Sashe 63
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dukkansu suka mishi sannu da zuwa yayin data maida kai tana ci gaba da gyarawa anni kai,shi kuma suna hira da annin,jifa jifa yakan daga kai ya dubeta sannan yaci gaba da abinda yake,tunaninsa daya ya take ji cikin ranta a yanzu haka data rasa soyayyar mahaifiya?,shi kadai yasan dadin da yake ji aduk sanda ya zauna suna hira da anninsa,ita kuwa bata taba samun irin wannan damar ba tsahon rayuwarta,amma har ta iya jure hakan ta hadiyeshi cikin zuciyarta
"Sannu takwara....kije ki nemi abinci kici kuma hakanan,tun dazun banga ko ruwa kinkai bakinki ba" murmushi tayi tana goge hannunta a kunyace tace
"Azimi nake" duban khalipha anni tayi
"Ah...amma kasan tana azumi baka gayamin ba bare a tanadar mata wani abun?" Dan dawurwura yayi sannan ya sake kallon ayshan kafin ya dubi anni,ya bude baki zaiyi magana ta rigashi
"Ban sanar mishi ba anni,saboda hanani zaiyi" ajiyar zuciya ya saki donta qwaceshi,ya bude bakinsa ne kawai ba tare da yasan me zai gayawa annin ba
"Ma sha Allah....bari nasa su atika sumiki wani abun haka"
"A'ah anni duk abinda suka dafa zan iya ci" tana gama fadin haka ta tsinkayi muryar khalipha yana qwalawa laure kira daya daga cikin ma'aikatan,cikin sakan goma ta bayyana a falon
"Idan akwai garin flour kiyimin dan wake yanzun,ayi mishi hadin salad pls"
"In sha Allahu yallabai" ta fada cikin girmamawa gami da miqewa ta juya zuwa kitchen da hanzarinta,yana waiwayowa suka hada ido da ayshan,saita sadda kai tana mamakin ya akayi yasan abincin da take matuqar so?,sau tari a gida takai duk sanda akayi danwake ko za'a daketa saitaci,hakanan koyaya aka bar ragowa bata barinsa saita bi ta cinye komai sanqarewar da yayi shida dafaffen wake(qulu),sharewa shima yayi kamar baiga kallonshi data sata ba,janyo jakarshi yayi ta office daya shigo da ita ya bude ya fito da da wasu takardu ya miqawa ayshan yana mata bayani
"Komai ya kammala,on 29 zaku fara lactures in sha Allah,yau saura sati daya kenan"tuni hawaye ya cika idanunta,kuka yana son qwace mata tana yunqurin danneshi,ta rasa me zatayi me ya kamata tayi,kaman wannan ne karo na farko da zata soma karatu haka take ji,sai ta zamo daga saman kujerar ta durqushe a gabansu shida annin
"na gode,ubangiji ya saka da mafificin alkhairi,Allah yayi muku sakamako da aljannarsa madaukakiya,Allah y...."
"Ya isa haka ayshatu...wannan addu'ar duka kina iya mana ita a zuciya,tashu ki tafi abinki,ki saka a ranki kamar a gidanku aka miki hakan" da qyar ta iya miqewa saboda kuka,inama ace a gidan nasu ne,inama ace ahalinta ne ke mata haka,duk wata soyayya da zata gani daga garesu a yanzu ba shakka akwai dalilin da yasa suke mata ita,ba haka kawai bane,da wannan kukan takai kanta sashensu ta zube saman kujera tana ci gaba da rerashi.
Gab da magariba yabar wajen annin don zuwa ya daura alwala ya wuce masallaci,tura qofar yayi bakinsa dauke da sallama,saman kujera ya hangota nannade waje guda,sheshsheqar kukanta da jan majina na fidda sauti kadan kadan,tsaiwa yayi yana dubanta duk da baya iya ganin fuskarta,duk sanda wata mace mai shekarun hajar ke kuka sai ya dinga jin kamar itace take kuka awancan lokacin da har yau ya kasa bacewa daga qwaqwalwarsa,lokacin daya sakawa suna da baqin lokaci,shi yasa a yanzun kukan nata ke sokarsa sosai,takawa ya soma yi zuwa wajen da take sai kuma yaji ana knocking,hakan yasanya ya sake juyawa zuwa wajen qofar ya bude,larai ce dauke da kayan kwanukan abinci,nuni yayi mata data aje,ta aje din kuwa a ladabce ta juya tabar wajen,ya sunkuya ya dauki kwanukan dai dai sanda ake qwala kiran sallar magariba,saman tebur din dake daura da ita ya aje
"Kukan ya isa haka,idan kuma a fasa makarantar ne kuma toh" da sauri ta tashi zaune tana hadiye kuken gami da qoqarin goge kyawawan idanunta da suka dan rine saboda kuka,ganin haka ya sanyashi wucewa ciki ya barta nan.
Sanda ya fito zai wuce masallaci tana zaune a wajen,jiranshi take ya fito ta shiga ta wanke bakinta,don idan daya yana cikin dakin dayan bai shiga har sai ya fito,har gwarashi wani lokaci zuwa lokaci yakan shiga idan akwai uzurin da bazai iya zaman jira ba,kaman zai wuce office yayi mantuwa zai dauki wani abu da makamantansu,dukkansu suna jin nunansu kaman baqi,saboda ba wanda ya taba rayuwa da wani jinsi daba nashi ba amuhalli guda sai wannan lokaci.
A bakin gate suka hadu da mus'ab da haidar,tun fadan daya yiwa mus'ab din bai sake kamashi da laifin rashin zuwa salla isha'in ko asuba ba,tare suka jera abinsu gwanin sha'awa,akwai qauna da fahimtar juna mai tarin yawa tsakaninsu,duba da wahalar da suka sha a baya wadda ita ta sake haifar da danqon qaunar junansu,haidar ke bare dabino yana ci khalipha ya kalleshi,yasan ma'anar kallon,da sauri yace
"Sorry yaya,kasan yau azumi mukayi ni da anty,ban samu na tsaya nayi bude baki ba kar jam'i ya wuceni,kuma ba'ason asha ruwa baka kai komai bakinka ba" bai sake cewa da shi komai ba,saidai yana mamakin yadda duk 'yan gidan keji da ayshan,yasan lallai ita rinjayi haidar ya soma azumin,don kwata kwata basa shiri da azumi.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Tun daga cikin dakinta take jiyo muryar hamid yana qwala mata kira,sosai kiran nashi ya bata tsoro har tana tuntube garin sakkowa saboda qara dage murya da yake wajwn kiran nata,a kitchen ta sameshi a tsaye,yayin da me aikinsu itama take tsaye gefe guda kantaba qasa kamar kazar da aka jiqa a ruwa,tana shiga ya dago mata kwalin lipton dinsu yana dubanta,sam bata fahimci me yake nufi ba sai da yayi magana
"Ya akayi ganyen shayin nan ya qare tun yau?"
"Kaman yaya?" Ta tambayeshi cikin takaici tana yamutsa fuska
"Tunda baki gane ba bari nayi miki bayani dalla dalla,sanda na kawo lipton din nan na qirgashi a gabanki na kwana sittin ne,ya akayi ya qare kwana ashirin kacal" hannayenta ta saka ta riqe qugunta duka biyun tana kallon hamid,itakam yanzu abun nashi bayan haushi ma tsantsar mamaki yake bata,koda wasa wani yace zaiyi abinda yake din yanzu sai anji kansu
"Ganyen shayin banza ganyan shayin wofi da zaka dinga yimin wannan kiran mafarautan saboda shi,kai yanzu hamid bakaji kunya ba saboda ganyan shayi kake daga jijiyar wuya haka,ohkey toni ban gaji tsiya ba,bazan bi wani lissafin ganyan shayi ba wallahi"
"Eh saboda ai bakisan ciwon kudi ba bakisan ciwon nema ba,yadda nayi almubazzaranci a waje haka ma yanzu kikeson naci gaba?,toba kudin banza gareni ba,lipton kuma saidai kici gaba da siya da kanki har kwana sittin ya cika" ya qarashe fada yana wurga kwalin a shara ya juya fuu ya fita daga kitchen din da alama ma ficewa xaiyi daga gidan donya shirya fes abinshi cikin suit kai baka ce shike magana kan lipton ba,binsa tayi da sauri tana tsaidashi,bai tsaya din ba har sai daya shiga motarsa yana shirin tada ta
"Man shafawa ta ne ya qare....inason wani irin na cikin kayana shine ya karbeni" dariya ya saki yana kallonta kamar yaga mahaukaciya
"Da Allah matsamin kina batamin lokaci kar baqina su wuce kija min asara,don na fuskanci ke bakisan darajar kudi ba"
"Wai hamid lafiyarka kuwa anya na asiri akayi maka ba?" Ta fada cikin harxuqa da mamaki,dariya ya sakeyi sannan ya ziro qafarsa daya waje kaman wanda ya fasa tafiya ya kalli cikin idanunta sosai
"Asma'u,kudi kika fiso a rayuwarki su na saka na shigo dake gidana,kin zaci ni wawa ne wamda baisan ciwon kudi ba saboda.ina da su ko?,toko dana tara bana almubazzaranci bane,kuma kaina na tarawa ba wani ko wata ba,idan zaki koyi rayuwar akwai da babu ki koya,shine kawai zaisa mu samu zaman lafiya ni dake matuqar ko zakici gaba da tambayata wani abu daya shafi in kashe kudina baki gayyaci zaman lafiya a gidan nan ba" yana kaiwa nan yaja murfin motarsa ya rufe ya kunnata ya dannawa mai gadi horn yaja motarshi ya fice.
Kuka asma'u ta saki ta juya zuwa cikin gidan a guje tana addu'ar Allah ya tasheta daga wannan mummunan mafarki da take,idan kuwa har ya tabbata mafarkin take ita da hamid ko hanya sunbar hadawa,sai data tabbatar cewa ba mafarkin bane ta soma tunanin sihiri 'yan adawa suka mata suka juyar mata da hankalin hamid dinta,banda haka mutum mai kudi kamar hamid ace yana maqo irin haka ba shakka da wata a qasa,hakan ya sanya ta dauki wayarta ta lalubi mommy don kai mata qorafi kamar yadda ta saba,don ko misqala zarratin asma'un bata da juriyar riqe damuwa ko solving matsalolin da duk zasu taso mata da kanta.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
35
Kusan tunda suka taho ita da shi fuskarta ke a cunkushe,ba don komai ba sai don batasan abinda zata je ta tarar ba a gidan,sam bata wani sha'awar zuwa gidansu hamid din,duk da cewa tunda sukai aure bata taba zuwa ba sai yau daya matsanta mata sai taje,saboda zaiyi tafiya ne shima,gaba daya haushin duk wata tafiya tashi take,a yanzu baya cikakken sati daya a gida,bashi wancan gari bashi wannan,bata isa tayi qorafi ba yanzu zai hauta da gorin yana yawon neman abinda ta aureshi ne saboda shi.
A harabar gidan ya tsaida motar sannan ya kasheta,fitowa yayi hakan ya sanya itama dole ta fito tabi bayanshi tana hade fuska har suka isa falon gidan.
Qannenshi ne zaune gaban t.v suna kallo,maza biyu mata biyu sune wadanda suka rage ba'a aurar ba,mahaifiyarsu na tsakiyarsu,kowanne yaci uban asma'u a girman kai da tabara,hakan ya sanya yayansun kawai suka yiwa sannu da zuwa kowa yaci gaba da sabgarsa,babu abinda uwar tace musu don ko ita bata nuna tasan tare suke da ita ba.
"Sannu takwara....kije ki nemi abinci kici kuma hakanan,tun dazun banga ko ruwa kinkai bakinki ba" murmushi tayi tana goge hannunta a kunyace tace
"Azimi nake" duban khalipha anni tayi
"Ah...amma kasan tana azumi baka gayamin ba bare a tanadar mata wani abun?" Dan dawurwura yayi sannan ya sake kallon ayshan kafin ya dubi anni,ya bude baki zaiyi magana ta rigashi
"Ban sanar mishi ba anni,saboda hanani zaiyi" ajiyar zuciya ya saki donta qwaceshi,ya bude bakinsa ne kawai ba tare da yasan me zai gayawa annin ba
"Ma sha Allah....bari nasa su atika sumiki wani abun haka"
"A'ah anni duk abinda suka dafa zan iya ci" tana gama fadin haka ta tsinkayi muryar khalipha yana qwalawa laure kira daya daga cikin ma'aikatan,cikin sakan goma ta bayyana a falon
"Idan akwai garin flour kiyimin dan wake yanzun,ayi mishi hadin salad pls"
"In sha Allahu yallabai" ta fada cikin girmamawa gami da miqewa ta juya zuwa kitchen da hanzarinta,yana waiwayowa suka hada ido da ayshan,saita sadda kai tana mamakin ya akayi yasan abincin da take matuqar so?,sau tari a gida takai duk sanda akayi danwake ko za'a daketa saitaci,hakanan koyaya aka bar ragowa bata barinsa saita bi ta cinye komai sanqarewar da yayi shida dafaffen wake(qulu),sharewa shima yayi kamar baiga kallonshi data sata ba,janyo jakarshi yayi ta office daya shigo da ita ya bude ya fito da da wasu takardu ya miqawa ayshan yana mata bayani
"Komai ya kammala,on 29 zaku fara lactures in sha Allah,yau saura sati daya kenan"tuni hawaye ya cika idanunta,kuka yana son qwace mata tana yunqurin danneshi,ta rasa me zatayi me ya kamata tayi,kaman wannan ne karo na farko da zata soma karatu haka take ji,sai ta zamo daga saman kujerar ta durqushe a gabansu shida annin
"na gode,ubangiji ya saka da mafificin alkhairi,Allah yayi muku sakamako da aljannarsa madaukakiya,Allah y...."
"Ya isa haka ayshatu...wannan addu'ar duka kina iya mana ita a zuciya,tashu ki tafi abinki,ki saka a ranki kamar a gidanku aka miki hakan" da qyar ta iya miqewa saboda kuka,inama ace a gidan nasu ne,inama ace ahalinta ne ke mata haka,duk wata soyayya da zata gani daga garesu a yanzu ba shakka akwai dalilin da yasa suke mata ita,ba haka kawai bane,da wannan kukan takai kanta sashensu ta zube saman kujera tana ci gaba da rerashi.
Gab da magariba yabar wajen annin don zuwa ya daura alwala ya wuce masallaci,tura qofar yayi bakinsa dauke da sallama,saman kujera ya hangota nannade waje guda,sheshsheqar kukanta da jan majina na fidda sauti kadan kadan,tsaiwa yayi yana dubanta duk da baya iya ganin fuskarta,duk sanda wata mace mai shekarun hajar ke kuka sai ya dinga jin kamar itace take kuka awancan lokacin da har yau ya kasa bacewa daga qwaqwalwarsa,lokacin daya sakawa suna da baqin lokaci,shi yasa a yanzun kukan nata ke sokarsa sosai,takawa ya soma yi zuwa wajen da take sai kuma yaji ana knocking,hakan yasanya ya sake juyawa zuwa wajen qofar ya bude,larai ce dauke da kayan kwanukan abinci,nuni yayi mata data aje,ta aje din kuwa a ladabce ta juya tabar wajen,ya sunkuya ya dauki kwanukan dai dai sanda ake qwala kiran sallar magariba,saman tebur din dake daura da ita ya aje
"Kukan ya isa haka,idan kuma a fasa makarantar ne kuma toh" da sauri ta tashi zaune tana hadiye kuken gami da qoqarin goge kyawawan idanunta da suka dan rine saboda kuka,ganin haka ya sanyashi wucewa ciki ya barta nan.
Sanda ya fito zai wuce masallaci tana zaune a wajen,jiranshi take ya fito ta shiga ta wanke bakinta,don idan daya yana cikin dakin dayan bai shiga har sai ya fito,har gwarashi wani lokaci zuwa lokaci yakan shiga idan akwai uzurin da bazai iya zaman jira ba,kaman zai wuce office yayi mantuwa zai dauki wani abu da makamantansu,dukkansu suna jin nunansu kaman baqi,saboda ba wanda ya taba rayuwa da wani jinsi daba nashi ba amuhalli guda sai wannan lokaci.
A bakin gate suka hadu da mus'ab da haidar,tun fadan daya yiwa mus'ab din bai sake kamashi da laifin rashin zuwa salla isha'in ko asuba ba,tare suka jera abinsu gwanin sha'awa,akwai qauna da fahimtar juna mai tarin yawa tsakaninsu,duba da wahalar da suka sha a baya wadda ita ta sake haifar da danqon qaunar junansu,haidar ke bare dabino yana ci khalipha ya kalleshi,yasan ma'anar kallon,da sauri yace
"Sorry yaya,kasan yau azumi mukayi ni da anty,ban samu na tsaya nayi bude baki ba kar jam'i ya wuceni,kuma ba'ason asha ruwa baka kai komai bakinka ba" bai sake cewa da shi komai ba,saidai yana mamakin yadda duk 'yan gidan keji da ayshan,yasan lallai ita rinjayi haidar ya soma azumin,don kwata kwata basa shiri da azumi.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Tun daga cikin dakinta take jiyo muryar hamid yana qwala mata kira,sosai kiran nashi ya bata tsoro har tana tuntube garin sakkowa saboda qara dage murya da yake wajwn kiran nata,a kitchen ta sameshi a tsaye,yayin da me aikinsu itama take tsaye gefe guda kantaba qasa kamar kazar da aka jiqa a ruwa,tana shiga ya dago mata kwalin lipton dinsu yana dubanta,sam bata fahimci me yake nufi ba sai da yayi magana
"Ya akayi ganyen shayin nan ya qare tun yau?"
"Kaman yaya?" Ta tambayeshi cikin takaici tana yamutsa fuska
"Tunda baki gane ba bari nayi miki bayani dalla dalla,sanda na kawo lipton din nan na qirgashi a gabanki na kwana sittin ne,ya akayi ya qare kwana ashirin kacal" hannayenta ta saka ta riqe qugunta duka biyun tana kallon hamid,itakam yanzu abun nashi bayan haushi ma tsantsar mamaki yake bata,koda wasa wani yace zaiyi abinda yake din yanzu sai anji kansu
"Ganyen shayin banza ganyan shayin wofi da zaka dinga yimin wannan kiran mafarautan saboda shi,kai yanzu hamid bakaji kunya ba saboda ganyan shayi kake daga jijiyar wuya haka,ohkey toni ban gaji tsiya ba,bazan bi wani lissafin ganyan shayi ba wallahi"
"Eh saboda ai bakisan ciwon kudi ba bakisan ciwon nema ba,yadda nayi almubazzaranci a waje haka ma yanzu kikeson naci gaba?,toba kudin banza gareni ba,lipton kuma saidai kici gaba da siya da kanki har kwana sittin ya cika" ya qarashe fada yana wurga kwalin a shara ya juya fuu ya fita daga kitchen din da alama ma ficewa xaiyi daga gidan donya shirya fes abinshi cikin suit kai baka ce shike magana kan lipton ba,binsa tayi da sauri tana tsaidashi,bai tsaya din ba har sai daya shiga motarsa yana shirin tada ta
"Man shafawa ta ne ya qare....inason wani irin na cikin kayana shine ya karbeni" dariya ya saki yana kallonta kamar yaga mahaukaciya
"Da Allah matsamin kina batamin lokaci kar baqina su wuce kija min asara,don na fuskanci ke bakisan darajar kudi ba"
"Wai hamid lafiyarka kuwa anya na asiri akayi maka ba?" Ta fada cikin harxuqa da mamaki,dariya ya sakeyi sannan ya ziro qafarsa daya waje kaman wanda ya fasa tafiya ya kalli cikin idanunta sosai
"Asma'u,kudi kika fiso a rayuwarki su na saka na shigo dake gidana,kin zaci ni wawa ne wamda baisan ciwon kudi ba saboda.ina da su ko?,toko dana tara bana almubazzaranci bane,kuma kaina na tarawa ba wani ko wata ba,idan zaki koyi rayuwar akwai da babu ki koya,shine kawai zaisa mu samu zaman lafiya ni dake matuqar ko zakici gaba da tambayata wani abu daya shafi in kashe kudina baki gayyaci zaman lafiya a gidan nan ba" yana kaiwa nan yaja murfin motarsa ya rufe ya kunnata ya dannawa mai gadi horn yaja motarshi ya fice.
Kuka asma'u ta saki ta juya zuwa cikin gidan a guje tana addu'ar Allah ya tasheta daga wannan mummunan mafarki da take,idan kuwa har ya tabbata mafarkin take ita da hamid ko hanya sunbar hadawa,sai data tabbatar cewa ba mafarkin bane ta soma tunanin sihiri 'yan adawa suka mata suka juyar mata da hankalin hamid dinta,banda haka mutum mai kudi kamar hamid ace yana maqo irin haka ba shakka da wata a qasa,hakan ya sanya ta dauki wayarta ta lalubi mommy don kai mata qorafi kamar yadda ta saba,don ko misqala zarratin asma'un bata da juriyar riqe damuwa ko solving matsalolin da duk zasu taso mata da kanta.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
35
Kusan tunda suka taho ita da shi fuskarta ke a cunkushe,ba don komai ba sai don batasan abinda zata je ta tarar ba a gidan,sam bata wani sha'awar zuwa gidansu hamid din,duk da cewa tunda sukai aure bata taba zuwa ba sai yau daya matsanta mata sai taje,saboda zaiyi tafiya ne shima,gaba daya haushin duk wata tafiya tashi take,a yanzu baya cikakken sati daya a gida,bashi wancan gari bashi wannan,bata isa tayi qorafi ba yanzu zai hauta da gorin yana yawon neman abinda ta aureshi ne saboda shi.
A harabar gidan ya tsaida motar sannan ya kasheta,fitowa yayi hakan ya sanya itama dole ta fito tabi bayanshi tana hade fuska har suka isa falon gidan.
Qannenshi ne zaune gaban t.v suna kallo,maza biyu mata biyu sune wadanda suka rage ba'a aurar ba,mahaifiyarsu na tsakiyarsu,kowanne yaci uban asma'u a girman kai da tabara,hakan ya sanya yayansun kawai suka yiwa sannu da zuwa kowa yaci gaba da sabgarsa,babu abinda uwar tace musu don ko ita bata nuna tasan tare suke da ita ba.