← Book details Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 174

Sashe 56

Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kar ka ce komai, in dai ruma ce, da kansu za su tattaro su dawo da ita, ka taho ka barsu".

Ayshercool.

*Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*

Abin da gwaggo ta yi ba ƙaramin ɓatawa Aliyu rai yayi ba, da ya san haka ne da ba zai taɓa bari ta saka a kai ruma ko ina ba, daga zuwa ziyara kawai ta riƙe 'ya wai sai wani lokaci.

Ya sake duban gwaggo ya ce "Gwaggo, ruma fa ba zata yarda ta zauna a garin nan ba, rigima za ta yi miki idan ta dawo ta tarar na tafi na barta".

Gwaggo ta ce "Babu komai, na san yadda zan shawo kan kayata, amma a yanzu dai ba in da zata".

Takaici ya ishi Aliyu, ya bi gwaggo da kallo.

"Gadanga ko dukana zaka yi ne? Na gama yanke hukunci, idan kuma kaima zaka zauna ne ni haka nake so, sai mu zauna idan lokacin yayi sai ku tafi duka".

Tabbas ba dan gobe yana da test mai muhimmanci a makaranta ba zama zai yi, ya saka lawalli a gaba sai ya kai shi ya É—auko ruma, amma ba yadda iya ya É—auki jakarsa ya fice.

****
Har Adam yayi kwanakinsa uku a birnin tarayya, bai iya aikata komai ba, saboda da ya fita da niyyar zuwa wani wuri, sai jiki ya hau rawa kai ya hau ciwo, ga ruma da ta addabawa rayuwarsa ya kasa mantawa da ita, komai yake yi sai ya din ga ganinta.
Bayan ya cika kwanaki huɗu, ya kira Ammi yayi mata ƙaryar bai gama abin da yake yi bane, sai dai tattaunawar haka aka yi ta babu shi, duk da halartarsa tattaunawar na da matuƙar muhimmanci.
A kwana na biyar ya kira direbansa a waya, ya ce ya zo da mota ya same shi a hotel É—in da yake.
Ƙarfe biyu direban ya sameshi, sai dai a wannan karon cikin ikon Allah tun da ya fito sau ɗaya kan ya sara, jiri ya ɗan ɗebe shi, amma  ya tattara nutsuwartsa, yana addu'a, ya nufi motar.
Suka gaisa da direban nasa, yayi masa ya hanya, daga nan ya ce ya gaya masa in da zai kai shi.
Mintuna ashirin ce ta kaisu, a harabar wata plaza suka yi parking, Adam ya buÉ—e motar ya fita.

Wani matashi ne zaune wanda zai yi sa'an Adam, yana danna computer, yana ganin Adam ya miƙe cikin girmamawa yana murmushi ya ce "Barka da zuwa"

Adam ya ƙarasa yana murmushi, ya miƙa masa hannu suka gaisa, sannan ya zauna.

Matashin ya kalli Adam ya ce "Adam, ya aka yi an shirya zama da kai, amma ba ka yi attending ba?, na din ga kiran wayarka ba ka É—agawa, har wayar ma ta daina shiga gaba É—aya?"

Adam ya ɗan taune lips ɗinsa na ƙasa ya ce "Am sorry Habib, wata matsala aka samu, amma komai normal yanzu in sha Allah".

Cikin kulawa Habib ya ce "Are you safe?"

Adam ya jinjina kai sannan ya ce "Me aka tattauna, wace matsaya aka cimma?"

Habib ya ɗan rausayar da kai ya ce "To, mun tattauna yadda yakamata, amma dai kamar yadda na yi maka bayani da farko, ko da ka fito ƙarara ka bayyana lamarin nan, ko an je kotu za a sake su, saboda haryanzu baka da wata cikakkiyar hujja ta zahiri da zaka kafa, yanzu ko kun yi wani abu a kai, ya riga ya gama shiri, da tattaunawa da lawyoyinsa, ya shirya tsaf da ka yi attacking zai yi depending, yanzu abin da yafi shine ka sake mayar da hankali sosai da kai da abokan aikinka, ku samo hujja ta gaske, ta zahiri da za ayi amfani da ita, nima zan shirya tsaf domin cimma nasara ni da tawagarmu"

Adam yayi ajiyar zuciya tare da dafe goshinsa, ya sake ɗagowa ya kalli Habib ya ce "Duk wata hanya da zan bi domin neman hujjar kama mutumin nan an tosheta, kuma kullum kallon mutunci ake masa, ana sake bashi girma tare da shigar da shi cikin al'amuran ƙasar nan, bayan su ne babbar matsalar mu"

"Adam, tun da ka ga haka, ba shi kaÉ—ai bane, ko dai an san me yake yi ake rufa masa asiri, ko kuma akwai wasu manyan da suke aikin tare "

"Haka ne, abin da nake tunani kenan nima, amma babu komai in sha Allah zamu yi nasara, zan cigaba da ƙoƙari, ina son magana da saifu ma, zan zauna a garin nan sai Allah ya kaimu monday zan koma kano".

Habib ya ce "To shikenan, Allah ya yi jagora, gashi ko shayi ban baka ba"

Adam ya girgiza kai ya ce "Kar ka damu"

Daga haka Adam ya tashi ya fita, ya saka direbansa ya mayar da shi masauki. Sam ya ƙi yadda yaje gidan sa, saboda wani Dalili nasa.

***

Ƙauye ne sosai in da aka kai ruma, sai dai mutane masu matuƙar karamci da girmama ɗan Adam, tamkar za su goya ruma, dan wasunsu duk basu santa ba, sai dai sun san mahaifinta sosai tunda ɗa ne a wurinsu.
Garin sun yi noma sosai, sai dai an girbe an tare shi a cikin gonaki, ba a kwashe an kai gida ba, ga yanayin garin kamar yanayin garin da aka yi wata annoba.
Wani wurin a ƙone, wani wurin dai gashi nan.
Tun da safe ruma ta fara cewa ita azo a mayar da ita gidan gwaggo, yau zasu koma gida ita da yaya Aliyu, amma dattijon da ya kasance ƙanin kakanta ne ya ce "Ai jikata ba ke ba tafiya, sai hutun makarantar bokonku ya ƙare, kina nan tare da mu"

A É—an razane ruma ta ce "Saboda me?"

"Haka gwaggonki ta ce"

"Ni gaskiya ba zan iya zama a garin nan ba, gida nake so na koma na ga mama, na gaji, ni ku mayar da ni gida" ta yi maganar tana kuka.

Matarsa da ake kira da iya ta ce "Haba rumaisa, muma fa duk iyayenki ne, muna ƙaunarki sosai, ki kwantar da hankalinki kin ji, za a mayar da ke, idan ki ka matsa zasu iya ƙwaceki gaba ɗaya, 'yan kwanaki zaki yi a mayar da ke"

"Ni mama nake son na gani".

"Ki yi haƙuri, za a mayar da ke in dai wurin mama ne" An kai ruwa rana sosai da ruma, kan ta daina koke-koke, sai dai ita ma ta haɗa musu aiki, ba komai take ci ba, tsirfar yau daban ta gobe daban.

In da ta ɗan ƙara samun sassauci, shine tana tare da lawisa, kuma a gidan akwai wata sa'ar tata zaliha, dan haka sukan ɗebe mata kewa.

***
Ba ƙaramin ɓacin rai 'yan mazan mama suka shiga ba, tun bayan da Aliyu ya dawo musu babu ruma, tare da sanar da su hukuncin da gwaggo ta yanke ba.
Abdallah ya ce "Wallahi gwaggon nan tana da matsala, tsabar mugunta ta yi garkuwa da yarinya dan son zuciya daga kai mata ita a sada zumunci".

Sai da suka yi dariya jin abin da ya ce, wai tayi garkuwa da ita.

Usman ya ce "Wane irin garkuwa kuma?".

"To idan ba garkuwa ba, ta yaya zata saka a kai yarinya wani ƙauye a ɓoyeta, wai ba zata dawo yanzu ba, amma idan ta cika musu ciki da rashin ji, ai sa dawo da ita da kansu"

Suna cikin tattaunawar mai sunan Baba ya dawo, suka gaisa da Aliyu, ya tambaye shi ina ruma? Ya sanar masa da yadda suka yi da gwaggo.

Tsuke fuska yayi ya ce "Wane irin abu ne haka? Idan na gama exams ranar lahadi zan je na taho da ita, akan me zasu riƙe ta?"

Mama ta ce "A'a babana, tun da na haƙura dan Allah kuma ku yi haƙuri ku ƙyalesu, yanzu sai ace zigaku nake yi, su je su ƙarata, sati biyu ai kamar yau ne"

"Duk da haka, bai kamata ruma ta zauna a wurin nan ba, babu tsaro gaba É—aya dole zan je na taho da ita, dan ba ta zuwa makarantar boko yanzu, islamiyya fa?" Sosai ya É—au zafi, mama dai ta ce ba ta yadda wani yaje ya ce zai taho da ruma ba.

***
Gaba daya ta tattara hankalinta da nutsuwarta a kan litattafanta, gefe kuma ga calculator tana dannawa, tayi ɗai ɗai a ƙasan carfet, ta saki dogwayen kalbar da aka yi mata, ta zubo har kafaɗarta, duk da kalbar ta tsufa amma ta yi kyau sosai.
Nusaiba ta turo ƙofar ɗakin ta shigo da sallama.
Iman ta amsa mata, ta zuba mata ido tana kallonta.

"Sarkin littafi, me kuma ake yi?" Iman ta kalli litattafan ta yi murmushi ta ce "Boko nake ci masoyiyya, ta samu ne?"

Nusaiba ta zaune ta ce "Eh to, ba nace ba, uncle J ne ya zo, kuma da alama ke yake son gani, sai tmbayata yake kina ina?"
Tsaki iman tayi, ta gyara zamanta tana ƙoƙarin mayar da kanta kan litattafanta.

"Kai, uncle J É—in ki ke yi wa tsaki, ya zo ya sakani a gaba sai tambayata yake kina ina?"

"Anty Nusaiba dan Allah ki ƙyaleni da sabgar mutumin nan, wai me zan yi masa ne dan Allah?"

"Nifa na kasa gane abin da kuke ɓoyewa, anya ba sonki yake yi ba?"

Da sauri iman ta girgiza kai ta ce "Dan Allah Anty Nusaiba kar ki ɗaga maganar nan, idan har Ammi ta ji za ta bayar goyon bayan hakan, ni kuma ba zan watsa mata ƙasa a ido ba, amma ni bana sha'awar duk wani wanda ya fito daga masarautar na, ke kin san me nake nufi".

Nusaiba ta yi ajiyar zuciya ta ce "Shikenan, na daina cigaba da aikin ki, zan je na ce masa bacci ki ke kawai"

Iman ta jinjina kai alamar to.

****
Tafe suke su uku, ruma na ta shan tsamiyar biri tana zubarwa a hanya, mayafinta a kafaÉ—a. Su fuskarsu duk da hoda da kwalli, ruma kuwa tata yadda take haka take kamar namiji, kunneta babu ko É—an kunne.

"Kai ku tsaya" ruma tayi maganar tana kallon wata bishiyar mangwaro, 'yar gajeriya amma tayi 'ya'ya fal.
Chapter 56 · 0% Book details