← Book details Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 106 OF 174

Sashe 106

Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Usman ya ce wa dattijon "Barka da wannan lokaci, fatan mun same ku lafiya?".

Turaki ya jinjina kai ya ce "Alhamdilillah".

Usman ya sake duƙawa ya ce "Ya ƙarin haƙuri na wannan rashi, Ubangiji Allah ya jiƙanta da rahama, ya bada haƙurin jure rashin"

Turaki ya amsa da "Amin 'yan samari, madalla Allah ya yi albarka"

Rumaisa ya kalla da take ta kalle-kalle, usman ya zungureta tayi maza ta kalli turaki ta ce "Ina wuni?" Yayi ƙuri yana kallonta, amma bai amsa ba.

Kallonsa tayi, ta kalli adam sannan ta kalli usman, ta kuma cewa ina wuni.

Adam ya risuna ya ce "Tuba take, ba ta san kan gaisuwar gidan sarauta ba, kamar yadda na yi maka bayani a baya, wannan ita ce wadda ta zo da jaririn wurin marigayiya". Adam ya ƙarasa maganar yana yi mata alamar ta sauke facemask ɗin ta.

Harar Adam ta yi, ta sake jan facemask É—in ta, ta rufe fuskarta.

Turaki ya yi mata ƙuri da ido, tsananin kwarjininsa ya sanyata sunkuyar da kai, ta ji kamar jikinta zai hau rawa, saboda kwarjininsa, sun fi mintuna biyar bai ce komai ba.

Adam ya kuma yi mata nuni da ta sauke facemask ɗin ta, amma taƙi sai da usman ya kalleta, sannan ta cire.

Turaki ya cigaba da kallonta sannan ya ce "Iko, sai Allah yanzu wannan ƙaramar yarinyar ce ta ceto yaron wurin fulani"

"Eh Allah ya baka nasara, ita ta zo da shi"

Ruma a ranta ta ce "Taɓ, wanna wace irin wahala ce, da ban cire facemask ɗin ba, kenan haka zamu yi ta zama ba zai yi magana ba?'.

Turaki ya ce "Bamu labari, ya aka yi aka haÉ—u da fulani, har aka zo mana da jaririnta?"

Rumaisa ta É—an waiwaya ta ce "Wace fulani kuma?"

"Aisha" Adam ya bata amsa.

Sai ta yi turus, ta sunkuyar da kanta ƙasa.

Usman ya ce "Ki yi magana mana"

Ta yi shiru ta shiga wasa da ƙasan rigarta.

Turaki ya ƙura mata ido ya ce "Ke muke sauraro yarinyar kirki" ɗaga idonta ta yi tana kallon adam, da ya murtuke fuska saboda ƙuluwa da ya fara yi, da iskancin da rumaisa ke yi.

"Ko su bamu wuri ne?" Turaki yayi maganar yana nuna su adam.

Ta jinjina masa kai alamar eh, ya ce "To babu laifi, takawa a bamu wuri, kar a damu a bamu wuri mu tattauna".

Takawa bai taɓa zaton iskancin rumaisa ya kai haka ba, ƙin yarda da shi ta yi masa bayanin abun da ya faru, ya sanya yayi zaton a gaban turaki za ta yi bayani, amma mirsisi taƙi magana sai sai ya fita.
Ganin yadda adam ya harzuƙa, ya sanya turaki yi masa alama da ya kwantar da hankalinsa.
Sai dai ba iya adam ɗin ne ya ƙulu ba, har usman ya ƙule da abun da rumaisan ta yi.

Haka suka tashi suka bar falon.

Turaki ya mayar da kallonsa ga rumaisa ya ce "Matso kusa da ni nan ki yi mini bayani"

Rumaisa ta ɗan ƙara matsawa daf da shi, ta hango hoton aisha a bayansa, ta ƙurawa hoton ido, da har sai da turaki ya waiwaya ya kalli hoton.

Ya ɗauko hoton a hannunsa, ya shafa shi ya ce "Kin ganta nan, a cikin 'ya'ya na kusan goma sha rayayyu da wanda suka rasu, babu wadda nake jin daɗinta nake zartar da hukunci komai ɗacinsa ta karɓa sai Aisha. Na tafka babban rashin da ba zan iya maye gurbinsa ba, Allahn da ya bani ya fi ni son ta, ban so ta mutu a wulaƙance haka ba, sai dai ba zan zargi sirikina ba, ɗana ne shima, kuma ba zai cutara da aisha ba"

Rumaisa da hawaye ya fara zubo mata ta ce "Tabbas anty aisha tana da kirki, kowa cewa yake yi bana jin magana, amma ita ta fara cewa rashin ji na yana burgeta. A makaranta bana gan karatu, amma ta ce mini mai kaifin basira ce ni, ta yi ta kula da ni a hannun 'yan bindiga kan ta rasu, amma mijinta ne ba shi da kirki ko kaɗan, shiyasa naƙi magana a gabansa".

Turaki ya yi murmushi ya ce "Tabbas takawa yana da zafin rai, amma mutumin kirki ne sosai".

"Na san a ƙule yake da ni, yanzu ba dan kai ba tsaf sai ya zaneni a wurin nan, ita rayuwa idan mutum yana son ya ci ribar abu ba haƙuri ake a bishi a sannu ba? Idan haka zai din ga yi komai ya tunkara sai ya faɗi. Kuma dai naga ɗan sanda ne shi, mai ya hana ya kai mana agaji lokacin muna hannun 'yan bindigar, da bakinsu fa suka ce jami'an tsaro ne suke basu gudunmawa, to yanzu kuma dan Allah me zai yi bayan mai faruwa ta faru".

Zuba mata ido kawai turaki yayi, yadda take zaro magana, tana arranging ɗin ta, tamakar tana karantowa, kuma ba zaka taɓa cewa yarinya ce mai kamar shekarunta take faɗa ba.

Ya gyara zamansa ya ce "Haka ne, kema kin yi magana mai kyau, amma yanzu dai ina jin ki".

"Baba"

Ya ce "Na'am yarinyar kirki"

"Amanatun amana, zan gaya maka komai, gani ake ni Yarinya ce amma ina da wayona, ta ƙarfin tsiya fa ya ƙwace mini ɗa, ko tausayina ba ya ji alhalin anty aisha ta ce ta bar mini shi halak malak. Zan gaya maka komai, amma shi ba zan gaya masa ba, kuma wallahi na san abubuwan da shi bai sani ba".

Duk girman turaki, ruma ta iya kallonsa ta ce masa amanatun amana, tare da yi masa kashedin, kar ya gaya wa kowa abun da za ta gaya masa.

Ƙwarin gwiwar ta, da rashin tsoronta a ƙananun shekarunta ne ya fi bashi mamaki, kuma tsara zancenta da kaifin basirarta ya burge shi.

Ya ce "Kar ki damu, babu wanda zai ji wannan maganar, daga ni sai ke sai Allah".

Nan rumaisa ta gyara zama ta fara yi masa bayanin abubuwan da suka faru, duk a hirarta ta ya fuskanci ba komai ta gaya masa ba, amma a hakan ta yi ƙoƙarin yi masa duk wasu bayanai da yakamata ya sani, sai dai kan ta kammala, hawaye ya wanke mata fuska, sai gogewa take da hijjabinta.
Shi kansa turaki kasa jurewa yayi, cikin dabara ya goge hawayen da yake shirin zubo masa, yana jin labarin wai-wai a kafafen watsa labarai, bai taɓa zaton masifa da tashin hankalin ya kai haka ba, kuma ta bakin rumaisa ne idan aka fara haɗawa da 'ya'yan masu faɗa a ji ana sacewa wataƙila a mayar da hankali a kan maganin abun, kuma abun kunya ne ga jami'an tsaro, ace an sace matar jami'in tsaro kuma an kasa ceto ta har ta rasa ranta.
Uwa uba azabar da rumaisa ta sha kan ta fito da jaririn, shi kansa ya isa abun tausayi duba da ƙananan shekarunta, gashi sai nanatawa take ita fa aisha ta bar mata ɗa, amma adam ya ƙwace mata.

Ya duba gefen sa, ya ɗauko wani handkerchief mai matuƙar kyau da taushi, sai ƙamshi yake yi, ya miƙawa rumaisa ya ce "karɓi nan ki goge hawayenki, kukan ya isa haka".

Karɓa ta yi, amma ta kasa gogewar, saboda kukan da ya ci ƙarfinta.

Usman kuwa ba ƙaramar mita yayi ba, a kan abun da rumaisa ta yi, tun da suka fito yake mita.
"Ban taɓa ganin yarinya mai azababben taurin kai, na tashin hankali kamar rumaisa ba, gaba ɗaya yarinya kamar wata majanuniya, ita duk wata hanya ta masalaha ba ta santa ba, idan ta akasin masalahar ma aka biyo mata ta fi misbehaving, ba a gane gabanta da bayanta kamar ɗan wake".
Adam kam azabar takaici, bai bari ya iya tankawa ba, gani yake gaba É—aya yarinyar ta gama raina masa hankali.

A nutse turaki ya din ga rarrashin rumaisa, yana yi mata nasiha, har sai da ya sanya ta É—an yi murmushi ta ce "Baba ka iya magana a nutse wallahi, ni yadda kake magana ma daÉ—i yake yi mini"

Abun da ta faÉ—a É—in sai da shi ma ya sanya shi murmushi, ta kai handkerchief É—in da ya bata fuskarta,
Ta lumshe idonta ta ce "Wayyo ƙamshi, baba ban taɓa jin turare mai daɗin wannan ba, kamar na suma dan daɗi".

Jan rawaninsa yayi ya rufe fuskarsa, dan dariya rumaisa take neman ta saka shi.

Hadimai ne suka yi sallama, suka shigo masa da kwanukan abinci a kuloli da kuma akushi, aka zo aka jere su a gabansa.

Rumaisa ta dinga kallon fulasai na alfarma.

Turaki ya ce "Ga abinci nan, buɗe a ciki ki zaɓi wanda ki ke so ki ci".

"A'a na ƙoshi, mama ta hanani cin abinci a waje".

"To ai nan gidanku ne, ki ci duk abun da ki ke so".

Ta nuna masa akushi ta ce "Wannan menene?".

Ya É—auko akushin ya ajiye a gabanta ya ce "Sunansa akushi".

"Akushi da rufi, sai sarki, kenan kai ma sarki ne?"

Ya girgiza mata kai ya ce "A'a, ni ba sarki bane ba".

"To dama ba duk masu rawani ba sunansu sarki ba"

Turaki ya murmusa ya ce "A'a ba kowane mai rawani ne sarki ba, kowa akwai sunan muƙaminsa"

Ruma ta din ga kallon akushin nan, ta saka hannu ta buɗe, ta ga dubulan fal a ciki" tayi iya ƙoƙarinta wurin tuna sunan sa amma ta kasa ta ce "Mmm ya ma, abun da ake kaiwa idan an yi aure mai sugan nan sunan shi kenan".

Ya kuma miƙo mata wani akushin, ya ce "Gashi nan, duk duba ki ci wanda ki ke so".

Ta bubbuÉ—e kulolin nan, wata irin miya ta alfarma, ta sha naman kaza yanka manya manya. Ta ce "Mama ta yi mini kashedi a kan banda rashin ji, kuma idan na yi wani rashin ji, yaya usman ya gaya mata zaneni za su yi".

Turaki da bai ji ya gaji da surutun rumaisa ba, kuma bai jin zai gajin ya ce "Ki ci ba zan gaya masa ba, ba zata sani ba".

"Hmm ba ka san halin mama ba, yaya usman sai ya gane, amma dai bari na ci wannan".

Ta saka hannu ta É—au dubulan, ta fara ci, dama rumaisa gata mayyar suga, tana ci tana lashe baki.
Chapter 106 · 0% Book details