← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 95 OF 114

Sashe 95

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Kardai fita zakiyi?" Bara'atu ta tambayeta
"Eh wallahi zanje dubiya ne....don Allah saqo zan baki,idan haidar ko mus'ab wani daga cikinsu ya shigo kice masa ina gidan daddy,amma bazan jima ba can zan dawo,akwai tamfofi da anni ta bayar za'a dinka guda uku tace telanta zasu kaiwa su sun sanshi"
"To a dawo lafiya,Allah ya tsare"
"Yauwa amin" nan ta juya ta fice,koda tazo fita itama bata bi takan kowa ba,sai kallo da kowacce take binta dashi a sace cike da baqinciki kishi qyashi da kuma hassada,maryam ce taja tsaki tana gyara kwanciyarta
"Shi abba yasan khalipha zaiyi kudi ya kasa taimakonsa,ai gashinan yanzu suna ganin arziqi saidai asan mana" take fada cikin zuciyarta
"Ya isheki haka malama,ya muna zaune muna hutawa zaki damu mutane da tsaki ne?,wai shin dawa ma kike ne?"
"Da uban wanda ya tsargu" ta fada tana gallawa zeenart harara,ai kuwa saita aje kwanon hannunta ta miqe tayo kan maryam din
"Ni kike zagi ko uba na?"itama tsaye ta miqe
"duk wanda kika zaba,aikin banza kawai,da kike wannan haqiqancewar wani kika fi har da zaki yiwa wani iyaka dayin yadda yaso,kin isa ki hanani tsaki ko cika gidan nan zanyi da tsaki?,ina cewa babu wanda gidan yake mallakinsa a cikinmu bare wani ya damu wani" nan fada yaso kacema tsakaninsu,sai suka hau 'yar gore gore,rahama ce ta leqo ta gansu sunayi,kallon banza ta watsa musu sannan taja tsaki ta juya ta koma dakinta ta maida qofar ta rufe,ita yanzu duka ba wannan ne yake damunta ba.

Aysha kam bata masan me suke ba,sanda ta fita gidan ba driver ko daya,duk sun tafi rakiyar anni kuma babu wanda ya dawo,malam shehu kuma ya tafi kasuwa cefane,hakanan ta taka zuwa bakin daya daga cikin motocin nata,ta tsaya gaban qaramar ciki tana dan dubanta,bismillah tayi ta saka muqullin ta bude ta shiga mazaunin driver,sai take jin fargaba,tana jin kamar ba zata iya ba,karon farko da zata soma driving,duk da ta jima da iyawa amma bata taba tuqi ba,saita rufe idonta ta karanto addu'ar hawa abun hawa,hakan yasa mata nutsuwa,ta maida qofar ta rufe,ta tashi motar ta daidaitata ta dan danna horn,mai gadi ya bude nata gate din ta fice a hankali cikin nutsuwa.

Sanda take fita su haidar na shigowa,mus'ab ne ya nunawa haidar ita,mamaki ya kamasu,suka dinga yi mata dariya mus'ab na fadin
"Wai yau anty da driving?ko ina zata oho,bari ta dawo yau zata sha tsokana"
"Ni kaina naso muna nan zata fita" haidar ya fada yana dariya,don basa manta yadda take da tsoron driving da kanta,taga shigowar motocin,sai taji kaman ta tsaya ta yiwa daya daga cikin direbobin magana su kaita,sai kuma kawai ta wuce abinta.

Tun daga harabar gidan haidar ya soma jin kaman hayaniya,saboda haka yabar mus'ab anan ya shige zuwa ciki,sanda ya shiga sa'insa tayi nisa,cikin fusata ya katsa musu tsawa nan take kowacce tayi shuru
"Wannan wanne irin iskanci ne da zaku maidawa mutane gida gidan karnuka?,toko wacce ta shiga taitayinta bana cike da rashin mutunci,ku bace ku bawa mutane guri da'alla ko kowacce ta wuce gidansu" hakanan maryam da zeenart suka wuce zuwa dakin suna qananun maganganu da gunguni,amal ya duba wadda ke zaune duk taqaddamar da ake
"Ke ba zaki tashi ba kenan sai nayi quli quli dake!" Ya fada.mata a zabure,ba shiri ta miqe itana ta wuce daki,don tasan halinsa sarai idan ya juye kaman khalipha haka yake komawa ba sauqi,dogon tsaki yaja sanda mus'ab ya shigo yake tambayarsa abinda ke faruwa,yana shafa tsakiyar kanshi yace
"Wadan nan mahaukatan yaran mana,ni na tsaya ma tambayarsu neke faruwa na kora kowacce,zasu zo suna mana hauka kaman gidan su" yana fadin maganar yana wucewa kitchen.

Cikin zuciyarta take hamdala sanda take shigowa layin nasu,sai kuma ta sakarwa kanta murmushi tana dariyar tsoro irin nata,yadda ta dauki abun ma duka ashe baikai haka ba,horna tayi cikin minti daya mai gadin gidan daddyn ya bude mata qifa ta sanya motar tata ciki,tana cikin rufe motar bayan ta fito adaidaita ta shigo gidan,saita daga kai cikin mamaki tana duban adaidaitan,asma'u ce ta fito daga ciki tana miqawa mai adaidaitan kudinsa,canji ya miqo mata saita watsa masa wani kallo
"Kai bana son iskanci yanzu zan saka ayi ma duka kana dai ganin cikin gidanmu ka shigo,yaya za'ayi ka dauki dubu daya daga inda ka daukoni zuwa nan,ko an gaya maka satar kudin ake?"
"Amma dai hajiya aiba haka mukayi dake ba ko?,drop kika ce bakyason na dauki kowa,a qa'idama kudinki sunfi haka,kuma wallahi kibar ganin gidanku na shigo baki isa ki dakeni akan haqqina ba" ashar ta maka mishi tana fadin
"Yau zakasan ubana waye zakaga qaryar iskanci" shi kuwa ganin haka saiya fito daga adaidatan nashi yana fadin idan ta isa tasa a dakeshi din saiya farke mutun wallahi ko waye,kallo daya aysha tayi masa ta karanceshi,irin matasan nan ne masu zuqe zuqe,askin kanshi kawai ya isa ya gaya maka wayeshi,a hankali ta tako ta saitin matashin tayi sallama,saiya tsaya da hayagagar da yake yana dubanta cikin dan layi,kwarjini tayi masa,haka shigarta ta banbanta data asma'un,amsawa yayi ta bude jakarta ta ciro dubu biyu sabbabi kar,wanda tun wancan satin ta ciro su a atm ta yiwa anni siyayyar tafiya a matsayin tata gudunmwar,duk da babu abinda ta rasa amma ance gaida mai gaidaka,miqa masa tayi sannan tace
"Kayi haquri don Allah malam,dauki motarka ka tafi" saiya amshe yana cewa
"Allah dai ya biya,kinga inda akasan arziqi,da alama wannan ba matsiyaciya bace irinki,ke ina jin ma ke 'yar riqo ce ko mai aiki a gidan don irinku sunfi kowa yin haka,matsiyaciya mai qaryar arziqi" ya shuga babur dinsa zai tayar,saita yunqura zata biye masa da sauri aysha ta damqe hannunta,qamshin turarenta da laushin tafin hannunta ya sanya asma'un waiwayawa tana dubanta
"Ba girma da mutuncinki bane anty,bakiga a yanayin da yake ciki ba?" So tayi ta wanke ayshan tas,saboda maganganun daya yaba mata sun qona mata rai sosai,to amma da wani abu ya fado mata a rai wani quduri da ayau takeson ta cimma saita hadiye komai
"Da kin barni na nunawa dan iska iyakarsa ai,basu da mutunci 'yan adaidaitan nan,koda yake ke dakike hawa saikinfi kowa sani ai"murmushi kawai ta saki
"Ki qyaleshi kawai,mun yini lafiya?" Ayshan tace da ita sanda suka soma takawa zuwa ciki,da qyar asma'un ta hadiye abinda ke damunta ta dan saki fuska ta amsa,wanda hakan yayi mata dadi
"Indo motarnan bata rufu ba fa" cewar usama wanda ta barshi yana duba motar daddy data yi parking kusa da ita
"Oh,ohkey,ina sauri ne zanwa mai adaidatan can magana naga kamar a buge yake,don Allah dan rufemin usama idan ba damuwa ka miqo min key din cikin gida"
"Toh ba matsala" ya karba yana yin gaba,su kuma suka cu gaba dayin cikin gida,saidai asma'u ta kasa cewa komai,mota kuma wacce iri?,ina ayshan ta samu mota?,kasa haqura tayi sai data waiwaya taga motar sanda usman ke rufeta,daskarewa tayi wani malolo ya taso mata wanda ta kasa hadiyeshi
"Mota kikayi aysha?"murmushi tayi
"a'ah,tunta lokacin bikina khalipha ya bani,bana hawa ne dai kurum" kan uba,wanne irin kudi wai gayen nan ke da shi ne?,asma'u ta furta cikin ranta,kaman baisan ciwonsu ba?,ko baisan nawa motar take ba,lallai ba shakka ya zame mata dole tayi wani abu,ita ya kamata ace tana cikin wannan yanayin ba aysha ba,taya zata zamewa aysha tsanin da zata taka ta cimma wani abu a rayuwarta?,da wannan saqe saqen zucin suka isa falon,wanda asma'u bata samu damar sake cewa komai ba.
52

Anty halima,anty kubra da anty lubabatu na zaune a falon,da fari sun soma hayaniyar ganin asma'u ganin shigowar aysha ya sanyasu rage hayaniyar tasu,dukkanin idanunsu na kan ayshan,kowa da irin kallo da yake mata,musamman anty halima da komai na ayshan ya tsone mata ido
"Ashe ana ganinku?" Cewar anty luba tana duban ayshan,tana neman abun fada,murmushi ayshan tayi
"Ana ganinmu mana anty luba,makaranta ce kawai ke sakawa wani zubin bana zama available koda yaushe,sai weekens nake dawowa gida" tabe baki anty halima tayi
"Kuma a haka ake zaman auren?" Dubanta aysha tayi,ta karanceta tsaf,ta kuma gogu da zama dasu hanan
"Eh...ba wata damuwa bace ko matsala ai idan akwai fahimtar juna tsakaninka da abokin zamanka"toh baki yasan abun fada baisan me za'a maida masa ba,sai maganar ta dan yiwa anty halima zafi,tunda suke da aysha wannan ne karon farko data soma maida mata amsa dai dai da maganarta,ta fuskanci amsar ta shigeta dai dai yadda ya kamata,don haka saita miqe tana cewa
"bari na qarasa na duba jikin daddyn" ba wadda ta amsa mata.
Chapter 95 · 0% Book details