← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 114

Sashe 32

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da yammacin wata ranar laraba anty safiyya tazo gidan,suna zaune a parlour ita da mummy da asma'un,mummyn na cinikin wasu magungunan mata da asma'un tace tana so,ta kira matar takanas kuwa har gida ta kawo mata,saboda tasan cewa zata maida uwar kudinta cas harma da riba,mummy na dauka asma'u na duddubawa tana zaba da kanta,anty safiyyan na gefe tana kallon ikon Allah,tun tana shuru har ta gaza yin shirun kasancewarta mai zafi da rashin son raini da wargi,kai tsaye ta yiwa asma'un magana saboda tasan idan ta mummy ne ma aikin banza ne a wajenta
"Wai asma'u meye haka?,wannan wacce iriyar muguwar dabi'a ce?"kai ta daga tana kwabe fuska saboda tasan halin anty safiyyan tsaf
" yanzu kuma meye nayi?,tunda kika zo gidan nan na kasa qwaqqwaran motsi na sake saboda nasan ki da dan banzan chellang din mutane da cin gyaransu"
"Akan gaskiya ba....ke ko kunya bakiji ki zauna kina zabawa kanki magungunan mata gaban babarki?" Matar ce ta saki dariya tana cewa
"Yo hajiya meye?,ai yanzu haka akeyi,idan ba'a mata a gidansu ba waye zaiyi mata?,'yammatan yanzu ma kansu ya waye,idan ba'a miki ba ni da kansu suke zuwa su siya abinsu kafin bikin suyi amfani da shi...meye a ciki ai gwara su gyaggyara ko" dauke kai safiyya tayi daga bangaren matar,donta fuskanci ita kudinta takewa campaign da kayanta,ba ruwanta da batun kunya ko al'ada ta dubi mummy
"Mummy....ko magani za'a bawa asma'u ba irin wannan take buqata ba,maganin sanyi da basir ya kamata ace an soma nema mata,baya ga haka ma akwai abubuwa da yawa daya kamata ace su aka fara dora ta akai bawai magani zalla ba da sauran qyale qyale,akwai abubuwa data rasa,mummy ina mai tabbatar miki babu abinda asma'u ta iya dafawa,hana rantsuwa indomie,komai a gidan nan yiwa asma'u ake bata san ta yiwa kanta komai ba,a haka zata zauna gidanta duka ba'a kula da wannan ba,wannan gata ne mummy?,duk macen data shiga gidan miji a haka ko hurul'een ce ita ba zata taba daraja ba" bacin rai qarara ya fito a fuskar asma'u,badan badan ba da tace anty safiyya na cikin 'yan baqincikinta,don dai kawai ciki daya suka fito,ta jima rabon da aci mata fuska irin haka,badan tasan bata daukar wargi ba ba abinda zai hanata gaggaya mata magana kota sheqa mata ma zagi
"Banda abinki safiyya duka mai ya kawo wannan maganar kuma,zancan koyon aiki kema kinsan inda zata je ai,bata da matsalar girki da sauran gyaran gida tana da masu yi mata"
"Barta kawai mummy,don ke baki da mai aiki kinqi daukar kowa kin hadawa kanki wahalar aikin gida kowa haka zai zauna kamar wani dan wahala?,already mun gama magana ni da hamid ina da masu yimin komai baya buqatar na wahal da kaina wajen dauke koda tsinke ne" asma'un ta fada cikin bacin rai tana ci gaba da duba kwalin magungunan abinta
"Idan kana da kyau asma'u ka qara da wanka,ni yar uwarki ce dole na gaya miki gaskiya koda kowa ya kasa gaya miki saboda tsoron ko shakkar rashin kunyarki,duk arziqin mijinki akwai wani abu da yake buqata matarsa ta iya tayi masa ita da kanta,ba burgewa bace kana jibge kaman kayan gwanjo wata ke miki aikin gidanki,duk ladarki kin tattara kin bar mata,bautar ubangijin da akace zakiyi cikin aure ke baki ma santa ba kenan,saidai kici ki sha kiyi wanka"
"Au dama bauta aka ce miki no zanje nayi?,tabdijan su bauta manya,ni gidan 'yanci zan shiga gidan soyayya"ta fada tana tabe bako,don ta soma kaiwa bango,gab take da yiwa mata rashin kunya,bata son ayi fito na fito da ita kwata kwata kan nata ra'ayin,tafiso a qyaleta tayi yadda takeso ta kuma tsara
"Rayuwarki ce kiyi duk yadda kike ganin ya dace,amma karki kuskura kimin rashin kunya,kin sanni bani da dadi wallahi" ta fada cikin fushi qarara bayyane a muryarta
"To ya isa haka don Allah,ni bana son wannan rigingumun naku" mummy ta fada tana turawa matar kayanta,tattarewa tayi ta soma maidawa cikin jakarta suna lissafi da mummy,tashi safiyya tayi ta wuce kitchen saboda bacin rai da takaici,kome asma'u zatayi batasan me yasa mummy bata iya tsawatar mata ba,ita a ganinta sam wannan ba soyayya bace,duk duniya kowacce uwa na son danta,amma duk sanda kikayi sakacin da baki iya tsawatar masa a sanda ya aikata ba dai dai ba to la shalla zakiyi kuka gaba da hawayenki,bahaushe yace ka saka danka kuka kafin shi ya saka ka,hakanan kaza tana sane take take danta badon bata sonshi ba,a'a sai don ta koya masa darasin rayuwa.

Sanda ta fito daga kitchen din matar ta wuce,hakanan asma'un bata falon,zama tayi kusa da mummyn dake latse latsen waya
"Mummy...don girman Allah ki daina biyewa asma'u a duk lamuran da tace tana so,mummy wannan fa ba gata bane,gidan wani zata je fa,yadda kika saba mata haka zata ce zata yi musu,bayan ita rayuwa ba tabbas gareta ba"
"Kai safiyya kai...wallahi kin cika qorafi...magana ta riga ai data wuce ko,maganin duka qwaya biyu na daukar mata sai kuma meye yayi saura?,nifa kinsan bani son takura kwata kwata" kai ta jinjina
"Shikenan mummy...kiyi haquri" daga haka ta soko maganar data kawota gidan,kan wani abun adon daki da za'a yiwa asma'un,saidai yadda taga mummyn na lissafin na mutum daya ne
"Mummy aysha fa...nayi zaton duka daddy ya bayar?"
"Eh...ina da uzuri da nata kudin ne,idan na samu wasu kudin ko kafin biki ne ayi mata tunda kamfani ne ba za'a rasu su available ba koda yaushe" shuru kawai safiyyan tayi,tunda ta fadi haka kawai ta sani banda ita,batasan me yasa mummy take irin haka ba,aysha ta cancanci a siya mata ma ahana asma'u,don yadda mummy ke morar aysha mo asma'un bata mata rabin wannan morar ko kusa ko alama.
(To gareku mata masu riqon yaran wasu,walau marayu dan kishiya ko masu iyaye...mu sani rayuwa bata da tabbas,baki da tabbacin kema zaki rayu da naki,idan kin rayu da naki jikonki fa?,duk abinda ka yiwa yaro na cutarwa yana sane abun yana kanshi,komai dadewar shekatu wallahi Allah yana sane da abinda kayi masa,wani ma a sanda zai tuna miki tsufa ya cimmaki ko qarfinki ya qare kema kina qarqashinsa ko qarqashinta,a sannan shi kuma Allah ne kadai yasan arziqin da yayi masa,a lokacin da zai tuna mikin Allah ne kadai yasan kunyar da zaki sha idan ma kina raye kenan,idan ma bai yada maganar a sanda kike qarqashin qasa ba,wallahi duk wanda ka zalunta duk qanqantar zaluncin Allah bazai taba yafe maka ba sai ya fiddawa kowa haqqinsa,da kike fifita yaranki a kanshi shima haihuwarsa akayi iyayensa na sonahi,qila da suna tare da shi gatan da zasu nuna masa yafi wanda ke kike nunawa naki yaran,hakanan yaranki na kallon me mike kina koya musu aqidar banza ne idan Allah ya basu aron rai suma akai zasu dora,shi sharri dan aikene maishi yake dawowa,hakanan alkhairi danqo ne baya faduwa qasa banza,Allah yasa mu dace,yasa mufi qarfin zukatanmu)

A tsakanin wannan lokacin mummy suka tafi dubai ita da asma'u da anty halima,batasan me da me suka tsarawa daddy ba,saidai baiyi fada kan tafiyar da sukayi babu ita ba,itama sabgarta kawai take,a yanzu gaba daya addu'o'inta sun karkata ne kan Allah ya sanya auren ya zama alkhairi a gareta duniyarta da lahirarta,bata jin motsin wani daga cikin 'yan uwanta bare yace wani abu kan aurenta ko zata ji dadi,tasha tasa wayarta a gaba tana kallon lambar umminta,ta sha kwatanta kiranta,tasha qissimawa a ranta inama ta wayi gari watan wata rana ta tsinci koda miscal ne akan fuskar wayarta,zata so Allah ya gwada mata wannan mafarkin nata koda sau daya ne tak a rayuwarta kafin tayi qaura wa duniya,abun mamaki da lantana mai aiki suka tafi,tana jin mummyn na cewa
"Gwara muje da itan,saboda daukar kaya da sauran 'yan wahalhalu" bata sani ba kota fadi hakanne saboda kar ayshan ta zargeta,itadai ko oho bata masa inda zancan nata ya dosa ba,don bata iya riqe magana ba a rai,ita kadai suka barwa gidan sai mai gadi,a lokacin daddy shima yayi tafiya,tana tsoron gidan sosai amma haka ta zauna babu yadda ta iya,idan tayi addu'a ta koma dakinta bata sake fitowa sai safiya,

Ba qaramar siyayya suka yo ba,har jikokinta sai data yi musu tasu tsarabar,kayan fitar biki nata dana asma'u,hakanan ta jido kayan business dinta,saidai babu ko tsinke da Allah yasa aysha taga gilmawarsa da sunan nata ne,kaya masu yawa haka aka jibgewa asma'u a store din gidan,a haka ma da wasu suna nan qarasowa.

Kwana biyu da dawowarsu taji mummyn na waya da wani mutum dake amsar kayanta a kantin kwari kan tana son kaya,da daddare sai gashi ya kawo din kuwa,a sannan yasha tana daki tana gyaran kumbarta lantana ta shigo ta kirata,kaman ko yaushe ta saka hijabinta ta fita
"Aisha ga kaya nan saiki zabi kalar wanda kikeso,daddynku ne yace a siya muku na fitar biki" kai ta tada ta dubi kayan
"Duk wanda kika dauka min yayi"
"A'ah A'ah ni babu ruwana kinsan halin daddynku,tare da asma'u muka je ta zabi wanda takeso to saboda kayan kar suyi yawa suja kilo shi yasa ba'a sai naki ba,dalili kenan daya sa nace nuraini ya kawo miki daga shagonsu kema ki zaba da kanki,tunda suma kayan su masu kyau ne"
"Mtsweew....mummy sai dana ce miki ba sai kin kirata ba,ina laifi ba ma da za'a siya mata,kawai ki zaba ki aika dasu wajen dinki ta bada size dinta,amma ai bama girma bane ki tsaya kuna wani maida magana ke da ita"
"Shikenan zabar mata,'yar uwarki zata zabar miki"
"Na gode" ta fada kawai tana miqewa tabar wajen,asma'un ita ta zaba mata atamfa da laces,kusan kayan ma mummyn ce ta sarosu kudin ya sake dawowa inda ya fita kenan,dinki ne kawai mummyn ta kai inda ake mata bayan ta dauki hotunan kayan ta turawa daddy da sunan kayan da aka siyowa asma'u ne da aysha.
Chapter 32 · 0% Book details