← Book details Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 174

Sashe 34

Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Aliyu ya yiwa mama bayanin abin da ruma ta aikata, da yadda suka yi, zuwansu police station yanzu.

"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Allah ka shiga lamarina, Allah ka dubeni a kan halin wannan yarinyar".

"Mama dan Allah ki yi haƙuri ba zan sake ba, ita ta fara tsokanata na rama, ban san zata karye ba wallahi"

Mama ta dube ta ta ce "In dai kece, ba zaki canza hali ba, yanzu ruma har ta kai ki ga zuwa police station ruma, kaf yaran nan yayyenki babu wanda ya taɓa zuwa wurin 'yan sanda, sai ke ruma ko? Allah ya yi miki magani, ki je ki yi ta yi kar ki fasa" mama na gama maganar ta shige ɗaki ta bar ruma a wurin.

Ruma ta kalli Aliyu ta ce "Kai baka da rufin asiri, wallahi da yaya usy ne zai rufa mini asiri, amma na fuskanci da kai da Yasir, da Huzaifa baku taɓa rufa mini asiri ba, ƙiris ku ke jira .....

"Dalla rufe mini baki, tun ban daki kuɗina a jikinki ba, dubu gomar nan ta tsaye mini, ni Wallahi da ma ƙyaleki na yi su yi miki duk abin da suka ga dama" ɓata fuska ta yi, ta bi bayan mama, sai dai mama sam taƙi kulata, wanda hakan ba ƙaramin tayar wa ruma hankali yake ba.

Wunin yau gaba É—aya aka rasa mai saurara ruma, duk wanda ta yiwa magana sai ya hantareta gaba É—aya haushin abin da ta yi suke ji.

"Hmm huzaifa ni fa Allah ne ya taimake ni, da matar cewa ta yi sai ta dakeni, ka ganta kuwa, ƙatuwace sosai da sosai fa, a kan benci ta zauna, kaga hannun ta a cure da nama, idan ta dakeni ai ji zan kamar an buga mini guduma"

Usman ya ce "Sai na zubar da haƙoranki, ba zaki nutsu ba ko?, ki ke cigaba sa kwatanta yadda take, ina ma Alin ya bar ta ci ubanki, ke ban da rashin kan gado, kawai ki je ki karya 'yar mutane saboda tsabar wauta ta yi miki yawa, sai ka ce wata rainon gaɓa-gaɓa?"

Aliyu ya ce "Kai ba ka san abin takaicin ba ma, har da wani cewa ai aljanunta ne suka tashi, ba a hayyacinta ta daki yarinyar ba, tsabar cin kai"

Mama ta ce "Ba ku ne ku ke zigata ta É—auko magana, ku ka ce kun tsaya mata, dole ta yi abin da ta ga dama ai, kuma daga yau duk wasu tashoshi na wrestling a gidan nan sai an sauke mini su, an daina kallon sa a gidan nan, kai kallon ma sai an daina"

Ruma ta waro ido ta ce "Mama, shikenan sai na daina ganin saurayina na wrestling"

Usman ya ce "Au ke har wani saurayi ne da ke a wrestling É—in?"

"Eh mana, ba ka san shi bane, Huzaifa ya ma sunan sa, É—an tuna mini, idan na ganshi har wani daÉ—i nake ji".

Huzaifa ya ce "Ke ki ka san shi ni ban san shi ba"

Yasir yayi tsaki ya ce "Wallahi Mama mi bamu go ahead, mu yi wa yarinyar nan ruƙiyya ni da Huzaifa, mu samo tsumangiya in cuɗa mata jikinta in haɗa da ayar Allah wallahi dolen aljanun na ta su magantu"

"Wallahi ni ba ni da aljanu sai raina ya ɓaci, kuma na sha tabara da ayatul kursiyyu, na fi ƙarfin aljani da makiri ko tsunburbura na fi ƙarfinta"

"Ke dalla ware, ai ke kin fi tsunburburar ma rashin ji" suka din ga caccakar ruka kamar zasu daketa.
Ita damuwarta a kan mai sunana Baba ne, hukuncin da zai É—auka a kan ta, na abin da ta aikata, sai ta ji bai ce komai ba ma, yayi shiru kamar bai san me aka yi ba.

***
Tsaye yake a bakin wardrobe ɗin, yana ƙarewa kayan ciki kallo kamar ba nasa ba, ya saka hannu da nufin ya ɗauko kaya, hannunsa a sauka a kan koriyar alkyabbarsa.
Kamar ya na jin tsoron Alkyabbar, ya zarota ya na kallonta.
*Sarki mai koriyar alkyabba a dawo lafiya, ka É—anani a kan dokinka ko ka bani kyautar doki*
Shiru ya É—an yi ya na tunani, ta yaya zai ji murya É—aya a mabanbantan wurare, kuma haryanzu bai kai ga ganin fuskar wacece ba, gashi a duk lokacin da zai ji muryar, sai ta kira shi da sarki!.
Ajiye Alkyabbar ya yi, ya É—auko wata dark blue É—in suit, ya shirya a cikinsu ya É—auki jakarsa ya fita.
A É—aki ya tarar da Ammi tana sallar walaha, ya zauna ya jira ta idar.
Ta idar ta kammala Adduointa, sannan ta kalli Adam ta ce "Barka da wannan lokaci takawa".

Yayi murmushi ya ce "Barkanki Ammi, zan wuce ne"

Cikin tausayawa ta kalleshi ta ce "Ka na ganin babu matsala, zaka iya zuwa aikin?"

"Babu wata matsala in sha Allah"

"To matso na yi maka addu'a" ba musu ya matsa kusa sa Ammi, ya durƙuso mata da kansa, ta ɗora hannunta na dama a kan nasa, ta dinga kwararo masa Adduoi.
Wata irin nutsuwa ya din ga ji ta na ratsa shi, ya lumshe idonsa, sai da ta idar, sannan ya riƙe hannun ya sumbaci hannun ya ce "Allah ya ja zamanin giwar Galadima, ya baki yawan rai, Allah ya jiƙan Galadima"

Murmushi ta yi, tare da jin maganar har cikin ran ta ta ce "Amin takawa, Ubangiji Allah ya tsare" ya miƙe yana faɗin Amin, ya bar ɗakin.

***
Tun da abin nan ya faru, an kai ruwa rana sosai, kan malaman su ruma su yarda ta cigaba da zuwa makarantar, bisa sharuÉ—ai sannan ruma ta cigaba da zuwa makarantar.
Tun baya da aka yi sulhu a police station, duk ranar juma'a sai mama ta aika wani ya tasa ruma a gaba sun je duba Asiya, sun kai wani abu, amma kullum babar Asiya babu godiyar Allah, kullum suka je sai ta yi complain, ita kuma ruma kan su taho, sai ta aikata wani abun da za ta sake tunzarata tayi ta masifa.
A haka duk suka ce sun daina zuwa, yau mama ta ce dan Allah mai sunan Baba ya saka ruma a gaba su je.
Tun da Allah ya sa babar Asiya ta yi arba da fuskar mai sunan baba, ta shiga hankalinta, ko maganar kirki ta kasa sai kame-kame.
Tun da suka gaisa, ya bata abin da zai bata, ya ce ruma ta tashi su tafi, ko yaya mai jiki bai ce ba balle ya ce Allah ya kyauta.

suka taho hanya, ruma a nutse take babu tsokana da hauma-hauma, saboda kura ta san gidan mai babban sanda.
da suka zo bakin layin su, cikin girmamawa ruma ta kalli mai sunan Baba ta ce "Mai sunan Baba, mama ta ce na taho mata da kayan miya a wurin Hudu"

Ya kalleta ya ce "Idan kin ga dama, ki tsaya hauma-hauma da neman magana a hanya, zaki zo ki sameni".

"In sha Allah ba zan yi ba"

Ganin da mutane a wurin Hudu, ya sanya ruma ta tsaya ta na jira, sai dai kan ya kawo kanta, ta ɗau wuƙa ta din ga daddatsa masa kabewa bai sani ba.

Da ta gaji ta ce "Malam hudu ka sallameni mana"

Ya ce "Yi haƙuri na fara sallamar matan aure, su da zasu ɗora girki"

Ruma ta yamutsa fuska ta ce "To da me matan auren suka fini? Nima fa watarana matar auren nan ce"

Yayi murmushi ya ce "Eh, amma dai yanzu ƙwaila ce, Allah ya nuna mana kin zama matar aure ruma"

Ta haɗe rai ta ce "Gaskiya malam Hudu ka daina gaya mini wannan kalmar ta watsewa, ƙwaila fa iskanci ne"

Ɗan buɗe baki yayi ya na kallonta, sai kuma ya ce "To Allah ya baki haƙuri" sai da ta bawa mutanen wurin dariya.

Can ta kalli Hudu, ta kalli lafcecen billensa kamar an yi masa da gatari ta ce  "Malam Hudu, na daɗe da tambayar nan a zuciyata wai meyasa aka yi maka bille?"

Yayi murmushi ya ce "Delu billen mahauta ne"

"To amma dai da wuƙa aka yi maka ko?"

Ya ce "A'a, aska ce, billen gado ne na mahauta"

"To kai baka gaji kuÉ—i ba sai bille, da babanku ya mutu sai aka raba muku billen?"

"Ke na gaji da wannan wulaƙancin naki, mai zan baki?" Ruma ta miƙa masa kuɗi, ta yi masa bayanin abun da zai bata, ya sallameta ta tafi gida.

Da ta je gida, ta haÉ—a kayan miyan, ta gyara su ta tafi kai markaÉ—e.

****
Tsaye take a harabar Hotel, tana sanye da doguwar riga ja, ta naÉ—e kanta da jan mayafi, fuskarta sanye da tabarau da kuma takunkumin fuska, dan haka idan ba wanda yayi mata cikakken sani ba, ba yadda za ayi ka ganeta.
Wayarta ta É—auko ta kira wata lamba, ta kara a kunnenta, a É—an hasake ta ce "Gani nazo ka na ina?"

"Room A7, Vip" ta ajiye wayara, ta shiga cikin hotel ɗin, babu wanda ta tambaya da kanta ta gano ɗakin, ta tsaya a bakin ƙofa, ta kuma kiran wayar "Gani a ƙofar ɗakin" ta faɗa a taƙaice.

Wani mutum ne ya buɗe ƙofar ɗakin ya leƙo ya ce "Ke ce baƙuwar yallaɓai?"

"Kai ka san wani Yallaɓai, ka je ka gaya masa gani na zo"

"Ok, to dama cewa ya yi a shigo da ke"

"Ba zan shigo ba, idan ya matsu ya fito idan kuma ba a matse yake ba zan yi tafiyata, bana son jira".

Ya É—an yi jimm ya ce "Amma kamar maganar ki ta yi tsauri"

A fusace ta ce "Kai ka san wacece ni kuwa? Na yi mai wuyar ai da na zo nan, idan ba zai fito ba zan tafi"

Juyawa mutumin ya yi ya koma cikin É—akin, babu daÉ—ewa sai ga wani mutumin ya fito, shi ma fuskarsa rufe da takunkumi.

"Ki shigo mana, zuwa bai yi miki wahala ba sai shigowa?"

"Ba zan shigo ba, ka gaya mini koma menene a nan ina jin ka"

Ya ce "Well, mu je ƙasa to, sai mu yi magana"

Tare suka sauka ƙasa, suka samu wuri suka zauna, ya dubeta ya ce "To sauke takunkumin mana"

"Ba zan sauke ba, wai tukuna kai wayene naga kamar ka na ƙoƙarin raina mini hankali"
Chapter 34 · 0% Book details