← Book details Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 121 OF 174

Sashe 121

Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Gashi nan kuwa" yayi maganar cikin sigar wasa. Ya bawa iman sabir ya tashi ya bar falon, a rayuwar duniya samha ba ta kishi da aisha kamar yadda take yi da iman, saboda akwai alaƙa mai kyau a tsakanin takawa da iman, ga iman da kyau tamkar ita ta yi kanta.

Suka gama zamansu, daga bisani suka tashi za su tafi, Samha ta ajiye wata leda cike da kayan sawa da na wasa, wai sabir ta kawowa, ammi ta yi mata godiya sannan suka tafi.

***
Ba kowa a gidansu rumaisa, kowa ya fita da masu makaranta da sauransu, sai mama itakaɗai, kasancewar ta ji sauƙi, ya sanya ta ɗora abincin rana, dan ba ta son su dawo ba ta kammala abinci ba, yanzu ƙaramarsu babbarsu za ta zo ta fara kwanciya da tura baki ita yunwa.
Sai dai babu tsammani ta ga kiran ammi a waya.

Ta É—aga wayar suka gaisa, ammi ta kuna yi wa mama ya jiki.
Sun ɗan taɓa hira sannan ammi ta ce "Yauwwa maman rumaisa wata magana nake son mu tattauna da ke, duk da kamata ya yi na zo ƙafa da ƙafa, ina da wasu baƙi ne da zan yi yau, kuma maganar yakamata mu yi ta"

Mama ta nutsu ta ce "To ina jin ki, Allah ya sa lafiya".

"Yauwwa, zuwa wannan lokaci tun da Allah ya riga ya haɗamu, mun riga mun zama ɗaya, tun bayan da na baro ku, nake ta tunani a kan maganar da ki ka yi mini a kan rumaisa, da kuma wasu dalilai na makomar jaririn nan, shine na yanke shawarar mai zai hana adam ya auri rumaisa, kin ga maganar wata gulma da ɓacin suna ya ƙare, kuma kin ga za ta samu cikakkiyar damar kula da sabir kamar yadda take buƙata, amma me ki ka ce?"

Jiki a sanyaye mama ta ce "Aure kuma rumaisan? Shekararta goma sha uku fa, kina ganin yadda ake fama da ita, ga kuma karatunta".

Ammi ta ce "Maman rumaisa ba zai gagara ba, mu ma duk da ƙuruciyar aka yi mana aure, kuma ba abun da zai samu karatunta, za ta cigaba idan aka yi auren nan ni da adam za a yi wa alfarma kuma ina tabattar miki in Allah ya yarda zai zama alkhairi, yanzu amsarki nake jira, zan kai maganar ga magabatansa, tun kan ace za a bashi wata matar, ban san wa za a bashi ba, ko dan makomar rayuwar marayan nan".

Mama ta yi ajiyar zuciya ta ce "Haka ne, amma gani nake rumaisa ba za ta iya raino ba, ita ma ba hankali ta cika ba"

Ammi ta yi murmushi ta ce "Babu damuwa, ai ba sakar mata rainon za a yi ba, ya zamana dai ta samu kusanci da shi sosai yadda take so".

"To, bari yayyenta su zo mu tattauna, abun da suka yanke shikenan"

Ammi ta ce "To, Allah ya sanya mu ji alkhairi, ina saurarenku dan da wuri nake son ayi komai a gama"

"To shikenan, duk yadda muka yi zaki ji ni" tun da suka yi sallama mama ta kashe wayar take zullumi. Ayi wa rumaisa aure ta je ta yi me a gidan auren? Yarinyar da ban da zunzurutun ƙuruciya da wauta ba abun da yake damunta.

A haka mama ta É—ora girkin nan, take aikin jikinta duk a sanyaye.

Rumaisa ce ta yi sallama, ta shigo da jakar makarantarta a ka, tana yamutsa fuska.

Mama ta kalleta ta amsa mata, rumaisa ta jefa jakarta ɗaƙi, ta cire hijjabinta ta kalli mama ta ce "Mama ki aika aje a yi wa mai ice warning ba ruwansa da ni, me na yi masa da idan na zo wucewa zai din ga cewa gata can, sau biyu yana yi mini, kar na yi abun da ba shikenan ba a zo ace na yi tom" tana gama maganar ta ɗau buta ya wuce banɗaki.

Bayan ta fito ta kalli mama a taɓare ta ce "Mama wai ba a gama abincin ba, ni fa yunwa nake ji" mama ta bi ta da kallo tana hango rumaisa da aure.

Ta gama taɓararta mama ta kammala girki, ta ci ta tafi makaranta, sai da yamma da mai sunan baba ya dawo, mama ta yi masa zancen.

Aikuwa ya haɗe rai ya ce "Dama na san ɗawainiyar da suke yi da ita, dole a ƙarshe su nemi wani abu, wane irin aure yaushe aka haifi rumaisan da har za a wani ce a aureta, mutumin da faɗa suke yi ba sa shiri, kawai ki ce musu ba zai yiwu ba su yi haƙuri".

Kasancewar usman yana nan ya ce "A'a fa ayi tunani, yarinyar nan kuna ganin abun da take yi a kan yaron nan, me ake nema a aure ne ba mutum na gari ba, kuma in da za a iya riƙeta ba, idan ta amince kawai ayi musu fatan alkhairi a nawa ganin, mussaman yanzu da ƴan unguwa suke ta ƙananan maganganu a kanta, wataƙila ana yi mata auren ta nutsu"

Wani mugun kallo mai sunan baba yayi masa, dan haka yayi shiru, kuma tun da ya kafe a kan ba ya so, ba zai canza magana ba.

Gaba ɗaya hankalin mama ya rabu biyu, kowannensu yana da gaskiya, ita kanta ba ta shirya rabuwa da rumaisa yanzu ba, dan Allah ya sani rumaisa ba za ta iya ɗaukar ɗawainiyar aure a yanzu ba, dan a sangarce take, sai dai kuma tana matuƙar jin nauyin ammi ta ce mata ba zata basu auren rumaisa ba.

Ayshercool.

08081012143

*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*

*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*

*15. Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*

Maganar ta yi ta damun mama, ta fara tunanin ko Abubakar za ta kira a waya, dan neman shawarar sa, dan ya fi sauƙin kai da fahimta.

Har zuwa dare mama kallon rumaisa kawai take yi, gashi yau ɗin kamar rumaisan ta san abun da ake ciki, sai taɓara take kala-kala da ƙuruciya.

Da daddare ta gama shimfiÉ—arta za ta kwanta, ta É—aga ido suka yi ido huÉ—u da mama.

"Mama wai na ga kina ta kallona?"

Mama ta ce "Mhmm, babu komai".

"Ko kin ga na ƙara girma ne?"

Mama ta ce "Girman ne dai yake tinkaro ki".

"A ina?"

"Ba ko ina, yi kwanciyarki".

Rumaisa ta yi miƙa, ta shige cikin net ɗin ta.

Cikin hanzari mama ta ce "Ke meye haka?"

Rumaisa ta yi zumbur ta tashi ta ce "Mama a ina?"

"Meye haka, daga ke sai wando da vest, ba zaki É—aura zani ko ki saka underwear ba?"

"Kaii mama, kin tsorata ni wallahi, zafi fa nake ji"

"To kuma sai ki kwana tsirara dan shirme, tashi ki saka zani ko kunya ba kya ji sai yayyenki sun shigo sun ganki a haka, ba kya jin kunya ma"

"To mama ba yayyena bane ba"
Chapter 121 · 0% Book details