← Book details Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 114

Sashe 87

Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Baqinciki ne cike a qirjin asma'u yayin da take kallonsu,kota ina khalipha ya yagawa hamid,koda can dinma tana sane da hakan,kawai rashin kudi da bata taba zaton khalipha nada shiba shinya janyo mata komai,ga dukkan alamu sun nuna babu wata matsala tattare da ayshan,ko waye kai ka kalleta kasan bata da damuwa,sai taja numfashi ta kuma fito dashi zuciyarta na ayyana mata abubuwa da yawa,zuwa yanzu ta soma gajiya da zama da hamid din,babu wata alama dake nuna zai sauya,kai babu ma batun sauyi saima sake tabarbarewa da al'amura sukayi,baya ga shegen maqonsa,rashin sanin darajar aure da iyali,sai kuma ta gano wata mummunar dabi'a data fi komai daga mata hankali,wato hamid yana neman mata,matan ma ya rasa wadda zai nema sai 'yar aikinta kafira ba musulma bama,sannan a yanzu haka yarinyar na cikin gidan duk data kamasu amma ya murje idonsa yace karta soma kuskuren korarta,tana ji tana gani ta barsu,Allah ya sani tana son hamid,saidai maganar gaskiya ba zata iya rayuwar takura da mammaqo ba,abu na farko daya sanya ta guji duk wani saurayi a baya data fuskanci babu dandalen arziqi tattare da shi,tunin daya soma konno mata kai ta dinga wassafa da kimanta yiwuwar faruwarsa,zai yiwu kuwa?.

Da wannan tunanin har jirginsu ya iso kano bata sani ba,koda suka fito daga airphort din sai tadan qara sauri ta cimmusu
"Na gode khalipha sosai,Allah ya qara arziqi" ta fada cikin murmushi,cikin mamaki suka dubeta,khalipha shi ya soma kauda kai,ya kama hannun aysha sukayi gaba sannan yace
"Ba donke nayi ba ai,albarkacin princess humaira kika ci" sosai maganar ta daketa,amma saita share ta sake takawa ta cimmasu
"Ko zaka sakamin number dinka don Allah,bai kamata ace bama zumunci ba,abinda ya faru ya riga daya faru insha Allah kuma bazai sake faruwa ba" murmushi yaso.ya subuce masa saboda kalaman rainin hankalin asma'u,sai ya saka hannu ya amshi wayarta da take miqo masa,har ta soma murna taji yace
"Riqe maza don Allah,da wannan wayar kike amfani?" Saita kada kai tana sakin murmushi
"Kiyi qoqarin canza wata don Allah,saura kadan ta jimin ciwo....muje princess" ya fada yana sake riqe ayshan da kyau,binsu kawai tayi da kallo baki bude,wato bai manta duk wani abu data taba yi masa kenan ba?,anya wannan tafiyar zata zama da sauqi kuwa?.

Aysha kam rasa bakin magana tayi,sauyawar asma'u lokaci guda?.....sauyawar asma'un ba abu bane mai sauqi ta santa sarai,wala'alla tana kwadayin abota dasu ne kamar yadda halayyarta take nason abota da suk wani mai kudi,dason ace tana da kusanci dashi ko kuma ta sanshi.

Sanda suka isa gida ta tsammaci zasu shiga sashen anni ne dafarko,sai taga yayi fuska ya kara wayarshi a kunne
"Anni mun iso,amma zamu dan huta kafin mu shigo....ohk" ya fada yana sauke wayar,hada ido sukayi saiya dan basar yana cewa
"Bana son in shiga na soma karo da fuskar wadan can yaran,don haidar ya gayamin maryam ma tazo,so daga yau babu zaman cin abinci a cikinsu" ya fada sanda suka shiga falon.

Qarfe takwas na dare tana zaune gaban annin cikin ado da qamshi ta nannade jikinta da farar laffaya kamar amaryar da aka kawo yau,shigowarta kenan sashen shima gajiya tayi da laqai laqai din khalipha ta gudo yana wanka donta qagu tazo taga annin,nasiha take mata mai kwantar da hankali kan yanayin haduwarta da mahaifiyarta,ta kuma bata shawarar ci gaba da addu'a,sosai duk wani qunci na zuciyarta ya zabge tun a lagos,kukawar data samu wajen khalipha ba qarama bace,taa zauna taayi nazari sosai tun a can,har ta dinga jin kamar tayi aiki da shawarar basma,saidai mahaifiya tafi gaban wasa.

Daganan wata hirar daban suka shiga yi da annin,aysha ta dubi dakin annin sai taga duka baiyi mata yadda takeso ba
"Anni...dakinki kwana biyu yayi kewata gaskiya" murmushi ta sako cikin jin dadi
"Ba dakin kadai ba har masu gidan,haidar cewa yake yayi zaton kwana daya ko biyu xakuyi sai kuka wuce haka" dariya ayshan tayi,kafin tace wani abu akayi knociking qofar dakin anni ta bada izinin shigowa,matashiya ce wadda a qalla ta kusa sa'ar rahama,ta qaraso dakin idonta akan aysha,da qyar take magaba kana kallonta kasan irin yaran nan ne da sakalci da tabara yayi musu yawa,bawai rashin wayo ko dolanci ba alamun rashin kwab'a tun daga quruciya.

Tana magana da anni amma idanunta qir kan aysha lanqwasa yatsunta,hada ido sukayi da ayshan saboda tsabar kallon da take mata yasa taji a jikinta
"Sannu" ayshan tace mata ganin sum hada ido,duk da a qa'ida itace zata soma mata.magana a matsayinta na wadda tazo ta samesu kamar yadda annabi ya koyar
"Yauwa sannunki" ta maida mata tana dauke kai ganin ayshan ta gane kallon qurillar da take mata
"Ya khalipha ya dawo ko?,naga kamar motocinsa"
"Eh ga matarsa nan aishatu sunanmu daya" duban ayshan ta sakeyi sannan ta dauke kai sai kuma tayi shuru.

"Yaushe zaki koma makaranta ne?,kamar kuna tsakiyar karatu ne ko?" Anni ta yanke shurun tana tambayar aysha,dan murmushi tayi
"Gobe...gobe in sha Allah,saboda muna da c.a goben da azahar"
"Batayi candy bane?" Maryam ta tambaya tana duban anni cikin salon dake nuna raini qarara
"A'ah,masters take hadawa" sai ta dan sake kallon ayshan again sannan ta dauke kai tana cewa
"K'nnnnn" a yadda taga shekarun ayshan tayi tsammanin ko degree na farko batayi ba bare aje ga masters,saboda ita gatanan har yanzu degree din taqi haduwa saboda wasa da sakarci data saka a gaba.

Lokacin cin abincin yayi don haka tare suka sauko gaba dayansu,basu kai ga wajen dining ba khalipha ya shigo falon,yayi kyau cikin fararen qananun kaya long sleev shirt da trouser shima fari,idanunshi kan aysha,saidai a dakenshi ya shigo saboda yasan wadanda zai taras a wajen,dan satar kallonshi tayi kadan,ita kanta saiya mata kwarjini ya cika mata ido,hakanan yayi mata kyau sosai,gaidashi sukayi ya karba a dake yana basarwa,fasa hawa dining din anni tayi ta dawo ta zauna a falon tana maraba da khaliphan,saboda haka mutum uku ne a wajen,rahama,maryam da amal,kowacce kanta na fisga tana cin abincinta ba tare data dubi 'yar uwarta ba,saidai dukkansu kunnensu na wajensu anni.

Nan tasa a kawo mata abincinta,hakan yayi masa sosai,tana ci suna hira,shi da ayshan dukkansu ba wani yunwa suke ji ba,don basu jima da shiga ba tayi musu girki suka ci,wanda ya jima baiji dadin cin abinci irin na yau ba.

Haidar ne da mus'ab suka shigo falon suna tafe suna musu da alama wani abu suka gani,harararsu khalipha yayi
"Hala bakusan muhimmancin sallama bako da zaku shigo da surutu a bakunanku" dukkansu basu san ya dawo din ba da basuyi wannan katobarar ba,shafa kai mus'ab ya soma,yayin da haidar yace
"Afwa yaya,mantuwa"
"Next time.." Bai qarasa ba yayi shuru suma kuma sun fuskanci me take nufi gargadine saboda haka suka ce
"In sha Allah" haidar ne ya qarasa gefan aysha yana murmushi
"Shuru anty kunyi tafiyarku?"
"Ai gashi mun dawo ya haidar"
"Gwara kam don wallahi ba qaramin missing dinki mukayi ba,duk gidan dadinsa sai a hankali" ya fada yana murmushi,dubanshi khalipha yayi,wani abu yadan taba ranshi
"Duk mutanen dake cikin gidan ba mutane bane sai ita kadai?"
"Ba haka bane yaya,antyn ...."
"Ohk idan ta wuce makaranta gobe saika bar gidan"
"Da sauri haka daga dawowarku?"murmushi kawai aysha tayi,sai ya juya yana tambayar anni me aka dafa
" jeka ka gani" ganin wadanda ke kan dining din yasashi dukan kafadar mus'ab
"Dalla jeka debo mana abinci,wadancan 'yan zaman dumama kujerar sun wani cike wajen,haka zaka je kana cin abinci suna qarema bakinka kallo kamar wasu mayu", can qasan ranta aysha tayi murmushi,a yanzu ta riga data san me yasa haidar din ke yawan mita akai,a baya mamaki take kan me yasa sam ba hadauwar jini tsakaninsu,ba shakka ma badon uwa ta gari da Allah ya basu ba zuwa yanzu ko kusantarsu dangin ubansu basu isa suyi ba,saidai uwa ta gari da Allah ya basu ya santa zakayi zaton komai bai faru ba,mus'ab na girmama haidar kamar yadda haidar ke bawa khalipha girma,yana game a wayarshi ya isa wajen yaja plate ya zubo musu ya sauko dashi,da yake sau tari sukanci abinci kwano daya idan lokacin cin nasu yazo dai dai,annin ta riga ta saba musu da haka tun lokacin quruciya.

Da d'ai d'ai amal da rahama suka dawo wajen bayan sun gama cin abincinsu,banda maryam data wuce daki tana amsa waya
"Tashi mu wuce" khalipha ya fada bayan ya miqe tsaye
"Tun yanzu?dare baiyi ba da yawa" Rahama ta tambaya idanunta na kansu
"Mun dawo daga tafiya akwai gajiya da take buqatar a wareta" khaliphan ya fada yana hade fuska kamar ya manta anni na wajen,aysha kaman ta zura da gudu haka taji saitaja mayafinta ta sake rufe kanta
"Anni sai da safe"
"Allah ya bamu alkhairi,mu tashi lafiya ayshatu"
"To anni" haka kawai taji kallon da suke binta dashi bai mata ba,tana sane tace
"Anty rahama,sister amal saida safe.....kinsan ya khalipha da son jiki tausa yace yana so" aysha ta fada can qasa saitin rahama wanda tafi kusa da ita,ta yanda idan ba rahaman da amal dake kusa da itaba babu maijin abinda tace,saidai ta makaro,tuni khalipha dake tsaye ya jiyo abinda ta fada din,wato itama ta iya tsokana kenan da cusa haushi ko?,dukkansu zuciyoyinsu kamar zasu fito,basu sake magana ba har suka ida fita daga
Chapter 87 · 0% Book details