Sashe 103
Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Allah ya yi mata rahama, Sannan a cigaba da haƙuri duk mai rai mamaci ne". Ya jinjinawa ammi kai, tare da zura hannunsa a aljihunsa, Saboda vibrating da wayarsa ta fara.
Bai san mai lambar ba, amma ya É—aga tare da yin sallama.
Aliyu amsa sannan ya ce "Aliyu ne yayan rumaisa, mun zo mu yi maka gaisuwa ne, mun shigo cikin gidan bamu san ina zamu bi ba, a wurin bashir na karɓi lambarka".
Adam ya ce "Ok babu damuwa, bari na zo gani nan" ya miƙe ya ce "Ammi ina zuwa".
Rumaisa kuwa riƙe ƙugu tayi tana ƙarewa harabar gidan su takawa kallo, ga motoci gefe guda kuma ga burgar dawakai, ko ina sai manyan bishiyu da ƙanana, sai kalle-kalle take kamar 'yar ƙauye, ga dogarai suna ta shiga suna fita, suna kaiwa da komowa a harabar.
Rumaisa ce ta fara hango adam ya nufo su, ya rame sai uban wuya, da dogon hanci, idon nan nasa jawur ya ƙaraso in da suke yana yi musu sannu da zuwa.
Risunawa ya yi ya ce "Mama sannu da zuwa, ya gida?".
Cikin kulawa mama ta ce "Lafiya lau, ya ƙarin haƙuri?"
"Alhamdilillah"
Haka ya bi su usman duk suka gaisa, amma bai kula ruma ba, ita ma ba ya kula shi ba.
Ya ce "mu shiga daga ciki"
Rumaisa dama tun da ya zo yana fara magana, ta wani juya ƙeya, irin ba ta ma san yana wurin ba, sai dai kamar yadda ta ga ya rame, haka shima ya ga tayi rama, ta fi cikowa kwanaki uku baya da aka sallameta daga asibiti.
Yayi musu jagora zuwa ciki, rumaisa ta gwalala ido, ganin kayan alatun da ke falon ammi, ya wuce da su babban falon, ya ratsa da su zuwa falon ammi, wanda bai kai wanda suka baro ba.
Yayi musu iznin su zauna, ya kira ɗaya daga cikin barorin ammi, ya ce a karɓi su rumaisa. Ya ce "Bari na yi wa ammin magana".
"To ina É—ana yake?" Ta yi maganar ba tare da ita kanta ta yi niyyar maganar ba.
Banza yayi mata bai kulata ba, sai da ya juya zai bar falon, sannan ya ce "Na kai shi koyo yadda ake gaida mutane"
Aliyu ya ce "Ai da abun duka ka samu ka zaneta wallahi, mara kunya kawai".
Adam yana barin falon, rumaisa ta miƙe tsaye, ta sake zama a kan kujerar ta ce "Wayyo laushi, Innalillahi kujerar nan ta ji katifa yasin, kujerar masu kuɗi daban take, har na tuna wata kujera da na gani a gidansu wata 'yar ajinmu, kujerar nan duk ƙashi, sai soso duk a waje, na ƙusa ta kusa tsarge mini mazaunai"
Usman ne ya talle mata ƙeya ya ce "Gaisuwa fa muka zo, ki ke yi mana surtu, shashasha" shiru ta yi ta sunkuyar da kanta ƙasa kamar ta Allah.
Mama ta ce "Rumaisa yaushe ki canza halaye zuwa na banza ne? Dama haka na koya miki rashin gaida mutane ko?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a ki yi haƙuri"
Aka zo aka din ga jere musu kayan abinci kala-kala, da na sha, ita dai rumaisa burinta ta ga Sabir.
Adam ya je ya tarar da ammi ta aiki su Nusaiba, daga ita sai sabir a ɗakin, ya ce "Ammi kin yi baƙi".
Ammi ta ce "Suwaye, na ce duk wanda yayi gaisuwa ya tafi ina son hutawa ne".
Rasa mai zai cewa ammi yayi, dan ko sunan rumaisa ba ya son kamawa, ya ce "Yarinyar nan ce, da mamanta da yayyenta suka zo yi mana gaisuwa".
Cikin rashin fahimta ammi ta ce "Wace yarinyar kenan?"
"Wannan yarinyar da ta zo da Sabir" Sabir É—in ma da ya faÉ—a ji yake kamar ya kwafsa, kasancewar rumaisa ce ta sanya masa sunan.
Cikin fara'a ammi ta miƙe tana faɗin Allah sarki.
Adam ya karɓi Sabir a hannun ammi, da niyyar ya gwanyawa rumaisa, suka fito falon.
Ko ammi ba ta kalla ba, ta miƙe tsaye tana jiran Adam ya ƙaraso ta karɓi Sabir, amma ya canza hanya ya yi wani wurin. Ai ba su ankara ba rumaisa ta bi bayansa da gudu tana "Ka tsaya in ɗauke shi, ka zo ka bani ɗana".
Ayshercool.
paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, masu buƙatar vip ko special kuma, suna iya garzayawa arewabooks ku searching sunan littafin*
Da fari bayan bayyanar rumaisa, mama ta zaci ruman nutsuwa ta ɗan ratsata, amma ina sai ta ga akasin abun da ta yi tsammani, halinta yana nan yadda yake, Aliyu na ƙwala mata kira amma ta rufawa takawa baya.
Murmushi ammi ta yi ta ce "Ƙyaleta, shi ma dai neman magana ne ya sanya ya ɗauke shi zai fice, da na san haka zai yi da ban bashi sabir ɗin ba".
Usman ya ce "Ai gara da ya hanata, ƙin gaishe shi ta yi, sai tambayarsa ina ɗan ta dan ba ta da kunya"
Mama ta girgiza kai ta ce "Rumaisa ai sai fatan Allah ya shirya. Hajiya ina wuni ina gajiya?" Ta yi maganar tana mayar da kallonta ga Ammi
Ammi ta ce "Lafiya lau Alhamdilillah, ya gida ya iyali?".
"Kowa lafiya ƙalau, ya kuma ƙarin haƙurinmu".
"Haƙuri mun gode Allah"
Mama ta ce "To Allah ya sa ta huta, Allah ya rahamsheta"
Ammi ta amsa da "amin ya rabb, ya jikin rumaisa kuwa ina fatan ta wartsake gaba É—aya"
Mama ta ce "Jikinta dai da sauƙi, amma taƙi sakin jiki kullum kuka ita sabir, yau ne ma ta ɗan saki jiki har da hira da ta ji an ce za a zo gaisuwa".
Ammi ta ce "Allah sarki rumaisa, Allah dai ya bata haƙuri"
Hira suka ɗan shiga taɓawa da mama, har ammi take ɗan gutsura mata kaɗan daga cikin halin da take ciki, na dangane da ƙalubalen rasuwar aisha, daga ita har adam, haka nan ammi take jin yadda da mama a cikin ranta.
Rumaisa kuwa bin adam ta cigaba da yi, tana cewa ya bata É—an ta, amma yayi banza da ita ya cigaba da tafiya.
"Wallahi idan ba ka tsaya ka bani ɗana ba, sai na yi maka ihu na tara maka mutane" bai ko tsaya ba balle ta sanya ran zai kulata. Kan ta ankara tuni ya sulale ta wata ƙofar ta neme shi ta rasa.
Komawa ta yi falon da ta baro su mama tana kuka.
Duk suka bita da ido, ammi ta ce "Rumaisa lafiya? Menene?"
Cikin kuka ta ce "Ba guduwa yayi da sabir ɗin ba, ina ta roƙonsa yaƙi kulani, ya bi ta wata ƙofa ya gudu"
Ammi ta ce "Subhanallah, takawa fa wasu lokutan ba shi da girma sai na jikinsa, bari kan ku tafi zai zo har nan ya sameni"
Mama ta ce "Rabu da ita, yanzun nan zamu tafi, can gida ina ta baƙi, yan dubiya da jaje"
Ammi ta ce "Allah sarki, na zata zaku wunar mini, baku ci komai ba fa"
"Wallahi karki damu"
Rumaisa ta ce "Dan Allah mama mu É—an jira ko zai dawo ".
Aliyu ya ce "Ba in da zai dawo, ba dai ke fitsara ba, gara ayi maganinki ai"
Ammi ta yi murmushi ta ce "Yauwwa, dan Allah wata alfarma nake nema, idan Allah ya kaimu jibi, ina son a kawo mini rumaisa, za'a kaita wurin turaki, mahaifin aisha, abun da zai hana a kaita yanzu, haryanzu yana karɓar gaisuwa kuma yana cikin alhini, amma ya buƙaci ya ganta, ko zuwa jibi ne in Allah ya kaimu sai ko turowa na yi a ɗaukota".
Mama ta ce "Yayyenta za su rakota in Allah ya yarda, babu wata damuwa Allah ya yi mata rahama, ai ko bai nemeta ba ya ci taje ta yi masa gaisuwa "
Ammi ta yi ta yi wa mama godiya, da kanta ta raka su har harabar gidan, rumaisa kuwa sai kuka take yi, ammin tana bata haƙuri, tare da yi mata alwashin hukunta adam.
Ko da suka taho hanya, mita ta cigaba da yi tare da cewa da ta san ba zata ga Sabir ba da wallahi ba zata bi su ba, dan ita saboda sabir ta je.
Su Aliyu ne suka tanka mata, mama kuwa shiru ta yi mata, sai da suka je gida, ta dirar mata da faɗa, faɗan da tun da ta kuɓuta daga hannun yan ta'adda ba ta yi mata irinsa ba, sakamakon rashin hankalin da ta yi wa takawa yau.
Takawa kuwa ya kai awanni uku bai dawo ba, har wayarsa ammi ta din ga kira, yana É—akinsa ya kulle kansa da shi da sabir, sai da ya daidaici su ruma sun tafi, sannan ya mayarwa da su iman sabir, ya fice ba tare da ya bari ya haÉ—u da ammi ba dan kar ta yi masa faÉ—a a kan abun da ya yi.
Yana fita gidansa ya wuce, ya je ya kulle kansa, ya kashe wayoyinsa, dan baya ko son jin motsin wani a kusa da shi.
Rainin hankalin da rumaisa ta yi masa ne ya faɗo masa a rai, taƙi gaishe shi, amma ta biyo shi tana kiran ya bata ɗan ta, wani gajeren tsaki yayi ya nemi wuri ya kwanta tare da lumshe idonsa.
Da magariba mama take bawa su Abdallah labarin yadda suka yi a gidan su takawa da suka je gaisuwa, da abun da rumaisa ta yi, suka yi mata caa suna yi mata faɗa, ita gaba ɗaya faɗan da suka yi mata bai dameta ba kamar takaicin rashin ganin sabir, ji take da zata ga Adam ta shaƙe shi ta huta.
Mai sunan baba da yake jin hirar ta su bai ce komai ba, ya kalli in da rumaisa take ya ga sam hankalinta baya kan faÉ—an da suke yi mata, baya raba É—ayan biyu ya san ba zai wuce tunanin Sabir take ba.
Gyaran muryar da ya yi ne ya sanya su waiwayowa suna kallonsa.
Cikin kakkausar muryarsa ya ce wa rumaisa "Ki nemo uniform ɗin ki kafin ranar monday in Allah ya kaimu, zan je mu yi magana da shugaban makarantar ku zaki koma makaranta" turus rumaisa ta yi, dan har ga Allah ita ba ta ƙaunar makaranta a ganinta kawai salon uzzurawa rayuwarta ne.
Bai san mai lambar ba, amma ya É—aga tare da yin sallama.
Aliyu amsa sannan ya ce "Aliyu ne yayan rumaisa, mun zo mu yi maka gaisuwa ne, mun shigo cikin gidan bamu san ina zamu bi ba, a wurin bashir na karɓi lambarka".
Adam ya ce "Ok babu damuwa, bari na zo gani nan" ya miƙe ya ce "Ammi ina zuwa".
Rumaisa kuwa riƙe ƙugu tayi tana ƙarewa harabar gidan su takawa kallo, ga motoci gefe guda kuma ga burgar dawakai, ko ina sai manyan bishiyu da ƙanana, sai kalle-kalle take kamar 'yar ƙauye, ga dogarai suna ta shiga suna fita, suna kaiwa da komowa a harabar.
Rumaisa ce ta fara hango adam ya nufo su, ya rame sai uban wuya, da dogon hanci, idon nan nasa jawur ya ƙaraso in da suke yana yi musu sannu da zuwa.
Risunawa ya yi ya ce "Mama sannu da zuwa, ya gida?".
Cikin kulawa mama ta ce "Lafiya lau, ya ƙarin haƙuri?"
"Alhamdilillah"
Haka ya bi su usman duk suka gaisa, amma bai kula ruma ba, ita ma ba ya kula shi ba.
Ya ce "mu shiga daga ciki"
Rumaisa dama tun da ya zo yana fara magana, ta wani juya ƙeya, irin ba ta ma san yana wurin ba, sai dai kamar yadda ta ga ya rame, haka shima ya ga tayi rama, ta fi cikowa kwanaki uku baya da aka sallameta daga asibiti.
Yayi musu jagora zuwa ciki, rumaisa ta gwalala ido, ganin kayan alatun da ke falon ammi, ya wuce da su babban falon, ya ratsa da su zuwa falon ammi, wanda bai kai wanda suka baro ba.
Yayi musu iznin su zauna, ya kira ɗaya daga cikin barorin ammi, ya ce a karɓi su rumaisa. Ya ce "Bari na yi wa ammin magana".
"To ina É—ana yake?" Ta yi maganar ba tare da ita kanta ta yi niyyar maganar ba.
Banza yayi mata bai kulata ba, sai da ya juya zai bar falon, sannan ya ce "Na kai shi koyo yadda ake gaida mutane"
Aliyu ya ce "Ai da abun duka ka samu ka zaneta wallahi, mara kunya kawai".
Adam yana barin falon, rumaisa ta miƙe tsaye, ta sake zama a kan kujerar ta ce "Wayyo laushi, Innalillahi kujerar nan ta ji katifa yasin, kujerar masu kuɗi daban take, har na tuna wata kujera da na gani a gidansu wata 'yar ajinmu, kujerar nan duk ƙashi, sai soso duk a waje, na ƙusa ta kusa tsarge mini mazaunai"
Usman ne ya talle mata ƙeya ya ce "Gaisuwa fa muka zo, ki ke yi mana surtu, shashasha" shiru ta yi ta sunkuyar da kanta ƙasa kamar ta Allah.
Mama ta ce "Rumaisa yaushe ki canza halaye zuwa na banza ne? Dama haka na koya miki rashin gaida mutane ko?"
Ta girgiza kai ta ce "A'a ki yi haƙuri"
Aka zo aka din ga jere musu kayan abinci kala-kala, da na sha, ita dai rumaisa burinta ta ga Sabir.
Adam ya je ya tarar da ammi ta aiki su Nusaiba, daga ita sai sabir a ɗakin, ya ce "Ammi kin yi baƙi".
Ammi ta ce "Suwaye, na ce duk wanda yayi gaisuwa ya tafi ina son hutawa ne".
Rasa mai zai cewa ammi yayi, dan ko sunan rumaisa ba ya son kamawa, ya ce "Yarinyar nan ce, da mamanta da yayyenta suka zo yi mana gaisuwa".
Cikin rashin fahimta ammi ta ce "Wace yarinyar kenan?"
"Wannan yarinyar da ta zo da Sabir" Sabir É—in ma da ya faÉ—a ji yake kamar ya kwafsa, kasancewar rumaisa ce ta sanya masa sunan.
Cikin fara'a ammi ta miƙe tana faɗin Allah sarki.
Adam ya karɓi Sabir a hannun ammi, da niyyar ya gwanyawa rumaisa, suka fito falon.
Ko ammi ba ta kalla ba, ta miƙe tsaye tana jiran Adam ya ƙaraso ta karɓi Sabir, amma ya canza hanya ya yi wani wurin. Ai ba su ankara ba rumaisa ta bi bayansa da gudu tana "Ka tsaya in ɗauke shi, ka zo ka bani ɗana".
Ayshercool.
paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, masu buƙatar vip ko special kuma, suna iya garzayawa arewabooks ku searching sunan littafin*
Da fari bayan bayyanar rumaisa, mama ta zaci ruman nutsuwa ta ɗan ratsata, amma ina sai ta ga akasin abun da ta yi tsammani, halinta yana nan yadda yake, Aliyu na ƙwala mata kira amma ta rufawa takawa baya.
Murmushi ammi ta yi ta ce "Ƙyaleta, shi ma dai neman magana ne ya sanya ya ɗauke shi zai fice, da na san haka zai yi da ban bashi sabir ɗin ba".
Usman ya ce "Ai gara da ya hanata, ƙin gaishe shi ta yi, sai tambayarsa ina ɗan ta dan ba ta da kunya"
Mama ta girgiza kai ta ce "Rumaisa ai sai fatan Allah ya shirya. Hajiya ina wuni ina gajiya?" Ta yi maganar tana mayar da kallonta ga Ammi
Ammi ta ce "Lafiya lau Alhamdilillah, ya gida ya iyali?".
"Kowa lafiya ƙalau, ya kuma ƙarin haƙurinmu".
"Haƙuri mun gode Allah"
Mama ta ce "To Allah ya sa ta huta, Allah ya rahamsheta"
Ammi ta amsa da "amin ya rabb, ya jikin rumaisa kuwa ina fatan ta wartsake gaba É—aya"
Mama ta ce "Jikinta dai da sauƙi, amma taƙi sakin jiki kullum kuka ita sabir, yau ne ma ta ɗan saki jiki har da hira da ta ji an ce za a zo gaisuwa".
Ammi ta ce "Allah sarki rumaisa, Allah dai ya bata haƙuri"
Hira suka ɗan shiga taɓawa da mama, har ammi take ɗan gutsura mata kaɗan daga cikin halin da take ciki, na dangane da ƙalubalen rasuwar aisha, daga ita har adam, haka nan ammi take jin yadda da mama a cikin ranta.
Rumaisa kuwa bin adam ta cigaba da yi, tana cewa ya bata É—an ta, amma yayi banza da ita ya cigaba da tafiya.
"Wallahi idan ba ka tsaya ka bani ɗana ba, sai na yi maka ihu na tara maka mutane" bai ko tsaya ba balle ta sanya ran zai kulata. Kan ta ankara tuni ya sulale ta wata ƙofar ta neme shi ta rasa.
Komawa ta yi falon da ta baro su mama tana kuka.
Duk suka bita da ido, ammi ta ce "Rumaisa lafiya? Menene?"
Cikin kuka ta ce "Ba guduwa yayi da sabir ɗin ba, ina ta roƙonsa yaƙi kulani, ya bi ta wata ƙofa ya gudu"
Ammi ta ce "Subhanallah, takawa fa wasu lokutan ba shi da girma sai na jikinsa, bari kan ku tafi zai zo har nan ya sameni"
Mama ta ce "Rabu da ita, yanzun nan zamu tafi, can gida ina ta baƙi, yan dubiya da jaje"
Ammi ta ce "Allah sarki, na zata zaku wunar mini, baku ci komai ba fa"
"Wallahi karki damu"
Rumaisa ta ce "Dan Allah mama mu É—an jira ko zai dawo ".
Aliyu ya ce "Ba in da zai dawo, ba dai ke fitsara ba, gara ayi maganinki ai"
Ammi ta yi murmushi ta ce "Yauwwa, dan Allah wata alfarma nake nema, idan Allah ya kaimu jibi, ina son a kawo mini rumaisa, za'a kaita wurin turaki, mahaifin aisha, abun da zai hana a kaita yanzu, haryanzu yana karɓar gaisuwa kuma yana cikin alhini, amma ya buƙaci ya ganta, ko zuwa jibi ne in Allah ya kaimu sai ko turowa na yi a ɗaukota".
Mama ta ce "Yayyenta za su rakota in Allah ya yarda, babu wata damuwa Allah ya yi mata rahama, ai ko bai nemeta ba ya ci taje ta yi masa gaisuwa "
Ammi ta yi ta yi wa mama godiya, da kanta ta raka su har harabar gidan, rumaisa kuwa sai kuka take yi, ammin tana bata haƙuri, tare da yi mata alwashin hukunta adam.
Ko da suka taho hanya, mita ta cigaba da yi tare da cewa da ta san ba zata ga Sabir ba da wallahi ba zata bi su ba, dan ita saboda sabir ta je.
Su Aliyu ne suka tanka mata, mama kuwa shiru ta yi mata, sai da suka je gida, ta dirar mata da faɗa, faɗan da tun da ta kuɓuta daga hannun yan ta'adda ba ta yi mata irinsa ba, sakamakon rashin hankalin da ta yi wa takawa yau.
Takawa kuwa ya kai awanni uku bai dawo ba, har wayarsa ammi ta din ga kira, yana É—akinsa ya kulle kansa da shi da sabir, sai da ya daidaici su ruma sun tafi, sannan ya mayarwa da su iman sabir, ya fice ba tare da ya bari ya haÉ—u da ammi ba dan kar ta yi masa faÉ—a a kan abun da ya yi.
Yana fita gidansa ya wuce, ya je ya kulle kansa, ya kashe wayoyinsa, dan baya ko son jin motsin wani a kusa da shi.
Rainin hankalin da rumaisa ta yi masa ne ya faɗo masa a rai, taƙi gaishe shi, amma ta biyo shi tana kiran ya bata ɗan ta, wani gajeren tsaki yayi ya nemi wuri ya kwanta tare da lumshe idonsa.
Da magariba mama take bawa su Abdallah labarin yadda suka yi a gidan su takawa da suka je gaisuwa, da abun da rumaisa ta yi, suka yi mata caa suna yi mata faɗa, ita gaba ɗaya faɗan da suka yi mata bai dameta ba kamar takaicin rashin ganin sabir, ji take da zata ga Adam ta shaƙe shi ta huta.
Mai sunan baba da yake jin hirar ta su bai ce komai ba, ya kalli in da rumaisa take ya ga sam hankalinta baya kan faÉ—an da suke yi mata, baya raba É—ayan biyu ya san ba zai wuce tunanin Sabir take ba.
Gyaran muryar da ya yi ne ya sanya su waiwayowa suna kallonsa.
Cikin kakkausar muryarsa ya ce wa rumaisa "Ki nemo uniform ɗin ki kafin ranar monday in Allah ya kaimu, zan je mu yi magana da shugaban makarantar ku zaki koma makaranta" turus rumaisa ta yi, dan har ga Allah ita ba ta ƙaunar makaranta a ganinta kawai salon uzzurawa rayuwarta ne.