Sashe 13
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ita kadai ke sakin tsaki jifa jifa saboda komawarta gida da bataso ba,yana biye da ita tare daci gaba da karantarta a haka har suka kusa isa parking space din dake wajen sannan ya qara hanzarinsa har ya cimmata,a bayanta ya tsaya sannan yayi mata sallama,ta dan tsorata hakan yasanya ta waiwayo tana dubanshi,da fari taso gaya masa magana ne saboda yadda ta tsorata,amma tashin farko sai ya mata wani irin kwarjini,kyan fuskarsa ya dakushe tsiwarta,saita sake ajiyar zuciya tana dubanshi tace
"Meye haka malam?,haka kawai ka tsorata mutane" murmushi ya saki cikin sassauta tsare gidansa da ragewa kwarjininsa kaifi
"Kiyi haquri ranki ya dade,banyi zaton zaki tsorata ba"
"Naji...lafiya?"kai ya girgiza
"ba lafiya ba" ido tadan fiddo waje
"Ba lafiya ba kamar yaya?"
"Idan ba zaki damu ba ko zamu matsa daga gefe?"
"Ba buqatar hakan don ni sauri nake,fadi matsalarka"
Cikin nutsuwa ya soma fadi mata sunanshi da abinda ke tafe da shi,kallo ta dinga qare masa tun sanda ya soma maganar har ya gama
"Kai din waye?" Ta furta tana son sanin waye shi din har zuciyarta,shafa kanshi yayi kamar wani mara gaskiya
"Ba kowa bane ni,hasalima qarqashin wani nake,shine ubangidana kuma shi na rako nan wajen" dariya ta saki cikin ranta tana jin haushi da takaici,tana ganin ya gama raina mata wayo,ya kuma fado da ajinta,ta yaya yaron wani zaice yana sonta?,maici a qarqashin wani?,me na sama yaci ballantana na qasa,toko gashin kanshi yake ci ai bata jin zai samu soyayyarta ta sauqi bare yaron wani,abu guda ne zai hanata ci masa mutunci,tsantsar kyau da kwarjinin da yayi mata,sai kawai taja siririn tsaki ta juya ta soma takawa a hankali da niyyar barin wajen
Cike da hanzari da zafin nama ya sake binta,daf da zasu isa inda su aysha ke jiranta ya sake shan gabanta,tsam tayi tana dubansa har ya gama maganarsa,tsiwa takeso ta masa amma ya mata kwarjini,yayi mata tako ina ya hadu,kai tsaye ma zata ce yafi hisham
Kyau kwarjini da cikar zati,namiji ne mai irin kyan da takeso,mai surar da takeso,saidai bai mallaki abinda zai bashi damar shiga jerin masoyanta ba,abu guda tak daya fada yasa taga sam bai dace tayi tarayya da shi ba,wato lafazin uban gidansa ya rako
"Kar ka sake bina pls,ka saurara min" lafazin da aysha ta iya jiyowa sun fito daga bakin asma'u kenan,tana iya hangoshi tar ta cikin hasken,a hankali ta janye idanunta daga kansu tana yunqurin komawa cikin motar ganin asma'un ta doso su tun kafin tazo itama ta sauke mata nata kason,tana matuqar mamakin yadda asma'un keda zarrar tsayawa gaban maza tana musu yadda taga dama ba tare da damuwa da shekaru ko darajar koma waye ba.
Garam ta rufe murfin motar ba tare data dubi usama ko aysha ba tace
"Muje" kai tsaye
Ita daya ta dinga mitar biyotan da akayi aysha na jinta bata ce komai ba,tana ganin kamar ya rage mata aji ne daya biyoya ma,kiran wayar hamid ita ta janye hankalinta har suka je gida suna waya,a cikin mota ita dai ta barta ta wuce ciki.
Kan dining ta samu daddy shi da mommy suna cin abincin dare,a nutse ta qarasa,tana shirin gaida daddy mommy tayi caraf cikin salon data saba amfani da shi koda yaushe tace
"Ina kuka tsaya tun la'asar sai yanxun?" Kanta a qasa tace
"Hajiya ce tace sai munci abinci zamu taho"
"Ina ita husnar?"
"Tana mota" ganin tambayoyinta sun qare yasa ta waiwaye bangaren daddyn ta gaidashi cike da ladabi da girmamawa,shima ya amsa mata cikin kulawa,tana shirin miqewa ta wuce asma'u ta shigo,a shagwabe take qarasowa zuwa wajen
"Ke ba zaki ci abinci ba?"mommy sa'adah ta fada ganin ayshan na niyyar wucewa,ga idanun daddy a wajen
"Na qoshi,naci wajen hajiya"har ta soma takawa daddy ya kira sunanta,sai duka hankalinsu ya koma kansu daddyn duk da magana suka soma yi a tsakaninsu,a ladabce ta dawo ta durqusa
"badai wata matsala ko?" Murmushi ta saki dan kadan,to wacce matsala ita din take da bakin cewa tana da ita?,a yanzu bata ganin wata matsala tattare da rayuwarta idan ta kwatanta da rayuwarta ta baya
"Eh daddy babu"
"Kin tabbatar?" Ya sake jaddadawa don har ga Allah yana qaunar yarinyar yana tausayin rayuwarta,sam bata da marsala tunda har yau duk abu irin na sa'adatu bata taba kawo masa qararta ko qorafi a kanta ba,duk da cewa bata taba yabonta ba,amma hakan ya alamta masa bata da wata matsala,yqsan halin matarsa sarai,da tana da damuwa yarinyar tofa duk sanda suka zauna hira ta dinga sakin qorafin akanta kenan,duk da ba zata fito kai tsaye ta kawo masa qararta ba,haka nan nutsuwarta ta daban ce
"Na tabbatar daddy" ta amsa masa muryarta can qasa idanunta na duban tiles din dake shimfide a qasan falon
"To Allah yayi albarka ya kuma yi jagora"
"Ameen daddy na gode,Allah ya saka da alkhairi"
"Ameen" ya amsa cikin jin dadi,miqewa tayi bayan ya sallameta,asma'u na zabga mata harara a fakaice tana ayyana munafuka cikin zuciyarta,yayin da haushi da takaici ya tuqe mommy sa'adatu,saidai sam ba zaka ce haka ba don ko kan fuskarta bata nuna ba,sai abinci da take diba kadan kadan.
A gajiye take liqis,cikin kasala ta dinga warware lafayar jikinta sannan ta shiga bayan gida ta hada ruwa mai zafi tayi wanka,mai ta shafa ta feshi jikinta da turare sannan ta zira rigar bacci doguwar mai taushi da kauri,bacci kawai take buqata tayi,saidai qarar wayarta ta dakatar da ita,ta qarasa ta cire wayar daga chargy tana duba mai kiran,asma'u ce,ta shafa ta kara a kunnenta
"Fito ki daukomin kayan da nace ki ajemin" ta fada da salon muryar data saba yi mata magana,aje wayar tayi ta zira hijabinta ta fice zuwa kitchen.
*_WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*
*DAURIN BOYE*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
HASKE WRITERS ASSO
(Home of expert and perfect writers)
10
A tsaye ta sameta cikin kitchen din riqe da cup tana shan yoghourt,fuskar nan a hade,fridge din ta bude ta ciro mata kayan,saidai bata ga dambun kazar ba
"Ina dambun?" Ta tambayeta tana duban kayan
"Ban sani ba nima cikin freezer din na ajjiye"
"Wacce iriyar banzar magana kike fada,banson iskancin banza waye zai dauka?" Ta fada a dan zafafe,da alama dai akwai wata a qasa,cikin sanyin muryarta kamar yadda yake a halittarta tace
"Wallahi ban sani ba anty asma'u,dana gama na saka a ciki mummy ta aikeni gidan mummy laraba", shigowar mummy cikin kitchen din shi ya katse muhawarar
" hayaniyar me nake ji?"ta tambayesu tana aje warmers din abincin da daddy ya gama ci
"Wannan yarinyar mummy nason ta fara rainani,sumumu kasau macijin sari ka noqe,na sata ta hadamin kaya amma tace wai bata ga dambun da nace ta yimin ba?"
"Banson tashin hankali da daren nan ki kira mana hankalin babanku,ta sake miki wani,wancan nayi baqi na basu" ta fadi tana ficewa a kitchen din,shiru tayi kafin ya kwashe kayan ta fice itama bayan ta aje mugun tsaki.
A qalla ta shafe kusan minti goma kafin itama ta soma takawa a hankali tana ficewa daga kitchen din,bata san me ya taba zuciyarta ba batasan tana hawaye ba saidata shafi fuskarta,tana goge hawayen tana addu'ar bacci da haka ta kwanta bayan taja bargonta zuwa kafadunta.
Ta jima a kwance tana nazarin rayuwa kafin ta tattara dukka lamuranta ta sake miqawa Allah.
Ya dan jima tsaye shida drivansa yana qarewa gidan kallo,haka kawai yaji zuciyarsa ta nutsu ta aminta da gidan,yana jin gamsuwa da nutsuwa har cikin zuciyarsa,yana son mace mai kamun kai da jan aji,yana ganin kamar akwai alamun hakan tattare da ita,yanayin arziqin gidansu yana ganin kaman bazai sanyata qyamatar mai qaramin qarfi ba,kamar zata amsheshi haka yakeji,amma hakan bazaizama dalilin da zai sanya ya kasa jarraba ta ba kamar sauran,a nutse ya yiwa drivern nasa umarnin su wuce.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Qarfe biyu na rana suke takowa zuwa cikin layin nasu daga bakin titi zuwa gidansu ita da asma'u dake qunquni kamar zata fashe,taci alwashin bata sake hawa motar,duk da ba tsufa ne yasata yin hakan ba,uban motar da take ci ne kawai da kuma halin tsiyar qarfen nasara,inda Allah ya taqaita saida sukazo kwanar gidan nasu ta kakare musu a nan,itakam aysha na gefanta,baki daya bata ga abun bacin rai ba,don dai yau kadai.
"Malam ka cikani,Allah bazan biya ba"
"Wallahi saika biya kaji na gaya maka,ba inda zan sakeka kaje" hayaniyar mutum biyu kenan data cika kunnensu gab da zasu qarasa qofar gidansu,hayaniyar na tashi ne daga wani dan case dake maqale da gidan maqocinsu dake kallon nasu gidan,case ne da mai gadin gidan ya bude yana saida katin waya da sauran 'yan qananun abubuwa da ba'a samu cikin unguwar sai sunje waje mai nisa saboda yanayin unguwar tasu,dukkansu hankalinsu yakai wajen,asma'u ta ganeshi tsaf,yayin da aysha taso ta shaida fuskar,da sauri asma'u ta dauke kanta,hakanan taji gabanta na faduwa,ta yaya akai yasan gidansu?,me yake a layinsu?,fatanta daya kada Allah yasa ya nuna ya santa,don ta fuskanci yana da wata zarra da rashin fargaba.
"Meye haka malam?,haka kawai ka tsorata mutane" murmushi ya saki cikin sassauta tsare gidansa da ragewa kwarjininsa kaifi
"Kiyi haquri ranki ya dade,banyi zaton zaki tsorata ba"
"Naji...lafiya?"kai ya girgiza
"ba lafiya ba" ido tadan fiddo waje
"Ba lafiya ba kamar yaya?"
"Idan ba zaki damu ba ko zamu matsa daga gefe?"
"Ba buqatar hakan don ni sauri nake,fadi matsalarka"
Cikin nutsuwa ya soma fadi mata sunanshi da abinda ke tafe da shi,kallo ta dinga qare masa tun sanda ya soma maganar har ya gama
"Kai din waye?" Ta furta tana son sanin waye shi din har zuciyarta,shafa kanshi yayi kamar wani mara gaskiya
"Ba kowa bane ni,hasalima qarqashin wani nake,shine ubangidana kuma shi na rako nan wajen" dariya ta saki cikin ranta tana jin haushi da takaici,tana ganin ya gama raina mata wayo,ya kuma fado da ajinta,ta yaya yaron wani zaice yana sonta?,maici a qarqashin wani?,me na sama yaci ballantana na qasa,toko gashin kanshi yake ci ai bata jin zai samu soyayyarta ta sauqi bare yaron wani,abu guda ne zai hanata ci masa mutunci,tsantsar kyau da kwarjinin da yayi mata,sai kawai taja siririn tsaki ta juya ta soma takawa a hankali da niyyar barin wajen
Cike da hanzari da zafin nama ya sake binta,daf da zasu isa inda su aysha ke jiranta ya sake shan gabanta,tsam tayi tana dubansa har ya gama maganarsa,tsiwa takeso ta masa amma ya mata kwarjini,yayi mata tako ina ya hadu,kai tsaye ma zata ce yafi hisham
Kyau kwarjini da cikar zati,namiji ne mai irin kyan da takeso,mai surar da takeso,saidai bai mallaki abinda zai bashi damar shiga jerin masoyanta ba,abu guda tak daya fada yasa taga sam bai dace tayi tarayya da shi ba,wato lafazin uban gidansa ya rako
"Kar ka sake bina pls,ka saurara min" lafazin da aysha ta iya jiyowa sun fito daga bakin asma'u kenan,tana iya hangoshi tar ta cikin hasken,a hankali ta janye idanunta daga kansu tana yunqurin komawa cikin motar ganin asma'un ta doso su tun kafin tazo itama ta sauke mata nata kason,tana matuqar mamakin yadda asma'un keda zarrar tsayawa gaban maza tana musu yadda taga dama ba tare da damuwa da shekaru ko darajar koma waye ba.
Garam ta rufe murfin motar ba tare data dubi usama ko aysha ba tace
"Muje" kai tsaye
Ita daya ta dinga mitar biyotan da akayi aysha na jinta bata ce komai ba,tana ganin kamar ya rage mata aji ne daya biyoya ma,kiran wayar hamid ita ta janye hankalinta har suka je gida suna waya,a cikin mota ita dai ta barta ta wuce ciki.
Kan dining ta samu daddy shi da mommy suna cin abincin dare,a nutse ta qarasa,tana shirin gaida daddy mommy tayi caraf cikin salon data saba amfani da shi koda yaushe tace
"Ina kuka tsaya tun la'asar sai yanxun?" Kanta a qasa tace
"Hajiya ce tace sai munci abinci zamu taho"
"Ina ita husnar?"
"Tana mota" ganin tambayoyinta sun qare yasa ta waiwaye bangaren daddyn ta gaidashi cike da ladabi da girmamawa,shima ya amsa mata cikin kulawa,tana shirin miqewa ta wuce asma'u ta shigo,a shagwabe take qarasowa zuwa wajen
"Ke ba zaki ci abinci ba?"mommy sa'adah ta fada ganin ayshan na niyyar wucewa,ga idanun daddy a wajen
"Na qoshi,naci wajen hajiya"har ta soma takawa daddy ya kira sunanta,sai duka hankalinsu ya koma kansu daddyn duk da magana suka soma yi a tsakaninsu,a ladabce ta dawo ta durqusa
"badai wata matsala ko?" Murmushi ta saki dan kadan,to wacce matsala ita din take da bakin cewa tana da ita?,a yanzu bata ganin wata matsala tattare da rayuwarta idan ta kwatanta da rayuwarta ta baya
"Eh daddy babu"
"Kin tabbatar?" Ya sake jaddadawa don har ga Allah yana qaunar yarinyar yana tausayin rayuwarta,sam bata da marsala tunda har yau duk abu irin na sa'adatu bata taba kawo masa qararta ko qorafi a kanta ba,duk da cewa bata taba yabonta ba,amma hakan ya alamta masa bata da wata matsala,yqsan halin matarsa sarai,da tana da damuwa yarinyar tofa duk sanda suka zauna hira ta dinga sakin qorafin akanta kenan,duk da ba zata fito kai tsaye ta kawo masa qararta ba,haka nan nutsuwarta ta daban ce
"Na tabbatar daddy" ta amsa masa muryarta can qasa idanunta na duban tiles din dake shimfide a qasan falon
"To Allah yayi albarka ya kuma yi jagora"
"Ameen daddy na gode,Allah ya saka da alkhairi"
"Ameen" ya amsa cikin jin dadi,miqewa tayi bayan ya sallameta,asma'u na zabga mata harara a fakaice tana ayyana munafuka cikin zuciyarta,yayin da haushi da takaici ya tuqe mommy sa'adatu,saidai sam ba zaka ce haka ba don ko kan fuskarta bata nuna ba,sai abinci da take diba kadan kadan.
A gajiye take liqis,cikin kasala ta dinga warware lafayar jikinta sannan ta shiga bayan gida ta hada ruwa mai zafi tayi wanka,mai ta shafa ta feshi jikinta da turare sannan ta zira rigar bacci doguwar mai taushi da kauri,bacci kawai take buqata tayi,saidai qarar wayarta ta dakatar da ita,ta qarasa ta cire wayar daga chargy tana duba mai kiran,asma'u ce,ta shafa ta kara a kunnenta
"Fito ki daukomin kayan da nace ki ajemin" ta fada da salon muryar data saba yi mata magana,aje wayar tayi ta zira hijabinta ta fice zuwa kitchen.
*_WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*
*DAURIN BOYE*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
HASKE WRITERS ASSO
(Home of expert and perfect writers)
10
A tsaye ta sameta cikin kitchen din riqe da cup tana shan yoghourt,fuskar nan a hade,fridge din ta bude ta ciro mata kayan,saidai bata ga dambun kazar ba
"Ina dambun?" Ta tambayeta tana duban kayan
"Ban sani ba nima cikin freezer din na ajjiye"
"Wacce iriyar banzar magana kike fada,banson iskancin banza waye zai dauka?" Ta fada a dan zafafe,da alama dai akwai wata a qasa,cikin sanyin muryarta kamar yadda yake a halittarta tace
"Wallahi ban sani ba anty asma'u,dana gama na saka a ciki mummy ta aikeni gidan mummy laraba", shigowar mummy cikin kitchen din shi ya katse muhawarar
" hayaniyar me nake ji?"ta tambayesu tana aje warmers din abincin da daddy ya gama ci
"Wannan yarinyar mummy nason ta fara rainani,sumumu kasau macijin sari ka noqe,na sata ta hadamin kaya amma tace wai bata ga dambun da nace ta yimin ba?"
"Banson tashin hankali da daren nan ki kira mana hankalin babanku,ta sake miki wani,wancan nayi baqi na basu" ta fadi tana ficewa a kitchen din,shiru tayi kafin ya kwashe kayan ta fice itama bayan ta aje mugun tsaki.
A qalla ta shafe kusan minti goma kafin itama ta soma takawa a hankali tana ficewa daga kitchen din,bata san me ya taba zuciyarta ba batasan tana hawaye ba saidata shafi fuskarta,tana goge hawayen tana addu'ar bacci da haka ta kwanta bayan taja bargonta zuwa kafadunta.
Ta jima a kwance tana nazarin rayuwa kafin ta tattara dukka lamuranta ta sake miqawa Allah.
Ya dan jima tsaye shida drivansa yana qarewa gidan kallo,haka kawai yaji zuciyarsa ta nutsu ta aminta da gidan,yana jin gamsuwa da nutsuwa har cikin zuciyarsa,yana son mace mai kamun kai da jan aji,yana ganin kamar akwai alamun hakan tattare da ita,yanayin arziqin gidansu yana ganin kaman bazai sanyata qyamatar mai qaramin qarfi ba,kamar zata amsheshi haka yakeji,amma hakan bazaizama dalilin da zai sanya ya kasa jarraba ta ba kamar sauran,a nutse ya yiwa drivern nasa umarnin su wuce.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Qarfe biyu na rana suke takowa zuwa cikin layin nasu daga bakin titi zuwa gidansu ita da asma'u dake qunquni kamar zata fashe,taci alwashin bata sake hawa motar,duk da ba tsufa ne yasata yin hakan ba,uban motar da take ci ne kawai da kuma halin tsiyar qarfen nasara,inda Allah ya taqaita saida sukazo kwanar gidan nasu ta kakare musu a nan,itakam aysha na gefanta,baki daya bata ga abun bacin rai ba,don dai yau kadai.
"Malam ka cikani,Allah bazan biya ba"
"Wallahi saika biya kaji na gaya maka,ba inda zan sakeka kaje" hayaniyar mutum biyu kenan data cika kunnensu gab da zasu qarasa qofar gidansu,hayaniyar na tashi ne daga wani dan case dake maqale da gidan maqocinsu dake kallon nasu gidan,case ne da mai gadin gidan ya bude yana saida katin waya da sauran 'yan qananun abubuwa da ba'a samu cikin unguwar sai sunje waje mai nisa saboda yanayin unguwar tasu,dukkansu hankalinsu yakai wajen,asma'u ta ganeshi tsaf,yayin da aysha taso ta shaida fuskar,da sauri asma'u ta dauke kanta,hakanan taji gabanta na faduwa,ta yaya akai yasan gidansu?,me yake a layinsu?,fatanta daya kada Allah yasa ya nuna ya santa,don ta fuskanci yana da wata zarra da rashin fargaba.