Sashe 1
Daurin Boye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
[ 🧣🧣 *DAURIN BOYE* 🧣🧣
UPLOADED ON
WWW.HAUSANOVELS001.COM.NG
*NA*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
HASKE WRITERS ASSO
(home of expert and perfect writers)✍
*_Dandano daga littafin DAURIN BOYE_*
DOWNLOAD MORE 👇 👇 👇
WWW.HAUSANOVELS001.CO.NG
0⃣1⃣
Sake gyara tsaiwarshi yayi jikin machine din nasa samfurin lifan kirar MOTO B,agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa ya kalla yana sake qiyasta mintocin daya kashe tsaye a qofar gidan,tabbas banda wani babban dalili babu abinda zaya sanyashi zaman jira har kamar haka,babu abinda ya tsana a rayuwarshi kaman jira,mutum ne shi mai kiyaye qa'ida wanda bai yarda da samfurin wannan maganar da hausawa ke bawa lokaci ba na african time.
Sauke hannun nashi yayi ya maida dubansa ga madaidaicin get din dake maqale da katangar gaban gidan wanda ya kasance shine kofar da zai sadaka da ainihin cikin gidan,kaman jiran hakan kuwa ake qofar ta soma yunkurin budewa,cikin sakannin kadan matashiyar dake yunqurin bude qofar ta bayyana.
A hankali take takowa zuwa inda yake,sanye cikin dinkin atamfa riga fitted da skert wanda ya zaunawa jikinta das,ta lullube jikinta da mayafi wanda baikai matsayin medium ba,a hankali yayi kokarin mamaye fuskarshi da murmushi duk da yadda fuskarta take kadaran kadaham hakan bai dameshi ba duk da yana ankare,ba fara'a sannan ba kuma a daure take can ba,kallo take kare masa tun daga nesa kaman yadda ta saba masa duk sa'ilin da ya ziyarceta,shirt ce jikinsa ruwan makuba da bakin wando jeans mai matsakaicin kudi,kafafunsa saye da takalmi budadde dinkin hannu na kasuwar kofar wambai,fes yake hakanan kayan sun masa kyau babu laifi,sumarshi kanshi zuwa sajensa a gyare a taje wanda hakan ya sake bayyana sirrin kyan da Allah ya bashi,ba shakka banda wani abu guda tak muhammad ya cika mijin aure wanda za'a iya nuna shi a ko ina,saidai wannan abun daya rasa din ya sanya ta cireshi daga tsarin mutumin daya cancanci aurenta.
"Barka da fitowa gimbiya zulaiha" ya fada cikin sassanyar muryarsa wadda na daya daga cikin abinda ke burge zulaihan tare da shi,duk da bata jin zata iya bashi damar kasancewa cikin rayuwarta,yana ci gaba da nazarin yanayin fuskarta a fakaice sanda ta amsa masa
"Barkan ka" ta fada cikin wani salon shan qamshi da basarwa
"Har na fidda rai ai,na tsammaci yau bazan samu ganinki ba"
"Kusan da hakan ce ta kusa faruwa,saboda zamu fita ne da maama,sannan ma kuma bansan zaka zo din ba,yanzun ma zuwa nayi na gaya maka.....don Allah ya kamata ace duk sanda zaka zo ka fara sanarmin tukunna kafin kazo din"ta fada kanta tsaye tana yamutsa fuska murmushi ya saki gami da dan duqar da kanshi qasa yana wasa da duwatsun dake shimfide a qofar gidan,baice komai ba sai murmushin da yaci gaba da fitarwa yana tattaunawa shi da zuciyarsa,tabbas yasan wannan rana na nan tafe,fiye da haka kuma na nan zuwa nan gaba kadan,wannan ba baqon lamari bane a gareshi,zulaiha ba itace mace ta farko da makamancin hakan ta faru tsakaninsu ba,saidai bazai yanke mata hanzari ba,zai jirata har zuwa ranar da zai zata furta kota yanke alaqar dake tsakaninsu da bakinta,sai bayan daya kammala wannan tunanin sannan ya dago ya dubeta
"Shikenan....babu damuwa...kiyi hakuri" ba tare data tanka ba ta juya tana niyyar komawa cikin gidan nasu
"Ki gaida maaman idan kin shiga"
"Zata ji" ta fada gami da jan qaramin tsaki can qasa ta shige gidan gami da rufe qofar gidan garam.
Kai ya girgiza bayan shigewarta cikin gidan yana sakin murmushi tare da cije lebansa na qasa,cikin qwarewa ya haye saman babur din bayan ya tadashi ya figeshi cikin gudu ya fice daga layin,zuciyarsa cike fal da tunani da mamaki,mamakin da har yau yaqi barinsa,tsahon shekaru kenan wannan abu na daure masa kai,da gaske haka rayuwa ta koma?,ya gode Allah da baiyi gaggawar yiwa hukunci wa rayuwarsa ba.
Titi ya hau ba tare da yayi wata doguwar tafiya ba ya soma sauka daga kan kwaltar zuwa gangaren titin,daf da wasu jeran baqaqen motoci da farare a qalla guda biyar ya soma qoqarin tsaiwa,wanda tun kafin ya kai ga tsaiwar wasu matasa kimanin su bakwai sanye da coat baqi da fari suka doso shi,kowanne fuskarshi manne da baqin gilashi wanda hakan ya sanya baka iya ganin qwayar idanunsa,ya kuma qara musu kwarjini qwarai,daya daga cikinsu shi ya riqe babur din sanda ya sauka,yayin da dayan ya matso kusa da shi yana bude masa qofar daya daga cikin motocin wadda duka ta fisu kyau da girma,sai da yaga ya shiga sannan ya rufe masa qofar,sauran suka zagaya suka shige ragowar motocin nasu,yayin da daya daga cikinsu shi kuma ya haye babur din ya bisu a baya.
"Ya dai,akwai wani sauyi ko ci gaba kuwa yau?" Wani kyakkyawan matashi wanda aqalla zaiyi shekara talatin da hudu dake zaune daga corner motar riqe da magazine ya fada yana dubanshi,fuskarshi na nuna alamun dariya yakeson yi,takalman qafarsa ya soma yunkurin cirewa gami da agogon hannunshi ba tare daya dubeshi ko ya amsa masa ba,ya dannan wani madanni dake gaban sit dinshi,wani qaramin akwati ne ya fito ya zuba agogon takalmin harda wayar dake hannunshi qirar VIVO bayan ya kasheta,ya maida akwakwun muhallinsa ya jingina da makarin kujerar sannan ya waiwaya ya dubeshi
"Me kake tunani mahmoud?,ita dinma kaman sauran,abun ma kamar yana sake lalacewa ne" ya qarashe maganar yana lumshe idanunsa tare da sauke numfashi
"Duk inda xaka je ka dawo dai shawarata ce kan hanya,na sha gaya maka ka sauqaqewa kanka walaha,ka laluba cikin familynka,akwai gomayyar 'yammatan dake sonka ka zabi daya cikinsu ka huta,kaga wannan babu wani fargaba tattare da kai,duka ana tare". Kansa yaci gaba da girgizawa ba tare daya bude ido ya kalli mahmoud ba,tsahon sakanni tamkar bazai amsa mishi ba sannan ya ware idanunsa yana duban sit din dake gabansa
"kana tunanin qaramin abu ne ya sanya na guje musu dukkaninsu na xabi inbiyo ta wannan hanyar?,su dinma kusan duka abu guda ne,babu wani banbanci,halayyar daya ce dai kaman yadda sunansu yake daya,abu guda dukkaninsu suke wa,manufarsu guda ce......" Maganar tashi ta katse sakamakon shigowar kira wayar tasa,ya maida qwayar idanunsa ahankali kan wayoyin dake zube a gefansa,kusan lokaci guda idanunsu shida mahmoud suka sauka kan wayar RAMLA sunan dake yawo kenan bisa screen din,murmushi mahmoud ya saki ganin ya kau da kanshi tamkar ba cikin wayarshi kiran ya shigo ba
"Yallabai ka daga mana?"
"Qyaleta kawai" ya bashi amsa kai tsaye gami da danna wani madanni,wani dan qaramin abu mai kama da fridge ya bayyana,cikinsa nau'ikan abubuwan sha ne masu sanyi da duka duka basu wuce gwangwanaye da kwalba goma sha biyu ba,daya a ciki ya dauka hadi da cup ya maida abun muhallinsa ya koma ya jingina da kujera ya tsiyaya yana kaiwa bakinsa ba tare da yabi ta kan qorafin daga waya da mahmoud ke masa ba,a maimakon hakan ma sai ya maye gurbin qorafin nasa da tambaya
"Jirgin qarfe nawa zamu bi ne?" Tunda ya masa hakan yasan bai bukatar xancan,saboda haka shima ya tayashi
"Yanzun airphort din muka nufa ai,tunda duka duka awa guda da 'yan mintuna ya rage lokacin tashin jirgin ya cika"
"Ok,kafin nan mu biya na sauya kayan jikina"
"Ba matsala" ya fadi yana gayawa driver inda zasu fara zuwa kafin su isa airphort din.
🧣🧣🧣🧣
A nutse ta miqe daga saman abun sallar tana sakin 'yar qaramar hamma tare da furta "a'uzu billahi minash shaidanir rajim" gami da ninke daddumar ta mata ma'ajiya a muhallinta,zare hijabin jikinta tayi tanayi tana duba agogon dake maqale a bango saboda gudun makara,qarfe shida na safiya ya nuna mata,hakan ya mata dadi ta tabbatar kafin lokacin tafiyarsu makaranta ta kammala dukkan abinda zata yi din,gyara dankwalin kanta tayi wanda ke niyyar zamewa saboda santsinsa da kuma santsin sumar kanta,sannan ta zura slippers ta bude qofar dakin nata ta fita a hankali.
Makekan falon nasu shiru yake tamkar babu halittar kowa cikin gidan,bugu da qari mamaye yake da dan sauran duhun asuba da bai gama yayewa ba,babu motsin kowa,don hatta da masu aikin gidan basu tashi ba,kunna qwayayen falon tayi take haske ya game ko ina ya kuma bayyana asirin kyan da falon ke da shi,sannan taci gaba da takawa a hankali ta doshi wani corridor wanda a nan kitchen dinsu yake.
Kitchen ne na alfarma wanda ya mallaki dukkan wani nau'in kayan amfani da kitchen ka iya buqata,kai tsaye ta nufi jikin wani dan qaramin Allo wanda ke dauke da timetable na abincin da gimbiyar gidan ke buqata kowacce rana,alhamis ce saboda haka ta sauke idanunta kan THURSDAY dake rubuce baro baro,ta kuma karanta abincin dake qarqashin ranar,kanta ta jinjina saboda yau aikin nata kaman mai yawa ne,gashi a jiya bata samu ta duba me zata girka ba yau sakamakon bacci fa yayi nasarar saceta tana tsaka da karatun test da zasuyi a safiyar yau,cikin hanzari ta bude freezer ta fiddo dukkan abinda zata buqata,sannan ta wuce store dake cikin kitchen din ta fiddo kayan amfani,sannan ta soma aikinta cikin hanzari da qwarewa.
A qalla ta shafe kusan mintina talatin sannan ta jiyo motsi alamun ana niyyar shigowa kitchen din,fuskarta qunshe da murmushi wanda ya sanya dimple dinta dake dukka kumatunta lonawa,tunkan ta qaraso tasan wacece,ita kadai ke tashi ta kama mata aiki,ita daya ce matar da hakanan Allah ya hada jininsu take qaunarta,ita daya ce take ganin qauna daga idanunta,irin qaunar data rasa,irin qaunar da take buri da fata ta ganta daga wajen wadda tayi silar kawota duniya saidai har yau abu yaci tura,a wajenta ne kawai take ganin kulawa qauna da kuma sassauci.
Ita dince kuwa,daya daga cikin masu aikin gidan ce inna laraba,fuskarta fadade da fara'a tace
"Yanzu inna laraba yau dinma ba zaki kwanta ki huta ba?,ina cewa jiya da qyar kika samu ciwon qafar nan ya barki?" Itama fuskarta qunshe da fara'ar tace
"Banda abinki shatu ai kema kinsan ban saba da wannan baccin bayan sallar asubar ba,kuma na tabbatar kina nan ke daya kina fama da kacaniya" ta fada tana qarasowa kusa da ita,murmushi ta saki sannan cike da girmamawa ta gaida innar kaman yadda take kiranta tare da tambayarta ya qafar tata,amsa mata tayi itama cikin kulawa kafin ta matso da niyyar kama mata aikin,duk yadda taso hanata amma innan sam taqi,haka ta sakar mata suka ci gaba da aikin tare suna hira.
UPLOADED ON
WWW.HAUSANOVELS001.COM.NG
*NA*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
HASKE WRITERS ASSO
(home of expert and perfect writers)✍
*_Dandano daga littafin DAURIN BOYE_*
DOWNLOAD MORE 👇 👇 👇
WWW.HAUSANOVELS001.CO.NG
0⃣1⃣
Sake gyara tsaiwarshi yayi jikin machine din nasa samfurin lifan kirar MOTO B,agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa ya kalla yana sake qiyasta mintocin daya kashe tsaye a qofar gidan,tabbas banda wani babban dalili babu abinda zaya sanyashi zaman jira har kamar haka,babu abinda ya tsana a rayuwarshi kaman jira,mutum ne shi mai kiyaye qa'ida wanda bai yarda da samfurin wannan maganar da hausawa ke bawa lokaci ba na african time.
Sauke hannun nashi yayi ya maida dubansa ga madaidaicin get din dake maqale da katangar gaban gidan wanda ya kasance shine kofar da zai sadaka da ainihin cikin gidan,kaman jiran hakan kuwa ake qofar ta soma yunkurin budewa,cikin sakannin kadan matashiyar dake yunqurin bude qofar ta bayyana.
A hankali take takowa zuwa inda yake,sanye cikin dinkin atamfa riga fitted da skert wanda ya zaunawa jikinta das,ta lullube jikinta da mayafi wanda baikai matsayin medium ba,a hankali yayi kokarin mamaye fuskarshi da murmushi duk da yadda fuskarta take kadaran kadaham hakan bai dameshi ba duk da yana ankare,ba fara'a sannan ba kuma a daure take can ba,kallo take kare masa tun daga nesa kaman yadda ta saba masa duk sa'ilin da ya ziyarceta,shirt ce jikinsa ruwan makuba da bakin wando jeans mai matsakaicin kudi,kafafunsa saye da takalmi budadde dinkin hannu na kasuwar kofar wambai,fes yake hakanan kayan sun masa kyau babu laifi,sumarshi kanshi zuwa sajensa a gyare a taje wanda hakan ya sake bayyana sirrin kyan da Allah ya bashi,ba shakka banda wani abu guda tak muhammad ya cika mijin aure wanda za'a iya nuna shi a ko ina,saidai wannan abun daya rasa din ya sanya ta cireshi daga tsarin mutumin daya cancanci aurenta.
"Barka da fitowa gimbiya zulaiha" ya fada cikin sassanyar muryarsa wadda na daya daga cikin abinda ke burge zulaihan tare da shi,duk da bata jin zata iya bashi damar kasancewa cikin rayuwarta,yana ci gaba da nazarin yanayin fuskarta a fakaice sanda ta amsa masa
"Barkan ka" ta fada cikin wani salon shan qamshi da basarwa
"Har na fidda rai ai,na tsammaci yau bazan samu ganinki ba"
"Kusan da hakan ce ta kusa faruwa,saboda zamu fita ne da maama,sannan ma kuma bansan zaka zo din ba,yanzun ma zuwa nayi na gaya maka.....don Allah ya kamata ace duk sanda zaka zo ka fara sanarmin tukunna kafin kazo din"ta fada kanta tsaye tana yamutsa fuska murmushi ya saki gami da dan duqar da kanshi qasa yana wasa da duwatsun dake shimfide a qofar gidan,baice komai ba sai murmushin da yaci gaba da fitarwa yana tattaunawa shi da zuciyarsa,tabbas yasan wannan rana na nan tafe,fiye da haka kuma na nan zuwa nan gaba kadan,wannan ba baqon lamari bane a gareshi,zulaiha ba itace mace ta farko da makamancin hakan ta faru tsakaninsu ba,saidai bazai yanke mata hanzari ba,zai jirata har zuwa ranar da zai zata furta kota yanke alaqar dake tsakaninsu da bakinta,sai bayan daya kammala wannan tunanin sannan ya dago ya dubeta
"Shikenan....babu damuwa...kiyi hakuri" ba tare data tanka ba ta juya tana niyyar komawa cikin gidan nasu
"Ki gaida maaman idan kin shiga"
"Zata ji" ta fada gami da jan qaramin tsaki can qasa ta shige gidan gami da rufe qofar gidan garam.
Kai ya girgiza bayan shigewarta cikin gidan yana sakin murmushi tare da cije lebansa na qasa,cikin qwarewa ya haye saman babur din bayan ya tadashi ya figeshi cikin gudu ya fice daga layin,zuciyarsa cike fal da tunani da mamaki,mamakin da har yau yaqi barinsa,tsahon shekaru kenan wannan abu na daure masa kai,da gaske haka rayuwa ta koma?,ya gode Allah da baiyi gaggawar yiwa hukunci wa rayuwarsa ba.
Titi ya hau ba tare da yayi wata doguwar tafiya ba ya soma sauka daga kan kwaltar zuwa gangaren titin,daf da wasu jeran baqaqen motoci da farare a qalla guda biyar ya soma qoqarin tsaiwa,wanda tun kafin ya kai ga tsaiwar wasu matasa kimanin su bakwai sanye da coat baqi da fari suka doso shi,kowanne fuskarshi manne da baqin gilashi wanda hakan ya sanya baka iya ganin qwayar idanunsa,ya kuma qara musu kwarjini qwarai,daya daga cikinsu shi ya riqe babur din sanda ya sauka,yayin da dayan ya matso kusa da shi yana bude masa qofar daya daga cikin motocin wadda duka ta fisu kyau da girma,sai da yaga ya shiga sannan ya rufe masa qofar,sauran suka zagaya suka shige ragowar motocin nasu,yayin da daya daga cikinsu shi kuma ya haye babur din ya bisu a baya.
"Ya dai,akwai wani sauyi ko ci gaba kuwa yau?" Wani kyakkyawan matashi wanda aqalla zaiyi shekara talatin da hudu dake zaune daga corner motar riqe da magazine ya fada yana dubanshi,fuskarshi na nuna alamun dariya yakeson yi,takalman qafarsa ya soma yunkurin cirewa gami da agogon hannunshi ba tare daya dubeshi ko ya amsa masa ba,ya dannan wani madanni dake gaban sit dinshi,wani qaramin akwati ne ya fito ya zuba agogon takalmin harda wayar dake hannunshi qirar VIVO bayan ya kasheta,ya maida akwakwun muhallinsa ya jingina da makarin kujerar sannan ya waiwaya ya dubeshi
"Me kake tunani mahmoud?,ita dinma kaman sauran,abun ma kamar yana sake lalacewa ne" ya qarashe maganar yana lumshe idanunsa tare da sauke numfashi
"Duk inda xaka je ka dawo dai shawarata ce kan hanya,na sha gaya maka ka sauqaqewa kanka walaha,ka laluba cikin familynka,akwai gomayyar 'yammatan dake sonka ka zabi daya cikinsu ka huta,kaga wannan babu wani fargaba tattare da kai,duka ana tare". Kansa yaci gaba da girgizawa ba tare daya bude ido ya kalli mahmoud ba,tsahon sakanni tamkar bazai amsa mishi ba sannan ya ware idanunsa yana duban sit din dake gabansa
"kana tunanin qaramin abu ne ya sanya na guje musu dukkaninsu na xabi inbiyo ta wannan hanyar?,su dinma kusan duka abu guda ne,babu wani banbanci,halayyar daya ce dai kaman yadda sunansu yake daya,abu guda dukkaninsu suke wa,manufarsu guda ce......" Maganar tashi ta katse sakamakon shigowar kira wayar tasa,ya maida qwayar idanunsa ahankali kan wayoyin dake zube a gefansa,kusan lokaci guda idanunsu shida mahmoud suka sauka kan wayar RAMLA sunan dake yawo kenan bisa screen din,murmushi mahmoud ya saki ganin ya kau da kanshi tamkar ba cikin wayarshi kiran ya shigo ba
"Yallabai ka daga mana?"
"Qyaleta kawai" ya bashi amsa kai tsaye gami da danna wani madanni,wani dan qaramin abu mai kama da fridge ya bayyana,cikinsa nau'ikan abubuwan sha ne masu sanyi da duka duka basu wuce gwangwanaye da kwalba goma sha biyu ba,daya a ciki ya dauka hadi da cup ya maida abun muhallinsa ya koma ya jingina da kujera ya tsiyaya yana kaiwa bakinsa ba tare da yabi ta kan qorafin daga waya da mahmoud ke masa ba,a maimakon hakan ma sai ya maye gurbin qorafin nasa da tambaya
"Jirgin qarfe nawa zamu bi ne?" Tunda ya masa hakan yasan bai bukatar xancan,saboda haka shima ya tayashi
"Yanzun airphort din muka nufa ai,tunda duka duka awa guda da 'yan mintuna ya rage lokacin tashin jirgin ya cika"
"Ok,kafin nan mu biya na sauya kayan jikina"
"Ba matsala" ya fadi yana gayawa driver inda zasu fara zuwa kafin su isa airphort din.
🧣🧣🧣🧣
A nutse ta miqe daga saman abun sallar tana sakin 'yar qaramar hamma tare da furta "a'uzu billahi minash shaidanir rajim" gami da ninke daddumar ta mata ma'ajiya a muhallinta,zare hijabin jikinta tayi tanayi tana duba agogon dake maqale a bango saboda gudun makara,qarfe shida na safiya ya nuna mata,hakan ya mata dadi ta tabbatar kafin lokacin tafiyarsu makaranta ta kammala dukkan abinda zata yi din,gyara dankwalin kanta tayi wanda ke niyyar zamewa saboda santsinsa da kuma santsin sumar kanta,sannan ta zura slippers ta bude qofar dakin nata ta fita a hankali.
Makekan falon nasu shiru yake tamkar babu halittar kowa cikin gidan,bugu da qari mamaye yake da dan sauran duhun asuba da bai gama yayewa ba,babu motsin kowa,don hatta da masu aikin gidan basu tashi ba,kunna qwayayen falon tayi take haske ya game ko ina ya kuma bayyana asirin kyan da falon ke da shi,sannan taci gaba da takawa a hankali ta doshi wani corridor wanda a nan kitchen dinsu yake.
Kitchen ne na alfarma wanda ya mallaki dukkan wani nau'in kayan amfani da kitchen ka iya buqata,kai tsaye ta nufi jikin wani dan qaramin Allo wanda ke dauke da timetable na abincin da gimbiyar gidan ke buqata kowacce rana,alhamis ce saboda haka ta sauke idanunta kan THURSDAY dake rubuce baro baro,ta kuma karanta abincin dake qarqashin ranar,kanta ta jinjina saboda yau aikin nata kaman mai yawa ne,gashi a jiya bata samu ta duba me zata girka ba yau sakamakon bacci fa yayi nasarar saceta tana tsaka da karatun test da zasuyi a safiyar yau,cikin hanzari ta bude freezer ta fiddo dukkan abinda zata buqata,sannan ta wuce store dake cikin kitchen din ta fiddo kayan amfani,sannan ta soma aikinta cikin hanzari da qwarewa.
A qalla ta shafe kusan mintina talatin sannan ta jiyo motsi alamun ana niyyar shigowa kitchen din,fuskarta qunshe da murmushi wanda ya sanya dimple dinta dake dukka kumatunta lonawa,tunkan ta qaraso tasan wacece,ita kadai ke tashi ta kama mata aiki,ita daya ce matar da hakanan Allah ya hada jininsu take qaunarta,ita daya ce take ganin qauna daga idanunta,irin qaunar data rasa,irin qaunar da take buri da fata ta ganta daga wajen wadda tayi silar kawota duniya saidai har yau abu yaci tura,a wajenta ne kawai take ganin kulawa qauna da kuma sassauci.
Ita dince kuwa,daya daga cikin masu aikin gidan ce inna laraba,fuskarta fadade da fara'a tace
"Yanzu inna laraba yau dinma ba zaki kwanta ki huta ba?,ina cewa jiya da qyar kika samu ciwon qafar nan ya barki?" Itama fuskarta qunshe da fara'ar tace
"Banda abinki shatu ai kema kinsan ban saba da wannan baccin bayan sallar asubar ba,kuma na tabbatar kina nan ke daya kina fama da kacaniya" ta fada tana qarasowa kusa da ita,murmushi ta saki sannan cike da girmamawa ta gaida innar kaman yadda take kiranta tare da tambayarta ya qafar tata,amsa mata tayi itama cikin kulawa kafin ta matso da niyyar kama mata aikin,duk yadda taso hanata amma innan sam taqi,haka ta sakar mata suka ci gaba da aikin tare suna hira.