Sashe 30
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kamar ya karanci zuciyarta ya dan sake ja baya tare da bada wata tazarar a tsakaninsu
"Bansan da sunan da zan dinga kiranki da shi ba....saboda sunan mama na kenan" ya fada cikin nutsuwa,shuru ne ya biyo baya kamar yana jiran yaji abinda zata ce,hakanan itama bata ce komai ba saboda bata da abinda zata ce din...tsahon sakanni sannan ya dora
"Sai kikaji an kawo kudi ba tare dana sanar miki ko na nemi jin ra'ayinki ba" ya sake furtawa still idanunshi a kanta,yanzun ma shuru yaga tayi ba tare da tace komai ba bayaga motsa jikinta kadan da tayi gami da cewa
"Uhmmm"
"Duk da banji ta bakinki ba amma bata baci ba...idan ba zaki iya aurar mutum irina ba kina iya fada saboda 'yancinki ne....kin ganni talaka ne ni bani da komai sai rufin asirin Allah,bamai kudi bane ni haka nan ni ba wani bane.....naga ba irinmu asma'u keso ba ban sani ba kema ko ra'ayinku daya"
"Asma'u kace....kana magana ne kan yara masu gata...masu nasaba.....masu kudi....masu kyau...."
"Da ace kema duka kina da wadan nan zabinki zaizo dai dai da nata kenan?" Ya tari numfashinta ba tare daya bari ta gama fadin maganarta ba,kai ta kada
"Rufin asiri da mutunci shine biyan buqatata,da ace ina da 'yancin zabar kalar mijin da nakeso to miji na gari zan roqa....." Har cikin tsakiyar zuciyarsa kalaman ta suka sauka,sai yaji maganganunta sun burgeshi qwarai,yanayin yadda kalamanta ke a tsare kadai ya bayyana masa tsantsar nutsuwar da Allah ya mallaka mata,sai yaji yana son hirar tasu ta dore saboda haka yace
"Bayan kin samu miji na garin alal misali,taya zaki zauna da shi koda baku taba soyayya ba?" Shuru tayi tana juya tambayar tasa,itakam gaba daya soyayya ba matsalarta bace,abinda kawai ta sani shine mutunta juna,tausayi da jin qai,qauna ta haqiqa su take buqata,inama zata samu hakan?,take qiyastawa a ranta
"Soyayya Allah ne yake jefata cikin zukatan bayinsa,duk da ban dan danata ba amma nasan da haka,tunda na samu soyayyar inna laraba da Aliya ba tare da sun zamo jinina ba....amma mutunci da karamci sanin qima suna daga cikin jigon dake riqe zaman tare" baisan sanda murmushi ya subuce masa ba,ta iya magana ta hikima taqaitacciya kuna dunqulalliyar dake isar da saqo a dan qaramin lokaci
"Humaira.....zan kiraki da shi idan babu damuwa.....daga sanda aka daura mana aure sunanmu miji da mata a idon duniya....."katseshi tayi
"Ina mamakin ta yadda zaka iya aure na wai....." Girgiza kai take duk da ba dubansa take ba
"Kada ka yaudareni kada ka yaudari kanka.....ba aurena zaka iya ba...." Qaramin murmushi ya sake
"Ni dake gaba daya lamarinmu na hannun ubangiji,bamusan yadda zaiyi ba....ban taba kawoki cikin qaddarata ba kamar yadda kema nasan hakan ne.....bazan boye miki ba,hajiyata ita ta yimin izini neman aurenki,wanda na tabbata ta hangi abinda mu kanmu babu lallai mu hangeshi" shuru tayi tana jinjina qarfin hali da jarumta irin na mahaifiyar tasa,ita a karan kanta hankalinta da shekarunta da iya abinda take gani tasan uwa na nufin wani abu mai girma a rayuwar dukkan wani abu mai rai,duk da cewa ita din batasan dadin hakan ba amma tasan ita din ba qaramin abu bace....
"Zaki iya rayuwa da talaka?"ya sake fada yana katse mata tunaninta
"Ni din wace?"
"Hajiya ce mana" ya fada yana murmushi,itama batasan sanda siririn murmushi ya qwace kan fuskarta ba,abinda ta jima rabonta da shi,sai kuma ta maida fuskarta ta gintse,miqewa yayi tsaye yana zuba hannayensa cikin aljihunsa sannan ya sake cewa
"Daddy ya saka rana gashi ni kuma ban shirya ba,infact ma ban soma shiri ba,kinsan abun talaka,lefe ma kawai aiki ne a wajenmu....ga wajen zama....toh..Allah muna gareka" ya fada yana dan daga kanshi sama,murmshi ta saki,ita din daba kowan kowa ba,ita din da aka cusa masa,ita ayshan daba wani gata ba,ita dinma tana ga Allahn,bata ga abinda zai damu kanshi ba akai wai wani lefe da wajen zama,tana daga kai suka hada ido da shi,ya jima yana dubanta ya kuma.karanceta tsaf ba tare data sani ba,sai ya dauke idanun nasa yana jin tausayinta,har ya danyi gaba sai ya dawo ya dauki lemon,irin lemonsa ne da yake yawan sha
"Bari naji zan iya shan kalar wannan,kinsan abinka da baka saba ba" ya fada yana kurbar lemon,bai aje ba sai daya shanye sannan ya aje cup din
"Zan wuce gida.....amma ba lallai ki sake gani na nan kusa....saboda muna tare da oga koda yaushe....kinsan qarqashin wani nake" yayi shuru yana jira ko zata ce wani abun a wannan gabar,saidai babu abinda tace illa
"Karka takura kanka....."
"Ki gaida mutanen gidan"ya fada yana takawa zai bar wajen
"Ka gaida hajiya" ta furta ba tare data shirya ba,sai data fada din sai kuma tayi shuru tana raba ido kanta a qasa,tana jin kamar tayi azarbabi,gabanta na faduwa sanda taji tsaiwarsa,zuciyarta na kwabarta na ta cika azarbabi da yawa
"Zataji na gode" ya fada har cikin zuciyarsa yaji dadin kulawar data nuna.
_ina godiya a gareku,kuci gaba da yimin uzuri kan yanayin gajeran typing don Allah,na gode_
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300
*KO KUMA*
07067124863
*DB*
19
Cikin sati hudu mummy ta soma shirye shiryen bikin 'yarta don bana ce shirin bikinsu ba,ta bangaren aysha sam babu abinda ya dameta,kallon komai ma take a matsayin almara,har sannan gani take koda yaushe ma muhammad kamar yadda tafi kiransa,duk da cewa cikin ranta ne bata taba kiransa a sarari ba zai janye shima,bata taba duba da wai cewa baida komai ba,ko bai taba bata wani abu ba,hatta da katin waya bai taba tura mata ba ko na naira biyar,hakanan duk sanda zaizo kayan gwanjo yake sakawa a wanke a goge a kawo masa ya saka,ko ya sayi shadda ready made mai sauqin kudi,wataran yasa a taho masa da babur ya amsa daga can qasan layinsu ya qaraso da shi,wataran kuma ya sauka daga bayan layin ya tako da qafafunshi ya qaraso,vivo qarama itace wayarshi,kama daga hula da takalmi dukka kudinsu bai taka kara ya karya ba,ko sau daya hakan bai taba damunta ba ko a fuska,bata ma daga kai ta kalla bare har ta tantance,wataran yakan jima yana satar kallon fuskarta ko zai fuskanci wani sauyi tattare da ita,saidai sam ko alama bai taba ganin wani abu ba daya danganci hakan.
Daddy da kanshi ya zauna da mummy,tayi masa lissafin duk abinda ake buqata na asma'u,daya tashi gaba daya ya hada ya bata dana aysha dai dai dana asma'un,abun ya qona ranta sosai,wannan karon tamkar zatayi magana,da qyar ta samu ta danne ta karbi komai daga hannunshi ba qorafi ko nuna ba'ayi dai dai ba.
A sannan asma'un na zaune cikin kitchen tana charting,aysha na tsaye bakin gas tana soya mata wainar fulawa,idan ta cire saita saka mata a plate ta miqa mata
"Mummy..kin fito?" Asma'u ta fada tana cire earpiece din dake kunnenta,wanda ba komai take ji ba sai waqe waqen 'yan kudu
"Na fito" ta amsa mata tana jingina da jikin qofar kitchen din
"Ya kukayi mummy...Allah yasa duk komai yadda na tsara hakan ya bada" ta sake fada tana sauke qafafunta qasa wanda daa suke nade a saman kujerar plastic din da take kai
"Eh haka ya baku" idanu ta zaro tana duban momyn
"Momy?....ya bamu ni da wa?"
"Dawa kikasan yana bakun?"
"Haba momy haba,why...why?...komai sai an hadani da wani,wannan abun fa gaskiya ni ya isheni mommy...kenan har dubai din tare zamu wani kwashi jiki muje?,salona rainani,wannan idan akaji labari ai ajina ya gama zubewa,ince mun tafi tare dawa dina?....wallahi mommy ban yarda ba,tsakani da Allah fa ni ba'a yiwa rayuwata adalci" ta fada cikin fushi tana cika kamar zata fashe,aysha na jinsu,tana kuma sane da cewar da ita ake,saidai ko daya ita ba wannan ne ma a gabanta ba,result dinsu data samu labarin ya fito takeso taje ta duba taga me ta samu
"Ke aysha....zamuje dubai siyayyar kayan aurenku....inaga don ayi serving kudin jirgi dana hotel da kuma abinci da zamu dinga ci kiyi zamanki kawai ki bada list na abinda kike so" mummyn ta fada bayan tana sane da daddyn ya bada kudin duk wani abu da zasu buqata,sai a sannan ta waiwayo ta dubesu
"Ba komai mummy....duk abinda kika siyo yayi" dan jim sukayi baki dayansu,don basu tsammaci sam zata ce hakan ba,duk da sunsan halinta indai aysha ce ba abinda yake damunta,duk yadda aka kai ga cusguna mata tana iya shanyewa saman fuskarta,koda bai mata dadi ba cikin zuciya,wani lokaci sukanyi mamakin hakan,su dauka ko zuciya ce bata da ita ko kuma mene
"Au haushi kika ji?" Inji mummyn ta fada tana son tabbatar da ainihin yanayin aysha,da sauri ta waiwayo fuskarta qunshe da murmushi
"Haba mummy....nima fa tamkar asma'u ce a wajenki,na daukeki kamar mahaifiya ce ke a waje na,ta yaya kuwa uwa zata cutar da diyarta,kawai gani nayi ko banje ba indai ke ko anty asma'u kunje duka daya ne kamar ina wajen ne,sannan gidan ma bai dace mu barshi babu kowa a ciki ba" baki asma'u ta tabe tana jin haushi,yadda duk takai ga son cusguna mata taga bacin ranta hakan yaci tura,bata bari wani abu ya qona mata rai komai girmansa,koda ya qona matan zata iya cewa basu taba gani su a nasu idanun ba
"Shikenan....hakan yayi" cewar mummyn ta juya ta fice,sai asma'un ta miqe tabi bayanta,bata bar wajen ba bata kuma je ko ina ba,ci gaba tayi da soya mata wainar tana ajewa cikin warmer cikin hanzari saboda makaranta da takeson ta shiga.
"Bansan da sunan da zan dinga kiranki da shi ba....saboda sunan mama na kenan" ya fada cikin nutsuwa,shuru ne ya biyo baya kamar yana jiran yaji abinda zata ce,hakanan itama bata ce komai ba saboda bata da abinda zata ce din...tsahon sakanni sannan ya dora
"Sai kikaji an kawo kudi ba tare dana sanar miki ko na nemi jin ra'ayinki ba" ya sake furtawa still idanunshi a kanta,yanzun ma shuru yaga tayi ba tare da tace komai ba bayaga motsa jikinta kadan da tayi gami da cewa
"Uhmmm"
"Duk da banji ta bakinki ba amma bata baci ba...idan ba zaki iya aurar mutum irina ba kina iya fada saboda 'yancinki ne....kin ganni talaka ne ni bani da komai sai rufin asirin Allah,bamai kudi bane ni haka nan ni ba wani bane.....naga ba irinmu asma'u keso ba ban sani ba kema ko ra'ayinku daya"
"Asma'u kace....kana magana ne kan yara masu gata...masu nasaba.....masu kudi....masu kyau...."
"Da ace kema duka kina da wadan nan zabinki zaizo dai dai da nata kenan?" Ya tari numfashinta ba tare daya bari ta gama fadin maganarta ba,kai ta kada
"Rufin asiri da mutunci shine biyan buqatata,da ace ina da 'yancin zabar kalar mijin da nakeso to miji na gari zan roqa....." Har cikin tsakiyar zuciyarsa kalaman ta suka sauka,sai yaji maganganunta sun burgeshi qwarai,yanayin yadda kalamanta ke a tsare kadai ya bayyana masa tsantsar nutsuwar da Allah ya mallaka mata,sai yaji yana son hirar tasu ta dore saboda haka yace
"Bayan kin samu miji na garin alal misali,taya zaki zauna da shi koda baku taba soyayya ba?" Shuru tayi tana juya tambayar tasa,itakam gaba daya soyayya ba matsalarta bace,abinda kawai ta sani shine mutunta juna,tausayi da jin qai,qauna ta haqiqa su take buqata,inama zata samu hakan?,take qiyastawa a ranta
"Soyayya Allah ne yake jefata cikin zukatan bayinsa,duk da ban dan danata ba amma nasan da haka,tunda na samu soyayyar inna laraba da Aliya ba tare da sun zamo jinina ba....amma mutunci da karamci sanin qima suna daga cikin jigon dake riqe zaman tare" baisan sanda murmushi ya subuce masa ba,ta iya magana ta hikima taqaitacciya kuna dunqulalliyar dake isar da saqo a dan qaramin lokaci
"Humaira.....zan kiraki da shi idan babu damuwa.....daga sanda aka daura mana aure sunanmu miji da mata a idon duniya....."katseshi tayi
"Ina mamakin ta yadda zaka iya aure na wai....." Girgiza kai take duk da ba dubansa take ba
"Kada ka yaudareni kada ka yaudari kanka.....ba aurena zaka iya ba...." Qaramin murmushi ya sake
"Ni dake gaba daya lamarinmu na hannun ubangiji,bamusan yadda zaiyi ba....ban taba kawoki cikin qaddarata ba kamar yadda kema nasan hakan ne.....bazan boye miki ba,hajiyata ita ta yimin izini neman aurenki,wanda na tabbata ta hangi abinda mu kanmu babu lallai mu hangeshi" shuru tayi tana jinjina qarfin hali da jarumta irin na mahaifiyar tasa,ita a karan kanta hankalinta da shekarunta da iya abinda take gani tasan uwa na nufin wani abu mai girma a rayuwar dukkan wani abu mai rai,duk da cewa ita din batasan dadin hakan ba amma tasan ita din ba qaramin abu bace....
"Zaki iya rayuwa da talaka?"ya sake fada yana katse mata tunaninta
"Ni din wace?"
"Hajiya ce mana" ya fada yana murmushi,itama batasan sanda siririn murmushi ya qwace kan fuskarta ba,abinda ta jima rabonta da shi,sai kuma ta maida fuskarta ta gintse,miqewa yayi tsaye yana zuba hannayensa cikin aljihunsa sannan ya sake cewa
"Daddy ya saka rana gashi ni kuma ban shirya ba,infact ma ban soma shiri ba,kinsan abun talaka,lefe ma kawai aiki ne a wajenmu....ga wajen zama....toh..Allah muna gareka" ya fada yana dan daga kanshi sama,murmshi ta saki,ita din daba kowan kowa ba,ita din da aka cusa masa,ita ayshan daba wani gata ba,ita dinma tana ga Allahn,bata ga abinda zai damu kanshi ba akai wai wani lefe da wajen zama,tana daga kai suka hada ido da shi,ya jima yana dubanta ya kuma.karanceta tsaf ba tare data sani ba,sai ya dauke idanun nasa yana jin tausayinta,har ya danyi gaba sai ya dawo ya dauki lemon,irin lemonsa ne da yake yawan sha
"Bari naji zan iya shan kalar wannan,kinsan abinka da baka saba ba" ya fada yana kurbar lemon,bai aje ba sai daya shanye sannan ya aje cup din
"Zan wuce gida.....amma ba lallai ki sake gani na nan kusa....saboda muna tare da oga koda yaushe....kinsan qarqashin wani nake" yayi shuru yana jira ko zata ce wani abun a wannan gabar,saidai babu abinda tace illa
"Karka takura kanka....."
"Ki gaida mutanen gidan"ya fada yana takawa zai bar wajen
"Ka gaida hajiya" ta furta ba tare data shirya ba,sai data fada din sai kuma tayi shuru tana raba ido kanta a qasa,tana jin kamar tayi azarbabi,gabanta na faduwa sanda taji tsaiwarsa,zuciyarta na kwabarta na ta cika azarbabi da yawa
"Zataji na gode" ya fada har cikin zuciyarsa yaji dadin kulawar data nuna.
_ina godiya a gareku,kuci gaba da yimin uzuri kan yanayin gajeran typing don Allah,na gode_
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300
*KO KUMA*
07067124863
*DB*
19
Cikin sati hudu mummy ta soma shirye shiryen bikin 'yarta don bana ce shirin bikinsu ba,ta bangaren aysha sam babu abinda ya dameta,kallon komai ma take a matsayin almara,har sannan gani take koda yaushe ma muhammad kamar yadda tafi kiransa,duk da cewa cikin ranta ne bata taba kiransa a sarari ba zai janye shima,bata taba duba da wai cewa baida komai ba,ko bai taba bata wani abu ba,hatta da katin waya bai taba tura mata ba ko na naira biyar,hakanan duk sanda zaizo kayan gwanjo yake sakawa a wanke a goge a kawo masa ya saka,ko ya sayi shadda ready made mai sauqin kudi,wataran yasa a taho masa da babur ya amsa daga can qasan layinsu ya qaraso da shi,wataran kuma ya sauka daga bayan layin ya tako da qafafunshi ya qaraso,vivo qarama itace wayarshi,kama daga hula da takalmi dukka kudinsu bai taka kara ya karya ba,ko sau daya hakan bai taba damunta ba ko a fuska,bata ma daga kai ta kalla bare har ta tantance,wataran yakan jima yana satar kallon fuskarta ko zai fuskanci wani sauyi tattare da ita,saidai sam ko alama bai taba ganin wani abu ba daya danganci hakan.
Daddy da kanshi ya zauna da mummy,tayi masa lissafin duk abinda ake buqata na asma'u,daya tashi gaba daya ya hada ya bata dana aysha dai dai dana asma'un,abun ya qona ranta sosai,wannan karon tamkar zatayi magana,da qyar ta samu ta danne ta karbi komai daga hannunshi ba qorafi ko nuna ba'ayi dai dai ba.
A sannan asma'un na zaune cikin kitchen tana charting,aysha na tsaye bakin gas tana soya mata wainar fulawa,idan ta cire saita saka mata a plate ta miqa mata
"Mummy..kin fito?" Asma'u ta fada tana cire earpiece din dake kunnenta,wanda ba komai take ji ba sai waqe waqen 'yan kudu
"Na fito" ta amsa mata tana jingina da jikin qofar kitchen din
"Ya kukayi mummy...Allah yasa duk komai yadda na tsara hakan ya bada" ta sake fada tana sauke qafafunta qasa wanda daa suke nade a saman kujerar plastic din da take kai
"Eh haka ya baku" idanu ta zaro tana duban momyn
"Momy?....ya bamu ni da wa?"
"Dawa kikasan yana bakun?"
"Haba momy haba,why...why?...komai sai an hadani da wani,wannan abun fa gaskiya ni ya isheni mommy...kenan har dubai din tare zamu wani kwashi jiki muje?,salona rainani,wannan idan akaji labari ai ajina ya gama zubewa,ince mun tafi tare dawa dina?....wallahi mommy ban yarda ba,tsakani da Allah fa ni ba'a yiwa rayuwata adalci" ta fada cikin fushi tana cika kamar zata fashe,aysha na jinsu,tana kuma sane da cewar da ita ake,saidai ko daya ita ba wannan ne ma a gabanta ba,result dinsu data samu labarin ya fito takeso taje ta duba taga me ta samu
"Ke aysha....zamuje dubai siyayyar kayan aurenku....inaga don ayi serving kudin jirgi dana hotel da kuma abinci da zamu dinga ci kiyi zamanki kawai ki bada list na abinda kike so" mummyn ta fada bayan tana sane da daddyn ya bada kudin duk wani abu da zasu buqata,sai a sannan ta waiwayo ta dubesu
"Ba komai mummy....duk abinda kika siyo yayi" dan jim sukayi baki dayansu,don basu tsammaci sam zata ce hakan ba,duk da sunsan halinta indai aysha ce ba abinda yake damunta,duk yadda aka kai ga cusguna mata tana iya shanyewa saman fuskarta,koda bai mata dadi ba cikin zuciya,wani lokaci sukanyi mamakin hakan,su dauka ko zuciya ce bata da ita ko kuma mene
"Au haushi kika ji?" Inji mummyn ta fada tana son tabbatar da ainihin yanayin aysha,da sauri ta waiwayo fuskarta qunshe da murmushi
"Haba mummy....nima fa tamkar asma'u ce a wajenki,na daukeki kamar mahaifiya ce ke a waje na,ta yaya kuwa uwa zata cutar da diyarta,kawai gani nayi ko banje ba indai ke ko anty asma'u kunje duka daya ne kamar ina wajen ne,sannan gidan ma bai dace mu barshi babu kowa a ciki ba" baki asma'u ta tabe tana jin haushi,yadda duk takai ga son cusguna mata taga bacin ranta hakan yaci tura,bata bari wani abu ya qona mata rai komai girmansa,koda ya qona matan zata iya cewa basu taba gani su a nasu idanun ba
"Shikenan....hakan yayi" cewar mummyn ta juya ta fice,sai asma'un ta miqe tabi bayanta,bata bar wajen ba bata kuma je ko ina ba,ci gaba tayi da soya mata wainar tana ajewa cikin warmer cikin hanzari saboda makaranta da takeson ta shiga.