← Book details Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 86 OF 174

Sashe 86

Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Tayi dariya ta ce "Ai bai fito É—in ba, kuma gaskiya kar ki yi masa sharri dan kin tsane shi, you are still a baby, ina wani nono a nan banda sharrinki ruma? Ko kwatan nawa ba su kai ba fa, ko ganinsu ba ayi"

Rumaisa ta ce "Wallahi sun fara fitowa, mama ta ce duk wanda ya taɓa ciki zai fito mini, kuma korata za su yi daga gidan su, yanzu da ya sa an koreni fa, ni fa bana son ma su fito, idan ba haka ba mama zata hanani yawo ba riga, yanzu ma hanani take yi"

Aisha ta yi dariya ta ce. "gaskiya ki daina zaginsa tun da dai ba a korekin ba, kin yi masa sharri, ina wani abun taɓawa a nan" tayi maganar tana sake tuntsirewa ruma da dariya.

Ruma ta ce "Wallahi ya taɓa, kuma idan Allah ya sa na bar nan idona idonsa zai gane bashi da wayo, ana i gobe zan zo katsina, yayi mini wanka da kwata a tsakiyar layi, wai har da cewa na yi masa sharri da nace ya taɓani, wai zuwa yayi ya duba ya ga ko akwai wani abu a ƙirjina ki ji ɗan iska fa"

Aisha ta dafe ƙirji ta ce "Wayyo zuciyata, haba baby rumaisa sunan mijina adam, kar ki sa kishina ya tashi. Amma ni nawa Adam ɗin shima yana da zafin zuciya, baya son raini ga miskilanci, amma idan ki ka fahimce shi, mutumin kirki ne, mai son kulawaga iya soyayya, sai dai...." ta ɗan yi shiru sai kuma ta ce "Ruma zaki auri Adam?"

Ruma ta waro ido ta ce "wane Adam É—in? Ni da ban yi tsawo na girma ba za ayi mini aure?".

"Adam da kuke faÉ—a, ki yafe masa ko dan albarkacin yana da sunan mijina"

Ruma ta turɓuna fuska ta ce "Ai wallahi ko yayanki ne ba zan yafe masa ba, da in auri Wannan gara na mutu ba aure, kuma ni miji kyakkyawa nake so, kuma mai kuɗi"

"In dai kuÉ—i ne akwai su ruma, kuma ai kyakykyawa ne"

Rumaisa ta dubeta ta ce "Ba fa mijinki ba, wannan da muke faÉ—a nake gaya miki, mai suffar mugwaye da wata banzar motarsa in sha Allah sai an sace motar ma".

"In an saceta ma zai sai wata, kuma ya sai miki kema, banda faÉ—an rashin gaskiya ke fa ki ka fara zaginsa a social media, amma tsabar rigimarki kina ta zaginsa, kin ci sa'a da bai É—aureki ba, ko ya sa a zaneki ba".

"Oho ni dai ban yafe ba"

Tayi ajiyar zuciya ta ce "I love your confidence my dear, you can face the challenges. Jikina na bani wani abu game da ke, zaki iya ruma" tayi maganar tana jan kunatun rumaisa ta ce "Kamar haka mijina yake wasa da kumatuna".

"Anty Aisha, yake taɓaki? Ba a wasa da maza fa" ba ta bawa ruma amsa ba, sai dariya da take yi mata, tana fatan Allah ya tabbatar da abun da take ji game da ruma.

Ranar da zata rasu bayan ta haihu, ta riƙe hannun rumaisa ta ce "Baby rumaisa, idan Allah ya sa kin kuɓuta, ni 'yar gidan turakin kano ce, amma kar a nemi mahaifina kai tsaye a nemi sirikata, idan ba zaki iya riƙe jaririn nan ba, ki danƙa mata shi, Hajiya Binta giwar Galadima, uwar gidan galadiman kano, sirikata ce ita zaki danƙawa jaririn nan, ɗan ta shine mijina" a lokacin gaba ɗaya ruma ta manta da wani adam balle ta kawo shi a lissafi da aisha ta yi zancen galadima.

Ko da ruma ta zo nan a tunaninta sai ta tambayi kanta 'Kenan da gaske shi ne mijinta?' a zahiri kuwa ta fashe da kuka ta ce "Wallahi ba shi ne babansa ba, ni ba shi ta ce mini ba" a bata iya tafiya ta fara ƙoƙarin dirowa daga kan gadon tana miƙa hannu ta ce "Ni ku bani jaririna, ba ɗansa bane ba, ni ba ta ce mini in bawa kowa ba, ku bani ɗana" mama tayi shiru ta zubawa sarautar Allah ido.

Bashir ya miƙawa Adam hannu ya ce "Ka ga Adam, kawo yaron nan, gaba ɗaya a ruɗe take, kamar ba ta hayyacinta ne ma, kawo a bata shi kan muga yadda hali zai yi".

"Bashir ka haukace ne? Taya ka ke cewa in baka É—ana ka bawa wani?".

"Wallahi ba É—ansa bane ba, ku bani É—ana" ruma tayi maganar tana kuka.

Bashir ya karɓe yaron, ya miƙawa rumaisa, ta rungumeshi tana fashewa da kuka ta ce "Cewa ta yi idan ba zan iya riƙe shi ba, in bawa giwar Galadima ni ban santa ba ma, ban san a in da take ba, amma ni dai zan iya riƙe yarona, ai cewa ta yi ta bar mini shi har abada nice mamansa". Gaba daya ɗakin aka zubawa sarautar Allah ido.

Ammi da tun É—azu take zaune kamar an shukata, ta kasa magana sai tasbihi kawai da take yi, ta tashi sannu a hankali, ta je kusa da rumaisa suka matsa mata ta zauna.
Ta dafa kafaÉ—ar rumaisa idonta fal hawaye ta ce "'ya ta, nice giwar Galadiman kano mai rasuwa, Adam kuma É—ana ne, shine mahaifin wannan jaririn, kuma mijin Aisha".

Ruma ta girgiza kai ta ce "A'a wallahi ba shi bane ba, ni fa ba zan bawa kowa ba, ni ta ce ta barwa shi".

Ammi ta ce "To shikenan, na ji babu mai rabaki da yaronki, Ubangiji Allah ya baku lafiya gaba É—aya, yanzu ki bayar da shi a mayar da shi sashen kula da yara".

Rumaisa ta girgiza kai ta ce "Ba zan bayar da shi ba, haka kurum ya bishi ya sace shi, da in bashi É—ana gara na koma wurin 'yan garkuwa da mutanen".

Huzaifa ya ce "To fa ana wata ga wata".

Ammi ta ce "To shikenan, rungume shi da kyau, kin ga bacci zai yi kema ki kwanta ki huta" a'a ba zan rufe idona in je ya gudu da shi ba.

Miƙewa Adam yayi jikinsa yana rawa, amma Ammi tayi masa wani irin kallo, tayi masa nuni da ya fita, yayi gaba ya tsaya ya waiwaya yana kallon rumaisa, da jaririnsa da yanzu ya shiga tunanin ina uwarsa? A wane hali kuma take ciki?".

Suna tafe a hanya babu wanda ya iya cewa komai, sai Bashir da yake yi wa Adam nasiha "Adam dole sai mun bi yarinyar nan a hankali har yanzu a rikice take, kuma a cikin firgici ba ƙaramar azaba ta sha kan ta fito da yaron nan ba, kaga Yarinya ce ƙarama ikon Allah ne ya fito da su, dan ita ma ba gama sanin ciwon kanta tayi ba, a sannu zamu bita mu ji a ina ita Aishar take, sai mu zo mu yi shiri".

Daga Ammi har takawa, babu wanda ya ce wani abu, kowa da abun da yake saƙawa a zuciyarsa, adam bai taɓa tunanin abubuwa su cukurkuɗe masa haka ba.

Suna zuwa gida ammi ta wuce part É—inta, adam ma bai jira bashir ba, ya rufa mata baya.
A falo nusaiba ta tare ta tana tambayarta, "Ammi wai ina ki ka tafi haka, mun dawo daga islamiyya kawai muka tarar ba kya nan, kalli dare har ya fara yi fa" sai dai fuskar ammin ta nuna mata ba lafiya ba. Kan ta yi magana ta ga adam ya shigo ya bi bayan anmi, hakan ya sanya ta sha jinin jikinta.

A É—aki ya tarar da ammi, ta ajiye carbin hannunta da mayafinta, hawaye tuni ya wanke mata fuska.

"Ammi dan Allah ki tsaya ki saurareni, kar ki yi mini haka".

Ta kalli Adam ta ce "In saurareke ka gaya mini me adam, yanzu a duniya akwai abun da zaka iya ɓoye mini? Ta ina zamu kalli duniya mu fara bayanin abun da ya faru? Ta yaya duniya za ta yadda da cewar jaririn nan ɗanka ne? Da yaya zaka yi wa turaki bayanin abun da ya samu 'yar sa, shikenan mun zama masu son kai kenan, idan maganar nan ta yaɗu ina zan saka kaina, ina ta ƙoƙarin toshe waccan kafar wannan ta ɓullo, adam kana me garin yaya haka ta faru ka ɓoye mini, ɗan da ba a san da cikinsa ba kawai mu ce ga ɗa meye shaidarmu ba ƙarya muke yi ba, ina ita Aishan?"

Adam da ya gama rikicewa ya ce "Dan Allah ammi ki fahimce ni, zan yi miki bayani bani da laifi, ba domin na ɓoye miki na yi duk abun da na yi ba"

Ammi ta katse shi ta hanyar cewa "To domin ka faranta mini ne? A tunaninka zan yi murna da hakan ne?".
Chapter 86 · 0% Book details