← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 92 OF 114

Sashe 92

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kai tsaye gidan gwaggo asabe ta yiwa dirvern kwatancen ya kaita,tunda suka shigi cikin garin ido ya dawo kansu,kafin kace meye wannan labarin indo tazo ya fara yawo.

Gwaggo asabe na cikin yin rude na tuwon dare sukayi sallama farfajiyar makeken tsakar gidan nata,wanda aka yiwa gidan wani gyara na musamman aka shafeshi da sumunti yayi mul gwanin sha'awa,fuskarta qunshe da wadatacciyar fara'a ta aje muciyar hannun nata ta miqe
"Wai wai wai,amaryar muhammadu yau a garin namu,lallai yau farar asabar ce" dariya aysha take sosai
"Kai gwaggo,kamar bani zuwa?"
"A'ah to wannan zuwa na yammaci haka?,yaushe rabonki da takan ma" ta fada tana yin gaba suka bita a baya zuwa rumfar dake gaban dakinta wanda ke shimfide da tabarma da alama bata jima da tashi ba akai,lale take musu wanda tana shirin tashi ta debo musu ruwa ayshan ta dakatar da ita,da kanta ta isa bakin randar gwaggon taba debo ruwan cikin kofin silba
"Wannan randa taki gwaggo da tsahon rai take,har yanzu kuma sanyi yake bata fasa ba"
"Ai 'yar amana ce wannan randa ni kaina na shaida...." Bata kai aya ba yara suka fara sallama dauke da kwalaye a kansu
"Wai gahi,kayan indo ne inji wasu mutane a waje a mota" kallonsu aysha take sanda take takowa riqe da kofin sulbar ta aje gaba hanan tana kallon kwalayen,dukkansu na kamfaninsu khalipha ne donga tambarin kamfanin nan rubuce baro baro a jiki,tana tsaye tana kallon ikon Allah sai da aka sauke kwalaye guda goma cif,jakarta ta bude ta dauko dubu daya ta baiwa yaran su raba,suka amshe suna godiya suka cilla suka fice a guje yayin data qarasa saman tabarmar ta zauna tana kallon kwalayen.

Sam batasan da kayan ba har suka zo garin,daga gaya mishi tafiyar kenan zuwa turosun da yayi har yasa aka sayi kaya irin wannan
"Wannan bawan Allah wannan bawan Allah akwai hannun alkhairi,bamu da abinda zamuce saidai ubangiji ya albarkaci aurenku,ya baku zuriyya ta gari,ya yalwata dukiya da arziqi" gwaggo asabe ke fadin haka sanda ta duba kwalayen taga kayan da aka nade da sunanta,dubanta hanan tayi da sauri jin gwaggo ta ambaci aurensu
"Aur...." Da hanzari aysha ta mata alama da ido kan tayi shuru don Allah,hakanan hanan ta hadiye maganar tana duban ayshan cikin mamaki,dama ayshan matar aure ce amma basu taba sani ba?,to meye dalilinta na boyewa?,haka taci gaba da duban ayshan cikin mamaki,wanda ta lura da hakan itama,dariyarta take ta dannewa kawai,don tasan yau za'a sha cakwakiya kam,nan gidan gwaggo sukayi sallar la'asar.

Tana saman abin sallarta taja waya ta soma neman number din khalipha,don tun dazun hankalinta na wajensa,tana son taji yanayin da yake ciki,saboda hanan na wajen da gujewa yawan tsiyar data shirya yi mata saita miqe ta fita daga dakin sanda wayar ta fara ringing.

Har zuwa sannan yana kwance rigingine saman gadon nashi dafe da kanshi,a lokacin ya jiyo qarar wayar saidai sam bashi da kuzarin da zai iya tashi bare ya daukota,haka ga qaraci ringing dinta ta gama,har wajen sau uku tana kira ba amsa,hakan ya sanya a sanyaye ta sauke wayar daga kunnenta ta rubuta masa gajeran saqo
_ya jikin naka?,ina fata dai lafiya,Allah ya qara afuwa yasa kaffara ne a gareka_

Sai data tabbatar yaje sannan ta juya don komawa ciki,sai taci karo da hanan dake tsaye harde da hannayenta tana kallonta
"Sannu mrs khalipha" dariya aysha ta sheqe da ita,don tasam cewa maganar nata cin hanan,don ba yadda zata yine yasa tayi shurh,qarasawa tayi ta kama hannun hanan din
"Me kike ci na baka na zuba?,abinda zamu kwana tare zaki ji komai"murmushi hanan tayi donta qagu taji labarin daga bakin ayshan,tana hango bala'in dacewar ayshan da khaliphan ne,ta hangi cewa wata iriyar soyayya ce ke riqe dasu duka su biyun mai tsayawa a rai
"Promise?" Ta tambayeta tana dariya dariya
"Nayi...muje mu qarasa gidan inna yelwa,itace ta haifi abbana"
"Uhmmm" hanan ta fada suna shigewa ciki.

Sanda suka fito da niyyar wucewa saitaga ashe dukka motocin na tsaye suna jiranta,cikin hanzari suka taso,mamaki ya rufeta,yanzu ashe dama wai suna tsaye,saita kasa shuru ganin kamar hakan bai dace ba,sam sai taji wani iri,suma fa mutane ne kamarta,ita din wace da za'a dinga bata wani tsaro da kulawa haka
"Ai da kunyi tafiyarku,idan yaso in zamu koma kwa zo ku maida mu,ai duka inda zanje ba mai nisa bane duk kusa suke da juna"
50

"duk yadda kika ce haka za'ayi madam,amma mu qarasa dake can gida"
"Shikenan" ta fada tana matsawa hanan ta soma shigewa sannan ta mara mata baya.

Tunda suka shigo layin mamaki ya cikata,saita kasa tantance gidan,don ba gidansu take gani ba,wani gida take gani mai dauke da ingarman katanga wadda duk girmanta mulmule take da sumunti da fenti mai kyau da daukar ido,sanda motar ta tsaya sanya kai kawai tayi cikin gidan cikin rashin qwarin gwiwa,don bata da tabbacin gidanne,hakanan bata da tabbacin jama'ar gidan har yau sune mazauna gidan.

Kamar ko yaushe mafi yawancin matan gidan suna qarqashin bishiyar da zamanta ga zame musu kamar al'ada,saidai a wannan karon bishiyar tafi kyau da qawata gidan fiye da lokutan baya,sakamakon siminti da aka yiwa ilahirin fadin gidan,sallamarta ita taja hankalin duk wanda ke zaune a wajen,gaba daya ido yayo kanta yayin da suka mimmiqe tsaye wasu sukayo gaba inda take
"A'ah,lale maraba sannu da zuwa"
"Maraba da matar allaji halifa"
"Sannunku da zuwa indo,indo mutanen birni"irin wadan nan kalaman dake nuna maraba da mutum su suka dinga furta mata,kowacce fuskarta wasai da fara'a,karo na biyu a rayuwarta da taga soyayya makamanciyar wannan.

Gaba daya suka dunguma dakin inna yelwa,wanda a yanzun ya zama babban falo da dakuna guda biyu a cikinsa,an sauya shi bayan gyaran da aka yi masa lokacin bikinsu,gaba daya mamaki ya cikata na waye ya iya irin wannan aikin a dukka gidan duk da kyau da yake dashi.

Tamkar inna yelwa zata goya ayshan haka ta rasa inda zata ajeta,kyakkyawar daddurma mai girma da taushi aka shimfide mata,kana ta umarci biyu daga cikin matan 'ya'yanta suje su dorawa ayshan wani abun
"karki wahalar dasu inna yelwa,mukam a qoshe muke"
"Ke ba irin cimar da kike zato bace" inna yelwar ta fada tana dariya,murmushi aysha tayi
"Allah mun qoshi inna,amma ban sani ba ko zuwa anjima"
"Toh ina zuwa" ta fada tana ficewa don ta bada sautu a samo mata fura da nono mai kyau,saboda ta sani indon mai son fura da nono ce a baya,saidai sum ranar kasuwa idan 'ya'yanta suka kawo haka za'a dama a rabawa kowa fana kallo bata da rabo duk yadda takai ga son furar,saidai ta sude a kofin wasu,sai tayi saurin kauda wannan tunanin daga zuciyarta,sau tari idan ta tuna saita dinga jin babu dadi ita kanta cikin ranta.

"Gaskiya aysha ke 'yar gata ce,kowa sonki yake?"
"Hmmm,hanan kenan" aysha ta fada tana dan qaramin murmushi,haka rayuwa take,a duk sanda kaga wani bawa cikin wata ni'ima saika yiwa kanka sha'awarta kota birgeka,harma wani lokaci ka yiwa kanka sha'awarta ba tare da kasan irin qalubalen daya fuskanta ba kafin yakai ga wannan bigiren.

Suna zaune aka kawo furar a dame an jefa qanqara a ciki ta dauki sanyi,bude faifan dake kai tayi,kallon furar tayi tana tuna wani lokaci can baya,sai taji gaba daya ta fice mata a kai bata bata sha'awa ba,saboda haka ta turawa hanan gabanta
"Bismillah sis kisha" ja hanan tayi gabanta ta soma shan abinta,ta mata dadi sosai saboda sanyi da suger data sha
"Ke bakya sha indo?" Inna yelwa ta tambayeta,murmushi kawai aysha tayi,a dacan baya wani lokaci daya shude,lokacin da take da buqatarta,lokacin da take sha'awa da qulafucinta aka hanata,hakan ya sanya a yanzu ma sam bata sha'awarta,bata baiwa inna yelwa amsa ba murmushi kawai tayi mata,sai jikin inna yelwan yayi sanyi,kwalin da tasa aka shigo mata dashi ta bude ta fidda tsarabar kowa ta lissafawa inna yelwan,fuskarta washe da fara'a take jerowa ayshan addu'a da fatan alkhairi,sai tayi zugudi kawai tana kallon innan,lafuzan da tunda ta budi ido tasan me duniya ke ciki bata taba jin makamancinsa a kanta daga bakinta ba,saidai ta jiyo akasin hakan
"Allah ya baki miji indo dan albarka,mijin da ina jin kaf zuriyata babu yarinyar da zata samu kamarshi,hannun kyayta Allah yayi masa,ki duba yadda duk wanda ke cikin gidan nan sai daya dandani arziqinki indo,ba shakka kedin mai qashin arziqi ce,ki qara masa godiya bisa aikin da yayi mana,ki duba kaf fadin karkarar nan babu gida ya namu dana kakanki salihu" mamakin khaliphan ya kamata,yaushe duka yayi wannan aikin?,cikin shi ko anni ba wanda ya taba nuna mata anyi ko a fuska,ya Allah,wadan nan wanne irin mutane ne masu kyakkyawar zucuya har irin haka da Allah ya hadata dasu?,dame ita kuwa ayshatu zata sakawa rayuwarsu?,khalipha...khalipha sunan data ringa maimaitawa kenan a ranta har zuwa wani lokaci,bayan hanan ta kammala sha suka nufi gidan mero.

Ta samu mai jego lafiya ita da yaronta,nan ta zauna suka kacame da hira,hirar da suka jima basuyi irinta ba,itama kwali guda ne na tsarabarta,itadai dukka mamaki take,waita yaya khalipha yasan kowa yasan kuma siyayyar data dace da kowa?,waye ya gaya mishi?.

Godiya mero ta dinga yi sosai,kaya ne turamen atamfofi da rigunan jariri masu kyau da tsada,hira suka dinga wadda suka jima basuyi irinta ba,sun tuna baya sosai,sun tuna abubuwa kala kala,na dadi da akasin haka,hanan kam tana waje suna hira da saddiq dinta,basu bar gidan meron ba sai qarfe kusan goma na dare,gidan inna yelwa suka koma,a sannan tuni har an saka musu shimfida,qatuwar katifa ce mai kyau da taushi da bargunan rufa.
Chapter 92 · 0% Book details