← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 114

Sashe 48

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washegari da dagewar aliya da mero ta shirya cikin a tamfa,duk da cewa ba wani kwalliya tayi ba amma sosai tayi kyau,komai sabo ta saka daga cikin dinkin da asma'u ce ta zabi kayan har zuwa dinkin,hakanan taji tana sha'awar sanya kayan da daddy ne ya dinka mata,ta kasa taba kayan khalipha kwata kwata,komai a sukuku take yinsa,don hatta da karyawar safen da aka kawo musu tea da bread da chips da wainar qwai wanda batasan wanda ya hada ba bata iya ci ba,sosai aliya ta dinga sako hira da zance don ta sako jikinta amma ita kadai tasan ya take jin zuciyarta.

Goma na safe inna kulu ta aika tazo,da fari inna yelwa taso tayi gaddama amma daya daga cikin yaranta maza ya jata daki sukayi magana,batasan me ya gaya mata ba tace suje amma ta dawo kafin lokacin daura aure,tare suka fita da aliya don mero ta koma gida zata shirya kafin lokacin daurin auren yayi,don sai qarfe uku na yamma za'a daura,suna tafe aliya na yaba yanayin gari tare da tambayar indo wasu abubuwan,kusan tasan kowanne waje da abinda yake wajen kasancewarta sha gwagwarmaya ce.

Babu zato ba tsammani suka ga an sha gabansu gami da karta adda a qasa,a tsorace suka ja baya dukansu suna riqe da hannun juna,sai data duba sosai sai taga ashe dan ladi ne
"Indo baki isa kiyi aure ba idan ina raye...kin manta ke tawace?,har yanzu ke matata ce kuma ina sonki,babu wanda ya isa ya rabani dake"wani wawan tsaki taja sannan taja hannun aliya zasu wuce,don ta lura a buge yake ba cikin hayyacinsa yake ba,sake shan gabansu yayi
" na gaya miki ina sonki,babu inda kuma zaki daga nan sai gidana"ya fada cikin salo na maye,isowar wasu matasa wajen suka cakumi dan ladin sukai musu gefe da shi yayiwa ayshan dadi,haka suka wuce aliya na waigen dan ladin
"Waye wai wannan aysha..."
"Tsohon mijina ne"
"Dan ladi?" Kai kawai ta gyada mata,don tunawa da rayuwar datayi da shina qona mata rai yake,dariya aliya ta bushe dashi tana duban ayshan,tana son ta kalleta itama ta tsokaneta amma sai taga ayshan ta basar,da alamu har yanzu ranta ba'a sake yake ba,ganin haka itama ta share har suka isa gidan.

Ga mamakinta a canma jama'a ta samu zoqar ana shirye shiryen yinin biki sosai,a nan dinma maraba ake da ita,duk da bata wani ji abun har cikin ranta ba amma ta dan saki jiki albarkacin gwaggo asabe,saidai duk da haka nata ido,wuni bikinsu suke sosai,tana zaune tana binsu da kallo,lokaci lokaci tana share hawayen fuskarta,koda ace ba har zuciya suke mata wannan hidimar ba,koda ace ba don Allah suke yinin bikin ba,koda ace abun bai burgeta amma zata so ace mahaifiyata na wajen...zata so ace mahaifiyarta tazo...zata so ace tana ganin wulgawarta a wannan bigiren koda kuwa bata farinciki da ganin nata ko auren da take yi.

Qarfe daya na rana zayyanu dan qanin babanta yazo ya kirata,tana jinsu suna 'yan maganganun kiran itadai ta miqe suka wuce ita da aliya da wasu daga cikin 'ya'yan qannen umminta,sanda suka isa qofar gidan nasu ya soma cika damqam da jama'a,kusan kowa cikin shadda yake fara,matan kuma sanye da tasu shaddar light purple har zuwa cikin gidan haka kalolin suke,da alama dinkawa akayi kowa da kowa,hakan take kuwa,saboda tana shiga tsakar gidan dake cike da mata suka saki guda a tsakiyar kanta suna yabawa gami da godiya da dinkin shaddodin da aka yiwa kowa a cikinsu,ciki da wajen gidan,aliya ce ta ja mata mayafinta ta rufe mata fuska,kuka ne ya qwace mata,tana ganin komai kamar a mafarki,idan suka kirata amarya sai taji banbarakwai,tana ji kaman da gaske auren gaske zatayi bana samun 'yanci ba,ba yadda aliya batayi da ita tayi shuru ba amma hakan ya gagara,don ita kanta tasan bata da ikon tsaida wannan kukan,a haka aliya ta matsanta ta mata ta sake sauya wasu kayan,tayi kyau sosai saidai fuskarta duka tayi jajir ta tasa saboda kukan data kasa dainawa.

Kafin lokacin daurin auren gidan ya cika danqam da jama'a,ci da sha ake tako wanne fanni cikin walwala da dariya,saika rantse da Allah tun usuli ita din diyar gata ce a cikin gidan,tun tana kallon kowa cikin mamakin har ta daina mamakin ta zubawa sarautar Allah ido,wato a rayuwa idan kana da shi kaine wani?,kai ne abin so?,kaine abun taqama abun a nuna?,kai akewa biyayya?,kaine abun girmamawa koda baka biyayyawa mahaliccinka?,wadan nan tambayoyin ta dinga yiwa kanta suka dinga kai kawo da amsa kuwwa a kunnenta da kwanyarta.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*

*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_

*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300

*ko kuma*

07067124863

*DB*

28

Kafin a kammala daura auren tuni zazzabi da ciwon kai ya saukar mata mai zafi,haka ta samu can lungun gadon inna yelwa ta lafe,wanda da qyar ta yadda ta hau,gado ne da iya tsahon rayuwarta bata taba hawanshi ba koda da qiriniya irin ta quruciya saidai taga 'yan uwanta na hawa,kusan duk abinda ke faruwa daga cikin dakin zuwa farfajiyar tsakar gidan tana iya jiyowa,hayaniya ce kala kala cakude da muryoyin mawaqa da kidan qwarya wanda tun safe idan waccan ta tashi wata sai ta dasa nata,tana mamakin irin cikar data ji garin yayi,kusan gaba daya qauyen ya hade da hayaniya da dumin maganar daurin auren,duk wanda baka gani ba a wajen to bai kusa ne ko bai cikin garin,gayyar sodi kuwa ba'a maganarsu
"Sai yau kuttun farinjinki ya fashe ne indo?" Mero keta fada cike da al'ajabin halayyar dan adam,karadin maroqa kuwa har wani bai gane na wani,a haka ne ta jiyo sanarwar daurin aurenta daga bakin daya daga cikin maroqan wanda yafi kowa karadi da zaqin murya.

Idanunsa ya lumshe sanda aka kammala karanto siga aka shafa fatiha,yana jin kaman gaske wani b'ari na zuciyarsa na gaya masa ba gaske bane,Koma meye yana jin dadi cikin zuciyarsa,ko babu komai ya cikawa anni burinta na kawo yarinyar cikin ahalinsu,burin annin shine nashi,bai fatan taso wani abu guda daya da bazai iya bata shi ba koda kuwa rayuwarsa ce,ta damu da ita sosai kaman ma bashi yazo da zancanta ba itace tazo da shi,kullum zancanta take da sauran kwanakin da suka rage mata da zata bar gidan daddyn ta dawo cikin nasu gidan,ta dokanta sosai,tana ganin kamar hajar dinta ce zata dawo,ya tabbatar zatayi farinciki a sanda labarin daurin auren ya isa kunneta,yanajin wannan farincikin ne yake tayata shima.

Wasu sabbin hawaye ne suka gangaro mata ta gefan idonta,ta cusa hannunta qasan filo ta ciro wayarta,lambar wayar umminta ta lalubo sannan ta shiga wajen rubuta saqonni ta fara rubuta mata

_duk da na sani bani daga cikin yara masu 'yanci...bani daga cikin yaran da za'a nemawa albarka saboda laifukansu ga iyayensu...na sani fadar bata da wani amfani a gareki,amma a dai dai wannan lokaci ina neman alfarma a gareki karo na biyu a rayuwata,ki sakawa rayuwata albarka a ranar da aka dauran igiyar wani...ki nema min afuwa da albarkar rayuwa wajen ubangijinmu,koda cikin zuciyarki ne keda ubangiji...koda wannan ce alfarma ta farko kuma ta qarshe da zaki yiwa rayuwata,na barki lafiya,daga 'yarki mai mafarkin watan watarana zaki rungumeta kamar sauran zuri'arki_

Tura mata tayi,sai data tabbatar yaje sannan ta maida wayar qasan filo ba tare data saka ran samun amsa ba.

Duk yadda aka dinga hada hada da shigowar tawagar ango cikin gidan tayi luf babu inda ta motsa,duk da tana jiyosu suna cigiyar angon,har sukai suka fice taqi ta fito ko nan da can,kusan aliya ce ta zama uwa ta zama makarbiya.

Qarfe hudun yamma inna laraba mai aiki ta iso,tuni maman aliya suka juya ita da abbanta bayan ta saka mata kudi masu yawa a hannunta tace ta riqe,da hanzari aysha ta diro daga gadon ta rungume innar tana sakin kuka,lallashinta ta dinga yi tana mata fadan kukan da tayi daya sauya mata fuskarta ga zazzabi a jikinta,sai data nutsu sannan tayi mata nasiha gami da jan hankalinta,nasiharta tayi mata tasiri matuqa saboda ta tunasar da ita abubuwa da yawa,wannan shi ya taimaka ya riqeta har zuwa dare bata sake zubda wata qwalla mai yawan da zai mata illa ba,saidai kawai gatanan ne sukuku,wanda mutanen qauyen da yawa ke ganin rashin ganin mahaifiyarta da kalar alaqar dake tsakaninsu ne yake haifar mata da sanyin jiki.

Tun daga zuwansu zuwa dawowa yake karantar abubuwa da dama daga cikin rayuwarta,yaga gaskiya zalla,yaga ainihin labarinta da take bashi qarara kusan a aikace,baya manta zuwanshi na farko tattakin da yayi yaje qauyen nasu cikin gidan nas a zuwan mai bincike kan wace indo ba tare da sunsan kowaye shi ba,maganganu marasa dadi da yaji a kanta da mahaifiyarta daga bakunansu,abubuwan daya karanto daga idanunsu,amma ga mamakinsa zuwa na biyu da yaje da sabanin abinda yaje muau da shi da farko sai gashi ta farad daya komai ya canza,cikin qanqanin lokaci ya siya mata qauna da soyayya mai tarin yawa,duk da idean anni ce wadda Allah ya sallada mata qauna da soyayyar ayshan duk da bata taba sanyata a idonta ba,da gaske ne kaso mafi yawa na mutanen duniya sun sauya,babu mutunci babu qauna babu soyayya,komai suna aunashi ne kan mizanin me kake da shi?,me ka mallaka?,waye kai?,waka sani wa yasanka?,zaka iya siyan komai idan kana da kudi,zaka iya mallakar komai komai yana iya zama naka idan kana da abun hannunka,yakan kwatanta yanzu da rayuwarsu ta baya,sai yake ganin banbaci na zahiri mai tarin yawa,ya sauya abokan rayuwa da yawa,da rabu da wasu mutane da yawa ya sauyasu da wasu...saboda walqiyar da akayi suka ga kowa quru quru,kusan shirunsa yafi maganarsa yawa cikin motar,saboda tsohon ciwon kansa dake son ya tashi,wanda hayaniya da kuma tarin tunanin dake cunkushe a kwanyarsa keson tayar dashi,da fari mahmoud bai gane ba,ya addabeshi da tsokanar kodai kewar amarya yake,bai samu ya ganta ba,sai daga bisani ya gane matsalar ciwon kan nashi ce keson tashi,tilas ya tsaida ayarin motocin suka koma mota daya shida khaliphan iya su biyu,yadda hakan zai bashi damar hutawa sosai.

***********************
Chapter 48 · 0% Book details