sauke,jiki a sanyaye ta miqe ta soma kintsawa annin dakinta gami da gyara duk wani da tasan zai iya samun matsala kafin dawowarta,a qalla ta kusa kashe minti ashirin qwarara sannan ta sanya key ta kulle dakin ta sauko zuwa falon gidan.
Rahama,amal maryam harma da zeenrat dukkansu na zaune darshe darshe a falon,kowacce na sabgar gabanta kamar wadda ta samu gidan gyatuminta,hannun ayasha harde a qirji tabi kowaccensi da kallo ba tare da sun ankara ba,dukkansu mamaki suke bata,baya ga wani abu mai kama da haushi haushinsu da yake tasiei gami da mintsinarta can qasan ranta,saidai babu wadda ta taba nunawa haka cikinsu,saboda tana ganin nata da wannan hurumin.
Bata cewa kowa komai ba ta ratsasu zata shige,saboda kacokam amanar gidan anni ta danqa a hannunta ne,wanda hakan tasan ya bata ransu duk da basuyi magana ba,saidai fuskokinsu sun nuna,wani tsaki taji rahama ta ja,bata waiwayo ba bare ta nuna tasan da ita take,tunda suke sallama da annin take wani cika tana batsewa.
Cikin lambun gidan ta samu waje ta zauna,tana son yanayi da iskar wajen,ita kadai wajen shuru,jifa jifa tana tunanin rayuwa da abubuwa da dama da suka shude daga cikin rayuwarta,tun wancan sati taso ta sake zuwa gida taga daddy har ta gayama khalipha saidai bata samu zuwa ba,sabida wancan karon tun ranar lahadi ta koma makaranta saboda monday takwas na safe tana da lacture,ajiyar zuciya ta sauke ta soma danna wayarta,number din anty safiyya ta nema ta kirata,don sukanyi waya duk bayan wasu kwanaki,ko bata kira ta ba ita zata kira,bugu uku aka daga,murmushi ta saki saboda kukan al'amin daya fara yi mata sallama
"Me aka.yiwa dan gida na anty?" Cewar aysha tana murmushi
"Hmmm,rigima kawai yakeji aysha wannan dan gidan naki sai a hankali"
"A lallabamin shi al'amin baya kukan banza" dariya antyn tayi sannan suka soma gaisawa
"Kin shiga wajen daddy ne?jiya ban ganki ba inata tambayarki mummy bata cemin komai ba"
"A satin nan nakeson shiga"
"A'ah,karki cemin bakisan baida lpy ba,jiya fa a asiniti muka wuni daxu da safen ya koma gida" idanu ta fiddo cikin mamaki,don ita ba wanda ya gaya mata
"Me ya sameshi anty?,wallahi ban sani ba ba wanda ya gayamin"
"Wani irin zazzabi ne mai naci wlh sai da aka qara masa ruwa"
"Subhanallah,ai kuwa yau ba sai gobe ba zanje na ganshi,wallahi anty banda na kiraki mummy bata gayamin ba" ajiyar zuciya anty safiyya ta saki,wato har yau mai hali baya fasa halinsa kenan
"Allah ya kyauta,shikenan idan na samu dama nina zan shigo,idan ban shigo yau din ba sai gobe"
"To aunty,Allah ya bashi lafiya" suna kammala wayar ta miqe,hankalinta duk sai taji yaqi kwanciya,tana qaunar daddy kamar nata mahaifin,shine mutumin daya soma saka maqullin alkhairi ya budewa rayuwata dukkan wata qofa da a yanzu ta samu kanta a tsaye,kai tsaye cikin gida ta nufa ta isa sashensu,cikin qanqanin lokaci ta shirya tsaf,kana dubanta kasan ta samu dukkan wata dama ta rayuwa,duk aninda ke sanye a jikinta mai aji da tsada ne,har yau tana jin gajiyar kayanta dake jibge ne cikin gidanta wanda ita ka ta batasan iya adadinsu ba,saidai ba makeup ko daya a fuskarta.
Daya daga cikin muqullan motarta da anni ta damqa mata ne sanda zata tafi take mata fadan ajiyesu da tayi bata taba hawan ko daya ba,saita gangaro zuwa sashen annin,zuwa yanzu daga maryam sai amal da zeenart a falon,amal na kwance tana charting,maryam.na zaune tana kallo,yayin da zeenart ke riqe da kwanon farfesun kayan ciki wanda yake a mazaunin abinda za'a hada cikin anincin dare aci amma tsabar zalama da son zuciya da aka saba ta kasa jira,sam ta kasa zaman gidansu duk da jan kunnen da babanta yayi mata na kada ya sake ganin qafarta gidan annin tunda har khalipha ya wulaqantasu amma ta kasa jurewa,don tace ko dadin da take ci gidan annin ai babu a gidansu,ko iya shi ta samu ai ta more,qasa qasa amal ke kallon ayshan,tayi mata kyau komai nata mai aji da burgewa,duk abinda tayi saiya nuna maka ita din ta dabance mai ilimi da kuma aiki dashi,kitchen ta wuce ta tadda bara'atu daya mai aikin tasu,don inna atika da ita aka tafi umarar wannan karon,da fari anni cewa tayi yayi visa din mutum biyu bayan ita,ko amal da zeenart,ko amal da maryam din,ya amsa mata da to kawai,amma harga zuciyarshi baya jin zai iya cire kudinshi ya biyawa wata daga cikinsu zuwa saudiyya,kosu ko iyayen nasu,saboda haka kawai sai passport din ya aiko mata dashi da komai da komai na baba atika,dama ya jima yana son kai matar,saboda yadda anni kejin dadin zama da ita,uwa uba riqon amana da gsky,hakanan annin bata taba kuka da ita ba,itama annin data gani bata ce masa komai ba bare tayi qorafi,tasan wannan abubuwan da suka faru shekarun baya har yau ke tsikarinsa,ba abu bane na mamaki,dafi ne ko ace gubace da duk sanda ya tuna take taso masa,tama godewa Allah da yakanyi musu alkhairi lokaci bayan lokaci na abinci da sutura,don da fari yadda ya birkice bata zaci tsinkensa zai bari su mora ba,shi kuwa yayi hakane saboda darajar annin da umarnin data bashi wanda bazai iya tsallakewa umarninta ba,da shawara ce da da sauqi.
"Dakata hamid,karka sake kiran uwata saboda ita din ba sa'arka bace,sannan rashin tarbiyya aikao za'a tambaya wannan,tunda baka iya zama da matarka ba kaga kuwa daga wajen tsoho aka...." Bata kai aya ba ya wanketa da wani lafiyayyen mari
"Karki sake ki qarasa,wanda kike shirin zagi shi ya bada kudin da kika gani kika maqale min"
"Ni ka mara hamid?,...."
"An marekin ko kina da abinda zakiyi?"kai take kadawa kuka kamar zai qwace mata
"wallahi zakasan ka mareni,ka mari aurenka,yau saika sakeni,saika bani takardata" wata wawiyar dariya ya saki yana jan tsaki,komawa yayi ya zauna saman kujerar daya tashi a kai yana kwance agogon hannunsa mai tsada ya sanya hannunshi cikin abincinsa
"Aikin auru kenan har abada,idan ma kina mafarkin zan sakeki ne to kinyi kuskure,don ni ba shashasha bane,nasan ciwon kudina" daga haka yakai abincinsa baki ba tare daya sake bi ta kanta ba.
Dakinta ta shige cikin kuka ta dauko jakarta da mayafinta ta fito,ko kallonta baiyi ba,itama hakan yayi mata dadi,saidai bata gane manufar sharetan da yayi ba sai data je bude qofa taqi buduwa,sai daga bisani ta gane muqulli ya saka mata,dawowa tayi gabanshi cikin hargagi ta tsaya
"Ka tashi malam ka budemin qofa,don wallahi daga yau na gama aurenka na gaji"
"Ni kuma yanzu na fara aurenki wlh,don ba more komai cikin abinda na kashe miki ba" wani qululun baqinciki ne ya taso ya tokareta,me yake nufi kenan?,yana son yayi mata qwalelen rayuwar da ta shiryawa kanta samu a gaba?,yana nufin fa bazai saketa ba,wanda hakan dai dai yake da cewa haramiyarta rayuwar da takewa kanta hasashe.
51
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
A hankali yake ratsawa ta cikin layin nasu har zuwa qofar gidan da yake mallakinshi ne,kuma a halin yanzu yake zaune a ciki,yayi kyau sosai cikin qananun kaya wanda ya dira jibgegiyar rigar sanyi a kai,yana saka key yana shirin bude qofar gidan wayarshi tayi qarar shigowar saqo,basu jima da gama waya da anni ba wadda ta tashi zuwa saudiyya don tayi umara,wayar ya zaro daga aljihunsa yana dubawa,murmushi ya saki a hankali yana karanta abinda saqon ya qunsa,a qalla ya dauki wasu kwanaki bai.maida.mata da amsa,yayi kuma hakanne saboda ya auna yadda ta damu dashi,shin abinda zuciyarsa take raya masa haka ne?,wani irin yanayi da bai taba hasashen shiga irinsa ba akanta ya samu kansa,bashi da shakku kuma ko kokwanton cewa wannan ba komai bane soyayya ce,yadda yake ji din ya tabbatar da cewa ba qaramin kamu tayi masa ba,yaushe hakan ta kasance duka bazaice ba,yana tsoron kar yayi zurfi da yawa abun ya zame masa matsala,ya kasa samun goyon baya yadda ya kamata daga gareta.
Sosai saqon yayi masa dadi,don har ya shiga parlour din gidan maimaita karanta saqon yake yana murmushi kafin daga bisani ya samu wajen zama.
Daga bangarenta kuwa tana zaune gefan gadon anni bayan sun dawo daga rakiyarta airphort,wadda ta bar mata muqullin dakin nata a hannunta saboda ta tashi ne ran asabar sanda ayshan ke zuwa gida hutu,kasa aje wayar tayi daga hannunta sai juyata take tana jin wani iri babu dadi a ranta,batasan me yasa a duk sanda ta tura mishi saqo take kasa samun amsar sa ba,batasan dalili ba tana jin babu dadi sosai cikin ranta,ko wani laifi tayi masa?,damuwarta tana ganin ko bata rasa nasaba da qoqarin kyautata matan da yake yasa batason itama tayi masa wani abu da yake ba dai dai ba?,duk dai bata sani ba.
Gauruwar ajiyar zuciya ta sauke,jiki a sanyaye ta miqe ta soma kintsawa annin dakinta gami da gyara duk wani da tasan zai iya samun matsala kafin dawowarta,a qalla ta kusa kashe minti ashirin qwarara sannan ta sanya key ta kulle dakin ta sauko zuwa falon gidan.
Rahama,amal maryam harma da zeenrat dukkansu na zaune darshe darshe a falon,kowacce na sabgar gabanta kamar wadda ta samu gidan gyatuminta,hannun ayasha harde a qirji tabi kowaccensi da kallo ba tare da sun ankara ba,dukkansu mamaki suke bata,baya ga wani abu mai kama da haushi haushinsu da yake tasiei gami da mintsinarta can qasan ranta,saidai babu wadda ta taba nunawa haka cikinsu,saboda tana ganin nata da wannan hurumin.
Bata cewa kowa komai ba ta ratsasu zata shige,saboda kacokam amanar gidan anni ta danqa a hannunta ne,wanda hakan tasan ya bata ransu duk da basuyi magana ba,saidai fuskokinsu sun nuna,wani tsaki taji rahama ta ja,bata waiwayo ba bare ta nuna tasan da ita take,tunda suke sallama da annin take wani cika tana batsewa.
Cikin lambun gidan ta samu waje ta zauna,tana son yanayi da iskar wajen,ita kadai wajen shuru,jifa jifa tana tunanin rayuwa da abubuwa da dama da suka shude daga cikin rayuwarta,tun wancan sati taso ta sake zuwa gida taga daddy har ta gayama khalipha saidai bata samu zuwa ba,sabida wancan karon tun ranar lahadi ta koma makaranta saboda monday takwas na safe tana da lacture,ajiyar zuciya ta sauke ta soma danna wayarta,number din anty safiyya ta nema ta kirata,don sukanyi waya duk bayan wasu kwanaki,ko bata kira ta ba ita zata kira,bugu uku aka daga,murmushi ta saki saboda kukan al'amin daya fara yi mata sallama
"Me aka.yiwa dan gida na anty?" Cewar aysha tana murmushi
"Hmmm,rigima kawai yakeji aysha wannan dan gidan naki sai a hankali"
"A lallabamin shi al'amin baya kukan banza" dariya antyn tayi sannan suka soma gaisawa
"Kin shiga wajen daddy ne?jiya ban ganki ba inata tambayarki mummy bata cemin komai ba"
"A satin nan nakeson shiga"
"A'ah,karki cemin bakisan baida lpy ba,jiya fa a asiniti muka wuni daxu da safen ya koma gida" idanu ta fiddo cikin mamaki,don ita ba wanda ya gaya mata
"Me ya sameshi anty?,wallahi ban sani ba ba wanda ya gayamin"
"Wani irin zazzabi ne mai naci wlh sai da aka qara masa ruwa"
"Subhanallah,ai kuwa yau ba sai gobe ba zanje na ganshi,wallahi anty banda na kiraki mummy bata gayamin ba" ajiyar zuciya anty safiyya ta saki,wato har yau mai hali baya fasa halinsa kenan
"Allah ya kyauta,shikenan idan na samu dama nina zan shigo,idan ban shigo yau din ba sai gobe"
"To aunty,Allah ya bashi lafiya" suna kammala wayar ta miqe,hankalinta duk sai taji yaqi kwanciya,tana qaunar daddy kamar nata mahaifin,shine mutumin daya soma saka maqullin alkhairi ya budewa rayuwata dukkan wata qofa da a yanzu ta samu kanta a tsaye,kai tsaye cikin gida ta nufa ta isa sashensu,cikin qanqanin lokaci ta shirya tsaf,kana dubanta kasan ta samu dukkan wata dama ta rayuwa,duk aninda ke sanye a jikinta mai aji da tsada ne,har yau tana jin gajiyar kayanta dake jibge ne cikin gidanta wanda ita ka ta batasan iya adadinsu ba,saidai ba makeup ko daya a fuskarta.
Daya daga cikin muqullan motarta da anni ta damqa mata ne sanda zata tafi take mata fadan ajiyesu da tayi bata taba hawan ko daya ba,saita gangaro zuwa sashen annin,zuwa yanzu daga maryam sai amal da zeenart a falon,amal na kwance tana charting,maryam.na zaune tana kallo,yayin da zeenart ke riqe da kwanon farfesun kayan ciki wanda yake a mazaunin abinda za'a hada cikin anincin dare aci amma tsabar zalama da son zuciya da aka saba ta kasa jira,sam ta kasa zaman gidansu duk da jan kunnen da babanta yayi mata na kada ya sake ganin qafarta gidan annin tunda har khalipha ya wulaqantasu amma ta kasa jurewa,don tace ko dadin da take ci gidan annin ai babu a gidansu,ko iya shi ta samu ai ta more,qasa qasa amal ke kallon ayshan,tayi mata kyau komai nata mai aji da burgewa,duk abinda tayi saiya nuna maka ita din ta dabance mai ilimi da kuma aiki dashi,kitchen ta wuce ta tadda bara'atu daya mai aikin tasu,don inna atika da ita aka tafi umarar wannan karon,da fari anni cewa tayi yayi visa din mutum biyu bayan ita,ko amal da zeenart,ko amal da maryam din,ya amsa mata da to kawai,amma harga zuciyarshi baya jin zai iya cire kudinshi ya biyawa wata daga cikinsu zuwa saudiyya,kosu ko iyayen nasu,saboda haka kawai sai passport din ya aiko mata dashi da komai da komai na baba atika,dama ya jima yana son kai matar,saboda yadda anni kejin dadin zama da ita,uwa uba riqon amana da gsky,hakanan annin bata taba kuka da ita ba,itama annin data gani bata ce masa komai ba bare tayi qorafi,tasan wannan abubuwan da suka faru shekarun baya har yau ke tsikarinsa,ba abu bane na mamaki,dafi ne ko ace gubace da duk sanda ya tuna take taso masa,tama godewa Allah da yakanyi musu alkhairi lokaci bayan lokaci na abinci da sutura,don da fari yadda ya birkice bata zaci tsinkensa zai bari su mora ba,shi kuwa yayi hakane saboda darajar annin da umarnin data bashi wanda bazai iya tsallakewa umarninta ba,da shawara ce da da sauqi.