← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 73 OF 114

Sashe 73

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Tayi zaton zai saketa ne bayan fitar ta amma saitaga baida niyyar hakan,tana jin saukar boyayyar ajiyar zuciyar daya saki ta qirjinsa da kanta ke saitin wajen,dumin jikinta ya masa dadi,qamshinta kamar bai taba jin turare mai dadin nata ba,saiya miqa hancinsa zuwa wuyanta da zummar shinshinawa,da sauri ta saki gyaran murya cikin rawar murya
"Su baba atika na iya shigowa koda yaushe fa" banza yayi kaman baijita ba cikin salo na waskewa,wayarshi ya ciro bugu uku aka daga,anni ya kira
"Anni,waisai yaushe ne rahama zata bar yawo tsakanin nigeria da nijer?,yanzu me ya kawota fisabilillahi?" Bata ji me anni tace masa ba,sai taji ya sake cewa
"Bana son damuwa ne anni....ohk to" ya katse wayar yana maidata inda ya dauko sannan ya saketa
"Ina fata baki manta maganar dana taba gaya miki ba abaya,wannan karon any mistake kikayi bazan daga miki qafa ba" ya kai qarshe yana daga girarshi cikin nuna da gaske yake mata
"Duk wani abu da kikai ba dai dai ba idan ba haka nakeso ya kasance ba zanyi yadda ya kamata ne koda kuwa a gaban anni ne,ina fata kin gane?" Kai ta daga mishi
"Oya....take ur cornflakes mu wuce tare,banaso ki zauna yau a sashen nan" bowl din ta dauka gaba daya,sai ya dubeta ta dan kauda kai,ya fuskanci me take nufi,amshewa yayi daga hannunta ya aje saman canter din
"Muje kya hada wani a can" babu musu ta bishi a baya suka fice.

Ranar gaba daya a sashensu ta wuni,shima kuma yana study room di shi yana wasu aikace aikace na office daga gida,da yammaci ya fito ya dubeta yana cire glass din idanunshi
"Ki koma ciki zamuyi wani dan aiki" tattara kayan karatunta tayi ta shige kaman yadda ya umarceta,ashe kitchen aka shirya mata da spare din dan madaidaicin dakin dake cikin ainihin dakinsa na motsa jiki.

Qarfe hudu na yammacin washegarin ranar bayan ta kammala abinda take tashiga wanka wanda bata samu yi ba saboda gyaran kayan sawarsu datayi,harda na khalipha wannan karon nata qyake ba dui da batasan ya zai dauki abinda tayin ba,bata gane kurenta ba sai data fara gyaran don batasan haka kayan keda uawa ba,hakana komai nashi a tsare yake a muhallinsa,kamar side sin tie socks boxers da sauransu kowanne daban daban,dole ta maida tsarin yadda ta gashi.

Tana shirin shafa mai wayarta tayi tsuwwa,murmushi ta saki ganin maman hunaifa ke kira
"Mutuniyar nan anya ba wani ne ya riqe mana ke ba?,kin riga mu tahiwa gashi har yau baki dawo ba koni gashi na haqura na dawo duk da baban hunaifa bai koma ba?"
"Kinga barta dawowar tata duk a suna ne,sun maidani abin tausayi ita da mijinta,a gabana take fecewa mijinta kwalliya duk sanda basu da lactures su fice yawo abinsu,yanzun ma kin ganta gaban kayan kwalliya tanayi" cewar hanan wadda ta amshe wayar ba tare data bar mmn hunaifa ta qarasa fadin abinda takeson fada ba,dariya aysha ta saki,duk sai taji tayi missing nasu,batasan me yasa khalipha ya tsaidata daga komawar datayi niyya ba dazun da safe
"Allah aysha saimun rama,Allah yakai damo ga harawa bari muna muyi auren nan saita ri ga rufe idonta"
"Idan ban wa mijina ba nikam duk banga amfanin ma kamfanin sutura da kayan kwalliya ba,kuma idan yazo kanku ban yadda ku saurara ba" mmn hunaifa dake gefe ta fadi,dariya suka sa gaba daya sannan suka soma gaisawa tare da tambayatta lafiya,sa kawai tace musu basu da lacuters ne dalili kenan amma tana kan hanya,hira suka yi sosai sai data ji kiranabban hunaifa na shigiwa alamar ya iso sannan sukayi sallama,aysha na dariya ta aje wayar,a hankali ta dora idonta kan fuskarta data bayyan a gaban mudubi,murmushi taci gaba dayi tana tuna yadda ma'auratan ke bawa junansu kulawa,abun na mtuqar bata sha'awa da burgeta kaman yadda yake burge hanan,sai kawao ta sami kanta da yin kwalliya sosai duk da cewa a yanzun mawuyacine ka ganta ba kwalliya koda lite ce.

Sosai tayi kyau uta kanta ta gani,siririyar sarqa ta saka da dan kunenta tana hade da zobe mai kyau ta feshe jikinta da turare sannan ta yafa yalolon mayafi daya dace da adon nata,gurin anni takeson shiga sai ta dauki litattafanta ta fita dasu tana son ta duba.

Ba kowa a falon sai rahama dake faman waya,wani kallo tabi aysha dashi tun daga sama har qasa,sauyawar yarinyar na bata tsoro,dudud wata nawa amma kaman an maya wankan engine,amal ce ta shigo daga wata qofa wadda zata kaika bayan gidan,itama kallo tabi ayshan dashi,duk ta lura dasu saita rasa na meye kallon?,a baya sam bata taba tsayawa dubawa ba bare ta tantance,saidai zuwa yanzu rashin jituwa tsakanin amal da rahama ke bata mamaki da tambyar kanta meye sila,uwa uba yadda amal din ta sake ja baya da ita ta rasa daliki,koma meye dukansu ba damuwarta bane,tana qoqarin sauke nauyin da musulunci kawai ya dora mata,haka nan taji zaman falon bai gamsheta ba,saboda haka ta jiya kawai ta fuce zuwa can bayan gidan inda ya wadatu da yawan shuke shuke,ta bude takardunta ta soma dubawa daya bayan daya.

Bata nima da zama ba taji shigowar motocinsu haidar,da alama daga office suka dawo,saitaqi tashi zuwa cikin gidan,don karatin ya soma mata dadi,duk da cewa akwai ma'aikatan dake gayafn flowers din wajen dake wucewa jifa jifa,amma da yake ba hayaniya suke ba basu dameta ba.

Sosai ta duquf tana duba wata paper dake hannunta,sai hancinta ya dinga jiyo mata wani qamshin turare nadaban wanda kamar ta sanshi,hat ta basar taji qamshin na sake daduwa cikin hancinta,saita daga kanta,khalipha ke dosowa inda take,bayanshi yaro shi nasir na biye dashi dauke da wasu fikes,juyawa taga yiyi yayi mahana kadan da shi saitaga yadan rusuna cikin girmamawa ya juya yabar wajen,shi kuma yaci gaba da qarasowa inda take,faduwar gaba tasamu wadda ta zame mata jiki aduk sanda ya kalleta ko suka kadaice daga ita saishi
"Sannu da zuwa" ta fada a yangance wanda ita batasan tayi din ba,idnunshi a kanta ya amsa shima cikin nashi salon.

Ticket din dake hannunshi ya miqa mata guda daya tana duban kwalliyar da tayi ta yau wadda tayi masifar burgeshi,buba ce da zani saidai kuma an danne gefe da gefanta dai dai jikin mai ita,sosai qirar jikinta ta fita,dan siririn mayafin data yane kanta bai rufa asirin gashinta ba da yasha gara yake qyalli,hakanan qamshin jikinta bai bar buso mishi ba tare da iska mai sanyi irin ta la'asar din da akayi dace aka samu raguwar yanayin zafin da ake ciki,fararen qwayar idanunta ta saka tana karanta ticket din,legos?,me zasuje yi a legos din?,kamar ya karanci abinda yake kai kawo a zuciyarta yace
"Gobe zamu wuce,kada ki damu da abinda zamuje yi" ya qarashe maganar yana bin yatsunta da kallo da har yanzu jan lallen dake jikimsu yake ci gaba da burgeshi hakanan
"Toh" ta furta a sanyaye tana ninke ticket din,haka kawao jikinta yayi sanyi take jin fargaba,hannunshi cikin aljihun wandonshi ya juya ya fara takawa,sai kuma ya tsaya cak yana duban gilmawar masu ya kan fulawar dake gyara a wajen,haka kawai yaji wani abu ya taba ranshi,saiya dawo da baya a sanda take ci gaba da rubutun assigment dinta
"Ko zaki koma ciki?,nan din maga bake kadai bace" kai ta girgiza tana shakkar hada ido dashi,batasan me yasa sau tari idan yana gab da ita take yawan jin hakan ba
"Duka bamu takura ba babu komai" bai sake tanka mata ba ya duqa ya soma tattare takardun,saita soma binsa da kallo,baiko dubeta ba har ya gama,hannunshi ya sanya ya zare biron dake tsakiyar yatsunta sannan ya juya ya soma tafiya,ta fahimci me yake nufi dole ta sauko daga saman lilon ta zira takalmanta ta biyo bayanshi.

A fakaice take qarewa tafiyarshi kallo,idan baka sanshi ba sai kayi tsammanin yana sane yake irin tafiyar,kamar saraki ko mai jinin sarauta a jikinsa haka yake takawa cike da nutsuwa
"Kinsan idan namiji ya amsa,sunanshi yanayin tafiyarsa ma kawai abun kallo ce" ta tuna kalaman hanan data sakata a agaba tana koya mata yadda zata gane ta fada soyayya da wani,da kuma siffofin qasaitaccen namiji wanda ba lallai sai mai kyau ne yake da su ba,duka shirme take daukan abun,sai gashi a yanzu batasan dalilin da yasa daya bayan daya komai yake dawo mata ba aduk sanda khalipha yayi wani motsi.

40

Tunda suka doshi sashen anni suke jiyo muryar rahama,hira suke da mus'ab amma kamar musu musu haka,anni na gefe bata sa musu baki ba tana sabgar gabanta,suna shiga ta bisu da idanu,idonta kan litattafan dake rungume hannun khalipha,duk wata walwalarta ta bace tsaf kunnuwanta da idanunta dukka suna kansu,idanu suka hada da aysha ta daga mata gira bayan ta sakar mata murmushi,ta mata sign na toya kika gani? Da idanunta,saita dauke idonta ta basar tamkar bata gani ba,saidai har yanzu kunnuwanta na wajen
"Gobe zamubi jirgin qarfe biyu anni in sha Allahu"
"To Allah ya bada sa'a,Allah ya nuna mana goben"
"Amin" ya fada cikin hikima yana karantar yadda hankalin rahama ya raja'a a kansu,littafi daya ya zaro cikin wadanda suke hannunshi ya dan buga ma ayshan kadan
"Wuce muje ki qarasa aikinki" kunya ce ta kamata,amma ya riga yayi warning dinta tun jiya,idan ma bata bishin ba zaiyi abinda yafi haka ne gaban annin kamar yadda yace mata,dole ta miqe,ya tasata a gaba suka fice.
Chapter 73 · 0% Book details