Sashe 110
Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mai martaba ya numfasa ya ce "Turaki yayi mana bayanin komai yadda al'amarin ya faru, sai dai bai kamata a ɓoyewa duniya gaskiyar abun da ya faru ba, maƙiya za su iya amfani da wannan damar, wurin cutar da kai, kamar yadda zancen ya fasu har wata gidan jarida suka wallafa, kuma ba zai wuce saboda ƙoƙarin da ake yi wa ƙasa ba, ya sanya miyagu ke ta ƙoƙarin bayyana laifinka, amma ayi haƙuri a daure, a cigaba da abun da ake yi kar a fasa Allah zai shiga lamarin"
Adam ya risuna ya ce "In sha Allah, muna fatan mai martaba ya cigaba da sanya mu a addu'a".
"Addu'a kullum cikin yi muku ake, kuma ko dan albarkacin mu babu wani abu da wani zai iya yi ya cutar da ku a kan gaskiya a ƙasar nan, a cigaba da ƙoƙari. Ita kuma 'yar mu Allah ya jiƙanta ya raya mini wannan kyakykyawan jikan nawa" yayi maganar yana shafa kan Sabir da yake hannunsa.
Mummy ta risuna tana "Allah ya taimaki mai martaba, mun gode da wannan karamci, Ubangiji Allah ya ƙara girma da ɗaukaka ya ƙara maka lafiya da nisan kwana"
"An gaisheki amaryar Galadima, , ƴar malam kin ƙi halin malam, mai martaba ya amsa kuma yana godiya" wani irin takaici ne ya kama mummy, jin yadda hadimin mai martaba ya amsa mata.
Aka karɓi jaririn aka miƙawa ammi, shamaki ya dubi ammi ya ce "Mai martaba ya bawa jariri gidaje guda biyu, ya bashi dawakai guda uku, sannan mai martaba ya yi umarnin a gina masallaci sadaka ga mahaifiyarsa. Sannan idan ya shekara uku a duniya mai martaba ya ce a kai shi umara"
Nan dogarai suka É—auka da "Godiya yake mai martaba, godiya yake Allah ya baka yawan nasara. Mai bayarwa da dama hagu ba ta sani ba"
Takawa ma risinawa yayi, suna yi wa mai martaba godiya.
Dogaransa suka kare shi ya tashi tsaye, har zai fita ya hangi iman a gefe a zaune.
Ya ce "Ahhh giwa, wannan buzuwar ƴar ta ki tana nan dama, ko da yake an ce mini bafullatana ce? ta daina zuwar mana, Allah ya jiƙan mai babban ɗaki, lokacin da muka kai mata ziyara a Saudiyya kan ta rasu, take tambayar ina wannan buzuwar ƴar ta giwar Galadima, a lokacin bamu sani ba ko kuna tare ko kin mayar da ita, mai babban ɗaki tana sonta"
Ammi ta yi murmushi ta ce "A'a muna tare mai martaba, ai tun da kuka saka baki a kan maganar nan, muke tare da ita"
"Allah sarki, baki fuskanci wani abu ba binta, wataƙila albarkacin yarinyar nan ne Allah ya kawo muku yaron nan cikin aminci, Ubangiji Allah ya yi jagora, Allah ya raya mana su baki ɗaya"
Ammi ta amsa da amin mai martaba.
Ba ƙaramin ƙulewa Mummy ta yi ba, yadda mai martaba ya mayar da hankali a kan yaran ammi, har da agola, amma ita ko kanta bai bi ba.
Mai martaba na tafiya, mummy ta fice fuuuuu ta bar sashin ita da su Fauziyya.
Bayan fitar su Ammi ta ce "Iman, mun yi laifi fa daina zuwa gidan mai martaba da ki ka yi, balle ki je gaishe shi, kin ga har ya magantu, Allah sarki mai babban ɗaki, lokacin kina ƙarama rigingimun da aka yi ta yi a kan ki, cewa ta yi sai na bata ke, na din ga kuka, ita tsaya mini a kan riƙonki".
Iman ta ce "Ammi tsoron zuwa gidan nake, fulanin yola ta hana ni zuwa, saboda yarima Hashim, kin san ai abun da aka yi mini su da Mummy"
Ammi ta ce "Na ji, kar ki yi kuka, jikina na bani mijinki mutum ne na gani na faÉ—a, karki damu autata"
Kunya ce ta kama Iman, Nusaiba ta ce "To ni fa, ko ita kaÉ—ai ake yi wa Addu'a"
"Ke dai nusaiba baki da girma sai na jikinki, kishi ki ke iman É—in?"
"To shikenan ma, ni na yi zuciya" Nusaiba ta tashi za ta fita, iman ta tashi ta bita da gudu tana yi mata dariya.
Ammi ta mayar da hankali a kan adam, da fuskarsa sam babu walwala, ta dube shi a tsanake ta ce "Mai martaba yake magana a kai ne, na ji yana cewa an yi amfani da gaskiyar abun da ya faru ana sukarka, meyafaru?"
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Wata gidan jarida ne suka yi posting a social media, cewar aisha ta mutu a hannun 'yan bindiga, ko kuma ni na kasheta na yi tsafi da gangar jikinta tun da ba aga gawarta ba ma"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, adam waye ya aikata wannan abun? Waye ya fitar da wannan zancen har da sharri haka?"
"Nima ban sani ba, ɗazu na ɗauko wayata a mota, kira daban-daban da saƙonni daga ƴan jaridu, suna buƙatar wai na ce wani abu a kan lamarin na kashe wayar ma gaba ɗaya".
Ammi ta dafe kai, ta rasa me ma za ta ce ko ta yi? Abubuwa kullum sake rikicewa suke yi.
Da la'asar yasir ba dan yana so ba, ya saka rumaisa a gaba zai kaita cikin gari, suna tafe yana mita, sai da suka je titi, sannan rumaisa ta ce "Dan Allah Yasir taimakona zaka yi"
"Taimakon me?"
"Dan Allah gidan su sabir zaka rakani na je na ganshi" wani mugun kallo ya yi mata ya ce "Ba zani ba, yaushe ki ka je ki ka ganshi? Ba zani ba ba nan muka yi da mama ba".
Riƙe hannunsa ruma ta yi ta fara kuka "Dan Allah yasir, wallahi na kasa bacci jiya, ba zamu daɗe ba dan girman Allah" ganin tana kuka ya sanya jikinsa yin sanyi.
"Kin yarda zaki wanke mini uniform, ki É—aukar mini jakata zuwa islamiyyar"
Da sauri ta ce "Eh wallahi na yarda"
"Shikenan mu je, saura idan buƙatar ki ta biya, ki yi mini rashin kunya".
"Ai ba ma zan yi ba"
Ya tarar musu abun hawa, suka hau suka tafi.
Suna tafe yasir yana danna waya, can ya ce "Kaii"
Ruma ta ce "Menene?"
"Wani labari na gani, ke dama baban sabir É—in nan shi ne Adam Sharif Galadima?"
"Wai wannan mai tona asirin mutanen, ba wani nan ba shi ne ba"
"Dan ubanki ƙarya zan yi miki?"
Rumaisa ta ce "Taɓ, ba shi bane ba, shi wannan yana abun arziki ne?"
Yasir ya ce "Ke ba wannan ba, wani labari aka wallafa wai, ya sayar da matarsa yayi tsafi da gangar jikinta, kuma jaririn da aka ce nasa ne, ƙarya ne rainawa mutane hankali ake"
Wani takaici ne ya turnuƙe rumaisa ta ce "In ji uban wa?"
'oho, wani gidan jarida ne suka wallafa"
Rumaisa ta ce "To rubuta musu ka ce ƙarya suke yi, wannan yaron nice nan na zo da shi"
Yasir ya ajiye wayar ya ce "A'a ba ruwana"
Rumaisa ta ce "Zan yi waya katsina a kawo mini wayata ni na rubuta, wannan ai sharri ne"
"Ke dalla rufewa mutane baki, zaki saka na ƙi rakakin wallahi"
Ta riƙe bakinta ta ce "Na daina in sha Allah"
Da haka suka ƙarasa gidan su Adam, rumaisa har da ɗan tsalle za su je ta ga Sabir.
Sai dai rumaisa ta yi ta mamakin ganin layin duk kashin dawakai, duk da abun mamaki bane, amma yanayin wurin ya nuna an yi wani sha'ani a wurin.
Yanzu babu wanda yake yi wa rumaisa shamaki da shiga sashen ammi, sai dai ta jira ta ce wurin ammi suka zo, ak shiga da su sashen Ammi.
Ko da ammi ta ga rumaisa sai da mamaki ya kama ta, shekaranjiya rumaisan ta zo, yau ma kuma gata.
Ammi ta ɓoye mamakinta, ta yi musu maraba, a nutse Yasir yake gaida Ammi, rumaisa kuwa ko gaisawar ba ayi ba, ta koma kusa da ammi ta ɗau Sabir.
Shi kansa takawa kallon rumaisan take, wannan nacin na ta ya fara yawa.
"Rumaisa ya mamanki"
"Tana lafiya ƙalau" ta ƙarasa maganar tana jujjuya sabir da yake bacci, wai sai ya tashi ya ganta.
Hakan kuwa aka yi sai da sabir ya buɗe ido yana miƙa, wasa rumaisa ta yi masa, ya geɓare baki ya fara murmushi.
"Laaa kun ga, yayi mini dariya, Yasir kalli yana yi mini dariya, ya gane ni, sabir ummanka ce rumaisa ka gane ni ko?"
Ammi ta ce "Ikon Allah, ko bacci bai fiye dariya ba, lallai ya ganeki, ke ya fara yi wa dariya".
"Kaii dama kewarsa ce ke damuna, na yi ta mafarkinsa, na cewa mama a rakani mandawari na duba Æ´ar uwarmu Hauwwaliya, na cewa yasir dan Allah ya rakoni na ga sabir É—ina"
Ammi kallonta take tana murmushi, tana jin daÉ—in yadda sabir ke yi wa rumaisa murmushi.
"Rumaisa baku gaisa da baban sabir ba" ruma ta É—ago ta kalleshi ta ce "Ni ma bai kulani ba, yauwwa ammi wai da gaske shi yake shayar da shi?"
"Shi wa?"
Rumaisa ta nuna Adam ta ce "Haka ya ce mini, wai idan aka bani sabir bani da abun da zan shayar da shi, na ce masa ana bashi madara, wai ba a bashi madara shine yake bashi abun da ake bawa jarirai wai ni idan an bani sabir me zan bashi?"
Paid book ne ₦500 via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143*
Dariya ce ta kuwa kufcewa ammi, ta ce "A'a rumaisa wannan maganar dai taku ce ba tawa ba"
Takawa dai ko kallonta bai yi ba, dan ya fuskanci yarinyar ba ta da kunya sam.
"Amma dai ammi ai ni ban taɓa ganin maza suna shayarwa ba, shi kuma ya ce mini haka, kuma dai na ga shima ƙirjinsa babu komai"
Ammi rasa amsar da za ta bawa rumaisa ta yi, can sai hankalin rumaisa ya É—auke daga kan maganar.
"Ammi" ta faÉ—a a hankali.
"Na'am umman sabir"
Rumaisa ta washe baki ta ce "Wayyo daɗi, ammi na ji daɗi, Allah ya amsa dukkanin buƙatinki, na fili da na ɓoye ya biya miki buƙatunki na alkhairi, na ji daɗi da ki ka kirani umman sabir"
"Amin rumaisa, in dai kin ji daɗi, ina son ki din ga saka baban sabir a addu'a, Allah ya biya masa buƙatunsa".
"To ammi, ai saboda ke zan yi masa addu'a ba dan halinsa ba"
Adam ya risuna ya ce "In sha Allah, muna fatan mai martaba ya cigaba da sanya mu a addu'a".
"Addu'a kullum cikin yi muku ake, kuma ko dan albarkacin mu babu wani abu da wani zai iya yi ya cutar da ku a kan gaskiya a ƙasar nan, a cigaba da ƙoƙari. Ita kuma 'yar mu Allah ya jiƙanta ya raya mini wannan kyakykyawan jikan nawa" yayi maganar yana shafa kan Sabir da yake hannunsa.
Mummy ta risuna tana "Allah ya taimaki mai martaba, mun gode da wannan karamci, Ubangiji Allah ya ƙara girma da ɗaukaka ya ƙara maka lafiya da nisan kwana"
"An gaisheki amaryar Galadima, , ƴar malam kin ƙi halin malam, mai martaba ya amsa kuma yana godiya" wani irin takaici ne ya kama mummy, jin yadda hadimin mai martaba ya amsa mata.
Aka karɓi jaririn aka miƙawa ammi, shamaki ya dubi ammi ya ce "Mai martaba ya bawa jariri gidaje guda biyu, ya bashi dawakai guda uku, sannan mai martaba ya yi umarnin a gina masallaci sadaka ga mahaifiyarsa. Sannan idan ya shekara uku a duniya mai martaba ya ce a kai shi umara"
Nan dogarai suka É—auka da "Godiya yake mai martaba, godiya yake Allah ya baka yawan nasara. Mai bayarwa da dama hagu ba ta sani ba"
Takawa ma risinawa yayi, suna yi wa mai martaba godiya.
Dogaransa suka kare shi ya tashi tsaye, har zai fita ya hangi iman a gefe a zaune.
Ya ce "Ahhh giwa, wannan buzuwar ƴar ta ki tana nan dama, ko da yake an ce mini bafullatana ce? ta daina zuwar mana, Allah ya jiƙan mai babban ɗaki, lokacin da muka kai mata ziyara a Saudiyya kan ta rasu, take tambayar ina wannan buzuwar ƴar ta giwar Galadima, a lokacin bamu sani ba ko kuna tare ko kin mayar da ita, mai babban ɗaki tana sonta"
Ammi ta yi murmushi ta ce "A'a muna tare mai martaba, ai tun da kuka saka baki a kan maganar nan, muke tare da ita"
"Allah sarki, baki fuskanci wani abu ba binta, wataƙila albarkacin yarinyar nan ne Allah ya kawo muku yaron nan cikin aminci, Ubangiji Allah ya yi jagora, Allah ya raya mana su baki ɗaya"
Ammi ta amsa da amin mai martaba.
Ba ƙaramin ƙulewa Mummy ta yi ba, yadda mai martaba ya mayar da hankali a kan yaran ammi, har da agola, amma ita ko kanta bai bi ba.
Mai martaba na tafiya, mummy ta fice fuuuuu ta bar sashin ita da su Fauziyya.
Bayan fitar su Ammi ta ce "Iman, mun yi laifi fa daina zuwa gidan mai martaba da ki ka yi, balle ki je gaishe shi, kin ga har ya magantu, Allah sarki mai babban ɗaki, lokacin kina ƙarama rigingimun da aka yi ta yi a kan ki, cewa ta yi sai na bata ke, na din ga kuka, ita tsaya mini a kan riƙonki".
Iman ta ce "Ammi tsoron zuwa gidan nake, fulanin yola ta hana ni zuwa, saboda yarima Hashim, kin san ai abun da aka yi mini su da Mummy"
Ammi ta ce "Na ji, kar ki yi kuka, jikina na bani mijinki mutum ne na gani na faÉ—a, karki damu autata"
Kunya ce ta kama Iman, Nusaiba ta ce "To ni fa, ko ita kaÉ—ai ake yi wa Addu'a"
"Ke dai nusaiba baki da girma sai na jikinki, kishi ki ke iman É—in?"
"To shikenan ma, ni na yi zuciya" Nusaiba ta tashi za ta fita, iman ta tashi ta bita da gudu tana yi mata dariya.
Ammi ta mayar da hankali a kan adam, da fuskarsa sam babu walwala, ta dube shi a tsanake ta ce "Mai martaba yake magana a kai ne, na ji yana cewa an yi amfani da gaskiyar abun da ya faru ana sukarka, meyafaru?"
Yayi ajiyar zuciya ya ce "Wata gidan jarida ne suka yi posting a social media, cewar aisha ta mutu a hannun 'yan bindiga, ko kuma ni na kasheta na yi tsafi da gangar jikinta tun da ba aga gawarta ba ma"
"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, adam waye ya aikata wannan abun? Waye ya fitar da wannan zancen har da sharri haka?"
"Nima ban sani ba, ɗazu na ɗauko wayata a mota, kira daban-daban da saƙonni daga ƴan jaridu, suna buƙatar wai na ce wani abu a kan lamarin na kashe wayar ma gaba ɗaya".
Ammi ta dafe kai, ta rasa me ma za ta ce ko ta yi? Abubuwa kullum sake rikicewa suke yi.
Da la'asar yasir ba dan yana so ba, ya saka rumaisa a gaba zai kaita cikin gari, suna tafe yana mita, sai da suka je titi, sannan rumaisa ta ce "Dan Allah Yasir taimakona zaka yi"
"Taimakon me?"
"Dan Allah gidan su sabir zaka rakani na je na ganshi" wani mugun kallo ya yi mata ya ce "Ba zani ba, yaushe ki ka je ki ka ganshi? Ba zani ba ba nan muka yi da mama ba".
Riƙe hannunsa ruma ta yi ta fara kuka "Dan Allah yasir, wallahi na kasa bacci jiya, ba zamu daɗe ba dan girman Allah" ganin tana kuka ya sanya jikinsa yin sanyi.
"Kin yarda zaki wanke mini uniform, ki É—aukar mini jakata zuwa islamiyyar"
Da sauri ta ce "Eh wallahi na yarda"
"Shikenan mu je, saura idan buƙatar ki ta biya, ki yi mini rashin kunya".
"Ai ba ma zan yi ba"
Ya tarar musu abun hawa, suka hau suka tafi.
Suna tafe yasir yana danna waya, can ya ce "Kaii"
Ruma ta ce "Menene?"
"Wani labari na gani, ke dama baban sabir É—in nan shi ne Adam Sharif Galadima?"
"Wai wannan mai tona asirin mutanen, ba wani nan ba shi ne ba"
"Dan ubanki ƙarya zan yi miki?"
Rumaisa ta ce "Taɓ, ba shi bane ba, shi wannan yana abun arziki ne?"
Yasir ya ce "Ke ba wannan ba, wani labari aka wallafa wai, ya sayar da matarsa yayi tsafi da gangar jikinta, kuma jaririn da aka ce nasa ne, ƙarya ne rainawa mutane hankali ake"
Wani takaici ne ya turnuƙe rumaisa ta ce "In ji uban wa?"
'oho, wani gidan jarida ne suka wallafa"
Rumaisa ta ce "To rubuta musu ka ce ƙarya suke yi, wannan yaron nice nan na zo da shi"
Yasir ya ajiye wayar ya ce "A'a ba ruwana"
Rumaisa ta ce "Zan yi waya katsina a kawo mini wayata ni na rubuta, wannan ai sharri ne"
"Ke dalla rufewa mutane baki, zaki saka na ƙi rakakin wallahi"
Ta riƙe bakinta ta ce "Na daina in sha Allah"
Da haka suka ƙarasa gidan su Adam, rumaisa har da ɗan tsalle za su je ta ga Sabir.
Sai dai rumaisa ta yi ta mamakin ganin layin duk kashin dawakai, duk da abun mamaki bane, amma yanayin wurin ya nuna an yi wani sha'ani a wurin.
Yanzu babu wanda yake yi wa rumaisa shamaki da shiga sashen ammi, sai dai ta jira ta ce wurin ammi suka zo, ak shiga da su sashen Ammi.
Ko da ammi ta ga rumaisa sai da mamaki ya kama ta, shekaranjiya rumaisan ta zo, yau ma kuma gata.
Ammi ta ɓoye mamakinta, ta yi musu maraba, a nutse Yasir yake gaida Ammi, rumaisa kuwa ko gaisawar ba ayi ba, ta koma kusa da ammi ta ɗau Sabir.
Shi kansa takawa kallon rumaisan take, wannan nacin na ta ya fara yawa.
"Rumaisa ya mamanki"
"Tana lafiya ƙalau" ta ƙarasa maganar tana jujjuya sabir da yake bacci, wai sai ya tashi ya ganta.
Hakan kuwa aka yi sai da sabir ya buɗe ido yana miƙa, wasa rumaisa ta yi masa, ya geɓare baki ya fara murmushi.
"Laaa kun ga, yayi mini dariya, Yasir kalli yana yi mini dariya, ya gane ni, sabir ummanka ce rumaisa ka gane ni ko?"
Ammi ta ce "Ikon Allah, ko bacci bai fiye dariya ba, lallai ya ganeki, ke ya fara yi wa dariya".
"Kaii dama kewarsa ce ke damuna, na yi ta mafarkinsa, na cewa mama a rakani mandawari na duba Æ´ar uwarmu Hauwwaliya, na cewa yasir dan Allah ya rakoni na ga sabir É—ina"
Ammi kallonta take tana murmushi, tana jin daÉ—in yadda sabir ke yi wa rumaisa murmushi.
"Rumaisa baku gaisa da baban sabir ba" ruma ta É—ago ta kalleshi ta ce "Ni ma bai kulani ba, yauwwa ammi wai da gaske shi yake shayar da shi?"
"Shi wa?"
Rumaisa ta nuna Adam ta ce "Haka ya ce mini, wai idan aka bani sabir bani da abun da zan shayar da shi, na ce masa ana bashi madara, wai ba a bashi madara shine yake bashi abun da ake bawa jarirai wai ni idan an bani sabir me zan bashi?"
Paid book ne ₦500 via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143*
Dariya ce ta kuwa kufcewa ammi, ta ce "A'a rumaisa wannan maganar dai taku ce ba tawa ba"
Takawa dai ko kallonta bai yi ba, dan ya fuskanci yarinyar ba ta da kunya sam.
"Amma dai ammi ai ni ban taɓa ganin maza suna shayarwa ba, shi kuma ya ce mini haka, kuma dai na ga shima ƙirjinsa babu komai"
Ammi rasa amsar da za ta bawa rumaisa ta yi, can sai hankalin rumaisa ya É—auke daga kan maganar.
"Ammi" ta faÉ—a a hankali.
"Na'am umman sabir"
Rumaisa ta washe baki ta ce "Wayyo daɗi, ammi na ji daɗi, Allah ya amsa dukkanin buƙatinki, na fili da na ɓoye ya biya miki buƙatunki na alkhairi, na ji daɗi da ki ka kirani umman sabir"
"Amin rumaisa, in dai kin ji daɗi, ina son ki din ga saka baban sabir a addu'a, Allah ya biya masa buƙatunsa".
"To ammi, ai saboda ke zan yi masa addu'a ba dan halinsa ba"