← Book details Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 169 OF 174

Sashe 169

Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Waye ya ce ka É—aukar mini littafi? Ba ka ga gargadin da na yi a farko ba?".

"Me wannan zanunnukan suke nufi, bayan kin ce mini, ke baki san komai ba? Meye ƙarashen wannan zanunnukan, kuma a wace tashar motar ku ka hau mota?"

Tura baki ta yi ta kawar da kai, ya nufeta gadan-gadan, nan take ta ga idonsa ya fara wannan hayaƙin.

"Yi haƙuri, ka bani zan yi maka bayani"

Ya miƙa mata littafin, sai dai tana karɓar littafin, ta riƙe towel ɗin ta, ta kasa da gudu ta bar ɗakin.

Ayshercool.
08081012143
Paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012243, ga masu buƙatar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book ɗin. Kar ku manta da subscribing YouTube channel ɗinmu na Cool hausa novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ƙanwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel ɗin*

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Susbcribe my YouTube channel please 🙏

Bai yi wata-wata ba ya rufa mata baya, tuni ta yi downstairs, tana riƙe towel ɗin ta, ko da ya sauka ƙasa ya neme ta ya rasa.

Ya kalli Asiya da take mopping a falon, ya ce "Ina ta shiga?"

Ta nuna masa kitchen, da sauri ya shiga kitchen ɗin, ya tarar da ita da barira, ta yi wuƙi-wuƙi da ido ta na kallon sa, sai dai ta ɓoye hannunta a bayanta.

"Ina yake ina littafin? Ina ki ka ajiye shi?"

Shiru ta yi masa ta na bin sa da kallo.

Takowa ya fara yi, yana cigaba da tambayarta, sai dai ta fara ja da baya, ganin idonsa ya cigaba da wannan hayaƙin.

Sai da ta dangana da jikin bango, ya zo ya tsaya a kanta.

"Wannan abu ne da ya shafi rayuwata, kacokan da iyalina, ba na wasa da duk wani abu da ya shafi aisha, zuwa yaushe zaki cigaba da wahalar da ni ne? Ki gaya mini abun da nake buƙata, ki yi mini bayanin zane-zanen da ki ka yi?".

Kawar da kanta ta yi gefe, daga kallon fuskar sa, tare da bawa kanta ƙwarin gwiwar jure duk wani abu da zai yi mata.

"Am talking to you!" Yayi maganar cikin shouting.

"Ni ka ƙyale ni, ai ba da iznina ka ɗau littafin ba" ta ƙarasa maganar tana ƙoƙarin jan jikinta ta wuce.

Dannata ya yi a jikin bango, ya zura hannunsa bayanta, ya banƙara hannunta, ta zunduma wani uban ihu, sai dai babu littafin a hannunta.

Hayaƙin da kitchen ɗin yake yi ne, ya sanya shi ɗaga kai, kawai ya hango littafin ta tura a cikin gas, yake ƙonewa.

'Innalillahi wa Innalillahi raji'un ' ya faɗa a zuciyarsa, bai taɓa ganin halitta mai azabar taurin kai da masifa, kamar wannan yarinyar ba'.

Baba uwani kuwa, magiya take yi masa a kan ya taimaka ya rabu da rumaisa, saboda yadda take kururwar zai karya mata hannu.

Da sauri ya nufi gas ɗin, barira ta ja da baya, saboda gaba ɗaya fuskarsa har ta fara sauyawa, saboda azabar ɓacin rai da fushi. Sai dai kash tuni littafin ya babbake, ya zama toka.

Rumaisa kuwa zubewa ta yi a wurin, tana yarfa hannunta, saboda yadda take jin sa tamkar ba a jikinta ba.

A fusace ya waiwayo ya kalleta, ya zo ya sake danƙar hannunta, ya ja ta daga kitchen ɗin.

Baba uwani ta bi shi tana yi masa magiyar ya rabu da rumaisa, amma ya shareta, rumaisa ta saka hannunta ɗaya, ta riƙe towel ɗin da yake barazanar faɗuwa. Duk wannan masifar da haƙilon, idon rumaisa mursisi, ba ta yi dana sanin abun da ta aikata ba.

Ɗakinsa ya wuce da ita, ya rufe ƙofar gam, ya tankaɗata kan gadonsa, ta zauna daɓas, ita kokowarta kar towel ɗin ta ya faɗi ƙasa.

"Ki gaya mini me ki ka sani game da mutuwar aisha, da saceta?".

"Wai ya ka ke tamabyata kamar ni na sace ta? Ni ban san komai ba, ni ma fa sace ni aka yi".

"Amma kin san wani abu, akwai abun da ki ke ɓoye wa, atleast a bayaninki akwai wani abu da zai taimaka, na gane idan saceta haɗin baki ne".

Ta ce "Oho, ni dai ban san komai ba, zanena kawai nake yi, idan kun ji haushi, tun da ku jami'an tsaro ne ku din ga aiki tsakani da Allah, ni ka daina yi mini masifa, ba abun da na sani".

Cikin matsananci fushi, ya ce "So ki ke na illataki ko? Idan ki ka bari na yi miki illa, na yi wa banza, ke zaki nakasa ba ruwana. Kin san muhimmancin aisha a wurina kuwa? She don't deserve, such kind of death, ki yi mini bayani kan na yi miki illa"

A karo na biyu ta sake kawar da kai, ta na zumɓura masa baki.

"Kalleni"

"Ni ba zan kalleka ba, kai baka ganin abun da yake fitowa daga idonka?".

Ba ta yi tsammani ba, ta ji ya riƙe gashin kanta ya ja, sai da ta kusa shiɗewa, ta miƙe tsaye tana ƙoƙarin ƙwacewa.

Ga mamakinta, sai ta ga fuskarsa ma ta fara baƙi, duk ya yi wani iri.

A take mafarkin da ta taɓa yi, ya fara ƙoƙarin zama gaskiya, dan faratansa ya fara karta mata a wuyanta, ya kuma shaƙeta ya na wani irin kakari.

Da fari su barira sun biyo bayan baba uwani, baba Uwani ta kasa kunne a jikin ƙofar, ta na jiyo abun da suke cewa, sai dai tun da rumaisa ta yi ƙara suka ji shiru.

Jiki na rawa barira ta ce "Baba uwani, ko mu kira masu gadi, a ceto ta, kar ya yi mata illa".

Baba uwani ta ce "Ke ina ruwan ki? Dalla ku wuce ku je ku cigaba da aikinku"

Rumaisa kuwa bayan ya yi mata wannan shaƙar, sai da  ta suma, ya saketa ta faɗi ƙasa, sannan ya yanke jiki ya faɗi a gefenta, cikin yanayi mai kama da bacci.

Asiya kasa nustuwa ta yi, ta ce "Barira, tsoro nake ji fa, kar ya kasheta, ko police station aka kaimu bayar da shaida an cucemu".

"Bari kawai, wallahi nima a tsorace nake, ga matar nan ta hana a nemo taimako".

Asiya ta ce "Bar Æ´ar rainin hankali mana".

"Ita ma dai, ta na da azabar taurin kan tsiya, ni ina girki kawai na ga ta shigo da gudu, ta tura abu a wuta, zan yi magana ta ce in yi shiru, sai ga shi ya biyo ta, amma na ji yana magana a kan Aisha, wataƙila abu ne mai muhimmanci da ya shafe ta".

"To waya sani, ni dai fatana kar ya illata kawai".

Bayan sa'oi uku, Adam ne ya fara yin juyi, dan ji yake kamar barci yake yi, kawai ya ga rumaisa a kwance a ƙasa, ita daban towel ɗin ta daban, da ga ita, sai gajeren wando.

Tashi ya yi zaune yana ƙoƙarin tuna abun da ya faru, kawai dai ya iya tuna yadda ya janyota har ɗakinsa, amma daga nan komai ya goge a kansa.

Tsura mata ido ya É—an yi, yana tunanin ko barcci take yi ne? Amma sai ya ga yanayinta bai yi kama da haka ba.

'Ko wani abun na yi mata?' ya tambayi kansa.

Matsawa ya yi kusa da ita, ya É—agota, ya ga jikinta a sake.

A gigice ya ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, i lose my sense again?" Rabon da ya fita completely daga hankalinsa haka, an kai shekaru goma, ko ya yi loosing control, ya na iya tuna abun da ya faru, amma completely yau ya kasa tunawa.

Wuyanta ya kalla, duk shedar an karceta da farce.

Ya É—an girgiza ta ya na kiran sunanta.

"Rumaisa!" Amma shiru ba ta motsa ba, ya taɓa hannunta, ya ji zuciyarta na bugawa, numfashi da take yi a hankali.

Ya kwantar da ita ya shiga banɗaki, ya ɗebo ruwa a hannunsa, ya dawo ya shafa mata a fuskarta, ya ƙure gudun Ac da na fanka.

Bai ɗaura mata towel ɗin ba ya ƙyaleta, ya lulluɓe ta da shi, ya tsura mata ido yana fatan Allah ya sa ta farka, dan kuwa idan ya ɗauketa ya kai ta asibiti, asirinsa zai iya tonuwa, dan babu lallai ta yi shiru, kuma dole a tambayi mai ya sameta, ya cigaba da addu'a Allah ya sa ta tashi.

Babu tsammani, kawai ya ga ta tashi zaune, tana ganinsa ta ja da baya, ta kare jikinta da hannunta.

Sai a lokacin ya yi ajiyar zuciya "Ki É—aura towel É—in mana" ya faÉ—a a sanyaye.

"Dole ka ce na ɗaura mana, bayan ka yi mini tsirara, za ka kasheni, wallahi gida zan gudu, ba zaka kasheni ba? A hakan zan gaya maka abun da na sani ɗin? Dama ban san komai ba ma, wallahi ba zaka kasheni a banza ba, ka shaƙeni kamar wata ɓarauniya".

A hankali ya ce "Ya ilahi, i attempt to kill her?'

Ta saka hannu ta ja towel ɗin, ta rufe jikinta, ta yinƙura ta tashi, ta fice daga ɗakin.

A hankali ya lumshe idanunsa, ya bawa hawayen da suka taru a idonsa damar zuba, ba zai so ammi ma ta ji wannan maganar ba, iya rayuwarta a hanyar nema masa magani take, ana murna abu ya ɗan yi sauƙi sai abun da ba a rasa ba, kwatsam yau abu ya dawo kamar da.

Sai ya ji tashin ciwon nan nasa, ya shafe abun da rumaisan ta aikata masa.

"Mahaukaci ne ni? Ko kuma maye? Ko kuma namiji mai mutanen ɓoye, wato aljanu?" Tambayar da tun da ya shekara takwas a duniya, yake yi wa kansa da ya gaza samun amsarta.

Ba shi da tabbacin rumaisa ta rufa masa asiri, haka zalika bai san ta ina zai fara yi mata bayani, ta fahimce shi ba, sai a lokacin yake ganin rashin kyautawar da aka yi, na rashin yi musu bayanin larurarsa.

Madigar kuwa ta na zuwa É—akin ta, gado ta hau ta cigaba da bacci.

Baba uwani kuwa, ta fita ta zagaya, jikinta na tsuma, ta kira lambar Mummy.
Aka yi sa'a mummy na kusa, ta É—ag wayar, gulma na cin ta ta ce "Allah ya taimake ki"

"Ina jin ki".

"Akwai abun da ya faru".

"Je ki kai tsaye".
Chapter 169 · 0% Book details