Sashe 146
Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Lokacin da ki ka san abu yakamata, ba sai wani ya saka ki ba, sai ki neme ni, yayyenki na ƙoƙari wurin baki tarbiyya, Allah ya biya su, kuɗi kuma ki zubar" ya kashe wayarsa.
Dungurar da wayar ta yi a ƙufule, ta ce "Yaya usy kalli abun da ka janyo mini"
Dungure mata kai yayi ya ce "Ki ka jawa kanki dai, ke a rayuwar duniya baki iya siyasa ba? Ji yadda ki ke gantsara masa magana, kamar kashi ba tausasa lafazi, ba É—an karya murya, wai ke ma namiji ce irinmu ne? to ko mu muna kashe murya, ranar da na kama malam habu yana waya, kamar ma nutse dan kunya, amma ke kina ta wani shirme.
Ke, tashi mu je ɗaki, na yi miki bayanin me auren ya ƙunsa, in fayyace miki komai in gaya miki, na ga mama ba ta da niyyar gaya miki, daga ita har su gwaggon.
Aliyu ya ce "Kai fa wasu lokutan baka da kamun kai, uban me zaka gaya mata?".
"Komai ma gaya mata zan yi, yo haka za ta je ta zauna masa a gida kamar gardi, idan ka ga tana tausa murya to wani abun take nema, tashi mu je na fayyace biri har wutsiya".
Aliyu da dariya ta ƙwace masa ya ce "Mama, wallahi usman ya zama abun da ya zama, zai juyawa yarinya tunani, saboda bashi da kamun kai".
Usman ya ce "Eh, bani da kamun kan, ni ina ma ni za ayi wa auren nan, wai muna zaune Æ´ar da aka haifa a gabanmu za ta rigamu girma Allahu Akbar wata shekarar sai ta fara Æ´a Æ´a kuma".
Aliyu ya ce "Wani irin ta fara Æ´aÆ´a wata shekarar, kamar wata bishiyar lemo, wannan yarinyar ko nan da shekara biyar albarka"
Wani irin kallo Usman ya yi masa ya ce "Haba, a banza za ku kaita ya din ga bata abinci, yana biya mata kuɗin makaranta ko? You don't get sense. Ko kaza dan a cinyeta ake killace ta a sai mata dusa, kar ka yaudari kan ka".
Aliyu ya ce "kai haba, she's too young for it, and the man is very decent and calm, bana tunanin haka".
Usman ya yi dariya ya ce "Uban calm da decent É—in, that thing don't get sense, don't fool yourself, if not ku fasa aurar da ita, hauka ake mutum zai kashe kuÉ—i ya auri Æ´a ya sakata a gaba yana kallonta, Allah ya sa jaririya ce"
Aliyu ya yi tsaki ya ce "Zaka ɓata mini rai "
Rumaisa da ba gane kan hirar take ba, ta din ga bin su da kallo, Usman ya ce "To Algume, sai kallon bakinmu ki ke, ƙila kin san komai, ki ka yi wani kasaƙe da kai".
Aliyu ya ce "A hakan ta san komai? Tana wannan gidadancin".
Usman ya ce "Kuma fa haka ne, to jeki na fasa gaya miki komai, duniya zata gaya miki, Allah ya shiryeki".
"Nuraini, Allah ya baka abun yi na aurara da kai, ina ga daga rumaisa kuma sai kai, tun baka wuce in da nake tunani ba" a guje Usman ya faÉ—a É—akinsu, dan sam bai san mama ta ji hirarsu ba.
***
Jabir ya din ga juya invitation É—in, sannan ya kalli Adam ya ce " da gaske Adam saura kwanaki a É—aura maka aure, amma ban sani ba?"
"Am sorry, abun ne ya zo cikin gahgawar gaske fiye da yadda na yi zato, sai haƙuri".
Jabir ya sake kallon invitation É—in, sannan ya ce "To ita kuma wacece, a ina take? Kamar na san sunan nan".
Adam ya ce "Zaka ganta very soon".
"Da jamil ya gaya mini maganar auren nan, na zaci da wasa yake yi, ashe da gaske ne, Allah sarki samha ina tausayin yarinyar nan sosai".
Adam ya ce "Please, don't raise that issue here, ku daina ganin laifina, ƙaddara ce ta zo a haka".
Jabir ya ce "Na yadda, ban ce wani abu ba, kawai dai ina jin tausayinta ne, sai dai na yi mamakin yadda har ka nemi aure, har ka samu ban sani ba, yaushe muka fara haka da kai".
"Jabir, this is an arranged marriage, ku yi mini uzuri".
Jabir ya ce "Arranged marriage, to Allah ya sanya alkhairi ya sa za ayi da mu".
"Amin, addu'arku nake buƙata dama, yanzu ka tashi mu je gidan mai girma turaki, zan kai masa nasa katin, da zai bawa mutanensa, da na jamil da gidan gaba ɗaya".
Jabir ya ce "Ok, ba damuwa bari mu yi salla tukuna"
Bayan sun idar da salla, suka tafi gidan turaki, kai tsaye sashinsa suka shiga, bayan sun tarar da babu kowa a falon.
Yayi murna sosai yayi addu'a da fatan alkhairi, sannan ya yi wa adam nasiha sosai mai shiga jiki. Sai dai kamar haÉ—in baki suka tarar da mama da Samha, har ma da zainab a falo.
Samha jikinta har tsuma yake da ta ga Adam, ga soyayya ga kuma kishi, ya gaida mama ta amsa masa sama-sama, ta saki jiki ta amsa gaisuwar Jabir.
Su Samha suka gaishe shi ya amsa, ya ajiye wa mama katuna, ya ce "Gashi nan, ammi ce ta ce in kawo miki, na taron wunin da za ta yi, na bawa mai girma turaki nasa".
Da ƙarfi Samha ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Adam wai dama da gaske ne, ta tabatta aure zaka yi?" Ya ɗaga kai ya kalli Samha da tsoro da kishi ya bayyana a fuskarta, ya jinjina mata kai a hankali cikin tausayawa.
"Shikenan, bakomai na gode " ta tashi ta bar falon. Jikin Adam ya yi sanyi, mama kawa jan tsaki ta yi ita ma, Zainab kuwa cewa ta yi Allah ya sanya alkhairi.
Æangaren ammi ma, da ta bawa mummy katin gayyata, masifa mummyn ta din ga yi, wai har ace adam zai yi aure, amma a kasa sakata a cikin lamarin bikin, sai dai ta zo a Æ´an gayya, saboda ba a mayar da ita a bakin komai ba.
A gidansu rumaisa ma, shirye shirye sun yi nisa. Mai sunan baba ya buga wani invitation ɗin na ɗaurin aure, aka rubuta sunan Adam sharif, ba tare da sanya cikakken sunan Adam ba. Ba ƙaramin mamaki ƴan unguwar su rumaisa suka yi ba, jin za ayi mata aure, wasu suka din ga surutu suna cewa sai ka ce a ƙauye, wasu kuma suka ce ta tabbata rumaisa ta yi cikin shege ne, ake son a liƙawa wani, kuma aka kasa gane wanene mijin, sai dai hatta wurin da aka rubuta za ayi bukukuwan a wurin ba ƙananan wuri ba ne, nan ma aka yi ta surutun ina suka samu kuɗin kama wannan wurare.
Zaman Gwaggo a gidan, ta din ga yi wa rumaisa faɗa, tare da nasiha a kan aure, da yadda za ta kula da miji, sai dai sam rumaisan ba ganewa take yi ba, yadda aka sakata a gaba ana sake koya mata girki ya fi komai ci mata rai, a ganinta ana hanata hutawa, girkin nan da karambani ta iya shi, dan tun shekara tara take gwadawa, tun mama tana hanata har ta haƙura ta rabu da ita.
Samha ta yi kuka kamar zata yi hauka, gaba É—aya ji take komai ya fita daga ranta, ko abincin kirki ba ta iya ci, sabuwar soyayyar adam ta dawo mata sabuwa fil, sai dai ta yi alwashin yadda ta zubar da hawayenta a kan sa karo na biyu, daga shi har matar ta sa sai sun É—anÉ—ana kuÉ—arsu.
Fauziyya ta din ga zigata a kan ta san duk yadda za ta yi, ta cuzgunawa matar da adam zai aura, har da ba ta tabbacin cewa, ta ji an ce auren haɗi ne ba son ta yake yi ba.
Ana gobe za a yi wa rumaisa jeren kaya, Adam ya É—auki Aliyu da Abdallah, zuwa gidan rumaisa, dan su gani daga nan ya basu mukulli.
Sai dai da suka je, Aliyu ya raina kayan da suka saya, da suna ta murna sun yi wa rumaisa kaya masu kyau da yawa, sai dai gidan babba ne sosai.
Sama da ƙasa ne, ƙasan akwai babban falo, da ɗakuna biyu, da kitchen da store, saman bene kuma falo biyu, bedroom uku, da kitchen da dining, kowane ɗaki da toilet.
Gidan ya tsaru yayi kyau, dan an kashe kuÉ—i wurin yin sa sosai.
Aliyu suka yi ta santin gida, suna yi wa Adam godiya. Sai dai tun da suka koma gida suka sanar da mama, gidan yafi ƙarfin abun da za a kai, jikinta yayi sanyi, dan ba dan kar ta nuna halin ƙaranta ba, cewa za ta yi idan da ƙarami a saka rumaisa a ciki.
Kaf Æ´an unguwa ba wanda mama ta ce su je yi wa rumaisa jere, Æ´an uwanta da Æ´an uwan mahaifinsu rumaisa, sai yayyenta ne suke je suka jera mata abun da ya samu a saman benen.
Gado biyu aka yi mata, dangin babansa suka yi mata ƴan waje guda ɗaya, yayyenta suka yi mata ƴan gida, masu matuƙar kyau.
Kitchen É—in ta ma babu laifi, a dai Æ´ar talaka, iyayen rumaisa sun taka rawar gani sosai da sosai, ga kujerunta da labulaye, ga dininga komai dai-dai gwargwado.
Ƴan uwa suka dawo, suka din ga santin gida, suna yi wa mama barka da arziki, rumaisa ta je gidan hutu.
Da daddare Adam ya je gida da shi da su ammi, suka ga jeren da aka yi, ammi ta jinjinawa ƙoƙarin iyayen rumaisa, ba ita ba shi kansa adam, abun ya bashi mamaki, aka jere mata akwatunanta goma sha biyar a bedroom.
Washegari Adam ya saka aka kawo abubuwan da babu, wanda basu ƙarasa ba.
Rumaisa ba ta yadda aurenta za ayi ba sai da satin biki ya kama, dama Aliyu sun shirya football match, a nan cikin unguwa.
Tun da rumaisa ta tabattar da idan aka yi auren barin gidan za ta yi, ta fara koke-koke tana fasa.
Ranar da za ayi bridal shower, daga gidan su adam, aka aiko da mota, aka ɗauki rumaisa zuwa gidan kwalliya, ita da ƙawayenta, babu ko sisinsu, aka yi musu kwalliya aka wuce da ita wurin biki.
Su Iman tuni suna can, sun sha kwalliya iman kamar balarabiya, da ita da wasu daga cikin famylinsu, da su ƙawayenta.
Dungurar da wayar ta yi a ƙufule, ta ce "Yaya usy kalli abun da ka janyo mini"
Dungure mata kai yayi ya ce "Ki ka jawa kanki dai, ke a rayuwar duniya baki iya siyasa ba? Ji yadda ki ke gantsara masa magana, kamar kashi ba tausasa lafazi, ba É—an karya murya, wai ke ma namiji ce irinmu ne? to ko mu muna kashe murya, ranar da na kama malam habu yana waya, kamar ma nutse dan kunya, amma ke kina ta wani shirme.
Ke, tashi mu je ɗaki, na yi miki bayanin me auren ya ƙunsa, in fayyace miki komai in gaya miki, na ga mama ba ta da niyyar gaya miki, daga ita har su gwaggon.
Aliyu ya ce "Kai fa wasu lokutan baka da kamun kai, uban me zaka gaya mata?".
"Komai ma gaya mata zan yi, yo haka za ta je ta zauna masa a gida kamar gardi, idan ka ga tana tausa murya to wani abun take nema, tashi mu je na fayyace biri har wutsiya".
Aliyu da dariya ta ƙwace masa ya ce "Mama, wallahi usman ya zama abun da ya zama, zai juyawa yarinya tunani, saboda bashi da kamun kai".
Usman ya ce "Eh, bani da kamun kan, ni ina ma ni za ayi wa auren nan, wai muna zaune Æ´ar da aka haifa a gabanmu za ta rigamu girma Allahu Akbar wata shekarar sai ta fara Æ´a Æ´a kuma".
Aliyu ya ce "Wani irin ta fara Æ´aÆ´a wata shekarar, kamar wata bishiyar lemo, wannan yarinyar ko nan da shekara biyar albarka"
Wani irin kallo Usman ya yi masa ya ce "Haba, a banza za ku kaita ya din ga bata abinci, yana biya mata kuɗin makaranta ko? You don't get sense. Ko kaza dan a cinyeta ake killace ta a sai mata dusa, kar ka yaudari kan ka".
Aliyu ya ce "kai haba, she's too young for it, and the man is very decent and calm, bana tunanin haka".
Usman ya yi dariya ya ce "Uban calm da decent É—in, that thing don't get sense, don't fool yourself, if not ku fasa aurar da ita, hauka ake mutum zai kashe kuÉ—i ya auri Æ´a ya sakata a gaba yana kallonta, Allah ya sa jaririya ce"
Aliyu ya yi tsaki ya ce "Zaka ɓata mini rai "
Rumaisa da ba gane kan hirar take ba, ta din ga bin su da kallo, Usman ya ce "To Algume, sai kallon bakinmu ki ke, ƙila kin san komai, ki ka yi wani kasaƙe da kai".
Aliyu ya ce "A hakan ta san komai? Tana wannan gidadancin".
Usman ya ce "Kuma fa haka ne, to jeki na fasa gaya miki komai, duniya zata gaya miki, Allah ya shiryeki".
"Nuraini, Allah ya baka abun yi na aurara da kai, ina ga daga rumaisa kuma sai kai, tun baka wuce in da nake tunani ba" a guje Usman ya faÉ—a É—akinsu, dan sam bai san mama ta ji hirarsu ba.
***
Jabir ya din ga juya invitation É—in, sannan ya kalli Adam ya ce " da gaske Adam saura kwanaki a É—aura maka aure, amma ban sani ba?"
"Am sorry, abun ne ya zo cikin gahgawar gaske fiye da yadda na yi zato, sai haƙuri".
Jabir ya sake kallon invitation É—in, sannan ya ce "To ita kuma wacece, a ina take? Kamar na san sunan nan".
Adam ya ce "Zaka ganta very soon".
"Da jamil ya gaya mini maganar auren nan, na zaci da wasa yake yi, ashe da gaske ne, Allah sarki samha ina tausayin yarinyar nan sosai".
Adam ya ce "Please, don't raise that issue here, ku daina ganin laifina, ƙaddara ce ta zo a haka".
Jabir ya ce "Na yadda, ban ce wani abu ba, kawai dai ina jin tausayinta ne, sai dai na yi mamakin yadda har ka nemi aure, har ka samu ban sani ba, yaushe muka fara haka da kai".
"Jabir, this is an arranged marriage, ku yi mini uzuri".
Jabir ya ce "Arranged marriage, to Allah ya sanya alkhairi ya sa za ayi da mu".
"Amin, addu'arku nake buƙata dama, yanzu ka tashi mu je gidan mai girma turaki, zan kai masa nasa katin, da zai bawa mutanensa, da na jamil da gidan gaba ɗaya".
Jabir ya ce "Ok, ba damuwa bari mu yi salla tukuna"
Bayan sun idar da salla, suka tafi gidan turaki, kai tsaye sashinsa suka shiga, bayan sun tarar da babu kowa a falon.
Yayi murna sosai yayi addu'a da fatan alkhairi, sannan ya yi wa adam nasiha sosai mai shiga jiki. Sai dai kamar haÉ—in baki suka tarar da mama da Samha, har ma da zainab a falo.
Samha jikinta har tsuma yake da ta ga Adam, ga soyayya ga kuma kishi, ya gaida mama ta amsa masa sama-sama, ta saki jiki ta amsa gaisuwar Jabir.
Su Samha suka gaishe shi ya amsa, ya ajiye wa mama katuna, ya ce "Gashi nan, ammi ce ta ce in kawo miki, na taron wunin da za ta yi, na bawa mai girma turaki nasa".
Da ƙarfi Samha ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Adam wai dama da gaske ne, ta tabatta aure zaka yi?" Ya ɗaga kai ya kalli Samha da tsoro da kishi ya bayyana a fuskarta, ya jinjina mata kai a hankali cikin tausayawa.
"Shikenan, bakomai na gode " ta tashi ta bar falon. Jikin Adam ya yi sanyi, mama kawa jan tsaki ta yi ita ma, Zainab kuwa cewa ta yi Allah ya sanya alkhairi.
Æangaren ammi ma, da ta bawa mummy katin gayyata, masifa mummyn ta din ga yi, wai har ace adam zai yi aure, amma a kasa sakata a cikin lamarin bikin, sai dai ta zo a Æ´an gayya, saboda ba a mayar da ita a bakin komai ba.
A gidansu rumaisa ma, shirye shirye sun yi nisa. Mai sunan baba ya buga wani invitation ɗin na ɗaurin aure, aka rubuta sunan Adam sharif, ba tare da sanya cikakken sunan Adam ba. Ba ƙaramin mamaki ƴan unguwar su rumaisa suka yi ba, jin za ayi mata aure, wasu suka din ga surutu suna cewa sai ka ce a ƙauye, wasu kuma suka ce ta tabbata rumaisa ta yi cikin shege ne, ake son a liƙawa wani, kuma aka kasa gane wanene mijin, sai dai hatta wurin da aka rubuta za ayi bukukuwan a wurin ba ƙananan wuri ba ne, nan ma aka yi ta surutun ina suka samu kuɗin kama wannan wurare.
Zaman Gwaggo a gidan, ta din ga yi wa rumaisa faɗa, tare da nasiha a kan aure, da yadda za ta kula da miji, sai dai sam rumaisan ba ganewa take yi ba, yadda aka sakata a gaba ana sake koya mata girki ya fi komai ci mata rai, a ganinta ana hanata hutawa, girkin nan da karambani ta iya shi, dan tun shekara tara take gwadawa, tun mama tana hanata har ta haƙura ta rabu da ita.
Samha ta yi kuka kamar zata yi hauka, gaba É—aya ji take komai ya fita daga ranta, ko abincin kirki ba ta iya ci, sabuwar soyayyar adam ta dawo mata sabuwa fil, sai dai ta yi alwashin yadda ta zubar da hawayenta a kan sa karo na biyu, daga shi har matar ta sa sai sun É—anÉ—ana kuÉ—arsu.
Fauziyya ta din ga zigata a kan ta san duk yadda za ta yi, ta cuzgunawa matar da adam zai aura, har da ba ta tabbacin cewa, ta ji an ce auren haɗi ne ba son ta yake yi ba.
Ana gobe za a yi wa rumaisa jeren kaya, Adam ya É—auki Aliyu da Abdallah, zuwa gidan rumaisa, dan su gani daga nan ya basu mukulli.
Sai dai da suka je, Aliyu ya raina kayan da suka saya, da suna ta murna sun yi wa rumaisa kaya masu kyau da yawa, sai dai gidan babba ne sosai.
Sama da ƙasa ne, ƙasan akwai babban falo, da ɗakuna biyu, da kitchen da store, saman bene kuma falo biyu, bedroom uku, da kitchen da dining, kowane ɗaki da toilet.
Gidan ya tsaru yayi kyau, dan an kashe kuÉ—i wurin yin sa sosai.
Aliyu suka yi ta santin gida, suna yi wa Adam godiya. Sai dai tun da suka koma gida suka sanar da mama, gidan yafi ƙarfin abun da za a kai, jikinta yayi sanyi, dan ba dan kar ta nuna halin ƙaranta ba, cewa za ta yi idan da ƙarami a saka rumaisa a ciki.
Kaf Æ´an unguwa ba wanda mama ta ce su je yi wa rumaisa jere, Æ´an uwanta da Æ´an uwan mahaifinsu rumaisa, sai yayyenta ne suke je suka jera mata abun da ya samu a saman benen.
Gado biyu aka yi mata, dangin babansa suka yi mata ƴan waje guda ɗaya, yayyenta suka yi mata ƴan gida, masu matuƙar kyau.
Kitchen É—in ta ma babu laifi, a dai Æ´ar talaka, iyayen rumaisa sun taka rawar gani sosai da sosai, ga kujerunta da labulaye, ga dininga komai dai-dai gwargwado.
Ƴan uwa suka dawo, suka din ga santin gida, suna yi wa mama barka da arziki, rumaisa ta je gidan hutu.
Da daddare Adam ya je gida da shi da su ammi, suka ga jeren da aka yi, ammi ta jinjinawa ƙoƙarin iyayen rumaisa, ba ita ba shi kansa adam, abun ya bashi mamaki, aka jere mata akwatunanta goma sha biyar a bedroom.
Washegari Adam ya saka aka kawo abubuwan da babu, wanda basu ƙarasa ba.
Rumaisa ba ta yadda aurenta za ayi ba sai da satin biki ya kama, dama Aliyu sun shirya football match, a nan cikin unguwa.
Tun da rumaisa ta tabattar da idan aka yi auren barin gidan za ta yi, ta fara koke-koke tana fasa.
Ranar da za ayi bridal shower, daga gidan su adam, aka aiko da mota, aka ɗauki rumaisa zuwa gidan kwalliya, ita da ƙawayenta, babu ko sisinsu, aka yi musu kwalliya aka wuce da ita wurin biki.
Su Iman tuni suna can, sun sha kwalliya iman kamar balarabiya, da ita da wasu daga cikin famylinsu, da su ƙawayenta.