Sashe 26
Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Huzaifa a ransa ya ce 'Alhamdilillah, na samo maganinki'
"Tabbas Deluwa kin kwaso mana abin kunya, yanzu abin da zai faru shi ne, ki haɗa kayanki a ɓoye, cikin dare na kai ki tasha ki bar gidan nan, dan idan mai sunan Baba ya sani sai ya jefa ki a rijiya"
Sake rushewa ta yi da kuka har da majina, ya yi saurin cewa "Sai mama ta jiyo kina kuka asirinki ya tonu ko?"
Ta goge hawanyeta ta ce "To ya zan yi?"
"Shikenan, zan rufa miki asiri, amma zaki din ga yi mini wankin uniform".
"Eh na yadda, amma dan Allah kar ka faÉ—awa mama, bana son a koreni dan Allah"
Huzaifa ya yi wani murmushi cikin mugunta ya ce "To na ji, goge hawayen ba zan tona miki asiri ba"
Abu kamar wasa, ruma ko abinci ba ta iya ci, gashi kullum sai ta wanke wa Huzaifa kayan uniform.
Mama ta gaji ta ritsa ruma, har da bulala sannan ta zauna ta yiwa mama bayanin abin da yake damunta.
Mama ta yi salati ta sanar da Ubangiji, gaba ɗaya ruma ba ta da wayo, ga shegiyar tambaya idan kuma ka yi mata bayani yadda za ta fahimta, nan ma ta yi wata kwaɓar.
Sai da mama ta yi da gaske, sannan Ruma ta yadda ba ta da ciki, dan har da nunawa mama cikinta wai ya kumbura É—a ne a ciki.
******
Ta na zaune a kan sallaya ta idar da salla, sai dai ta lula duniyar tunani, ba lazamin take yi ba.
Kamar daga sama ta ji ana kiran sunanta, ta yi firgigit ta dawo hayyacinta.
"Ohh Nusaiba, an gama girkin daren ne?"
Nusaiba cikin damuwa ta dubi Ammi sannan ta ce, "Ammi, tunanin me ki ke yi haka ne? kin san fa ba ki da cikakkiyar lafiya"
Ammi ta yi ajiyar zuciya ta ce "Nusaiba tunanin nan na dole ne, shi yake yin kansa, abubuwa sun yi mini yawa, bana son na nuna gazawata amma ni na san na gaza na kasa shawo kan komai, al'amura na ta ƙara dagule mini"
"Me kuma ya faru ne?"
"Mahmud, lamarinsa yana damuna, ga kuma yadda aka addabawa yarinyar nan a cikin gidan nan, haƙurina ya fara ƙarewa, duk wanda ya taɓa Iman ni ya taɓa raina ya na ɓaci fiye da tunaninki"
Nusaiba ta gyara zamanta ta ce "Ammi, kin san wannan duk shirin Mummy ne, so take ki magantu ku raba abin faɗa a cikin garin nan, ita take buga miki wannan wasan, ki ƙyaketa kuma ki yi haƙuri ki ɗauke kan ki daga Mahmud, ba ga takawa nan ba, mu da shi mun isheki rayuwa su je su ƙarata mana"
Ammi ta girgiza kai ta ce "Nusaiba kenan, ba zaki gane ba, tashi maza ki je ki tabattar an gama komai, sannan ki kira mini Iman, ba na son zamanta ita kaÉ—ai"
Nusaiba ta ce "To shikenan Ammi, bari na je".
Sannu a hankali yake tafiya, tamkar ya na tausayawa ƙasar da yake takawa, har wani rangaji yake kamar wanda ake yiwa kiɗa.
Fuskar nan a murtuke babu annuri, in da ya sa a gaba kawai yake kallo, yake burin cinmma. Babu tsammani suka yi kiciɓis a baranda, ba tare da ɗaya ya san ɗaya ya taho ba, kuma aka rasa wanda zai bawa wani hanya ya wuce.
Kallon-kallo suka yi na wani É—an lokaci, sannan ya lumshe idonsa a hankali ya buÉ—e. "Banihanya"
Kallonsa ya yi irin kallon ba ka isa ba ya ce "Ni da kai waye ya tarewa wani hanya?"
Cikin tsawa da zafin zuciya ya ce "Ka bani hanya na ce"
Murmushin gefen baki yayi, tare da rausayar da kai, yayi taku biyu ya koma gefe ya bashi hanya.
Sai da ya ƙare masa kallo, kamar ba zai wuce ba, sannan ya cigaba da takawa sannu a hankali ya wuce.
Ya waiwaya ya bi bayansa da kallo, yayi wani murmushi sannan ya ce "Zamu ga wanda ya fi iya buga wasan sa"
(A mini afuwa ban editing ba)
AYSHERCOOL
08081012143
[19/07, 8:42 am] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
        Â
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daÉ—aÉ—an litattafan hausa na sauraro.
P13
Kwanci tashi asarar mai rai, ruma ta kammala primary school za ta shiga sakandare, sai murna take yi, sai dai babu abin da ya sauya a halayenta na rashin ji, ta hanasu sakat,a gidan, da an jima sai ta buga tsalle ta ce "Wooo ni zan shiga sakanni in dire"
Yasir ya ce "Ji banza, me aka yi da maza meye wata sakandare, ai yanzu aka fara"
"A'a bar ni na yi tsalle, na samu cigaba a rayuwa ta, Sakandire fa, zan shiga jss1 ai girma ya zo, yanzu ni ma zan yi tsayi tun da zan shiga Sakandire"
Usman ne ya miƙo mata kuɗi ya ce "Yi sauri ki je wurin mai shayi, ki karɓo mini madara zan karya"
Ɗan ɓata fuska ta yi ta ce "Mama fa ta hana ni zuwa wurin mai shayi, da mai kifi da mai nama"
"Za ki wuce ki je ko sai na zo kan ki?"
Ba dan ta na son aiken ba, ta karɓa ta saka hijjabi ta fita, tama tafe tana shan farar ƙasa, bakinta yayi fari tas, kai ka ce akuya ce ta dumbuji dusa.
Ko da ta isa rumfar, dandzon matasa ne a ciki, sun cika kuma galibi abokan yayyenta ne, ba wanda ta kula a cikinsu ta miƙa kuɗi a bata madara.
"Rumaisa, ina Dambele?" Cewar wani matashi da yake ƙoƙarin kai lomar indomie.
Ta kalleshi ta ce "waye kuma dambele?"
"Ussy mana, na gidanku"
"Sai ka ce mini wani dambele kuma, kamar sunan rago, yana gida ya aka yi?"
"A'a ba komai, kawai na tambayeki ne, kin san Usman dambele wani É—an ball ne, shi ma haka ake ce masa a filin ball".
"Ni zaka gayawa dambele É—an ball me, ai sai dai na baka labari"
Kan kace me, aka ɓarke da hirar ball a teburin mai shayi tare da ruma, yadda take bayanin ball ya isa ka gane ƙanwar maza ce, gaba ɗaya ta manta da aike da aka yi mata, ta tsaya ana sharhi da ita.
A ƙalla ta kai mintuna arba'in a wurin, ta manta da aiken gaba ɗaya, ga wurin shayin a ƙofar gidan su yaje, ya ci ace ta je ta dawo, amma babu ruma babu dalilinta.
Ba shiri Usman ya sanya riga, ya fito nemanta, 'yar muryarta kawai yake jiyowa, tana bayani, har da dukan teburin mai shayi tana mayar da yadda aka yi.
"Ke! Meye haka?" Firgigit ta waiwaya, ta ga Usman a tsaye a bayanta.
"Aiken da na yi miki kenan?"
Kame-kame ta tsaya yi, dan har ga Allah ta manta da wani aike, musun ball na É—ibarta a rumfar mai shayi.
"Dambele yanzu nake tambayar ruma kai, ashe kana gidan ma, yarinyar nan ta burgeni, ta san ta kan ball abin mamaki, gaskiya na yarda ƙanwar maza ce"
A ƙule ya ce "Kai dilla ware, wannan ai hauka ne, kawai kun saka yarinya a gaba, kuna wani surutu, meye alaƙarku da ita?"
"Haba Usman, Ruma ai ƙanwarmu ce"
"Ba wani ƙanwarku, baku haɗa alaƙar komai da ita ba, ke kuma wuce kan na saka ƙafata, na kifa ki a wurin" sumi-sumi ta bar rumfar mai shayin ta nufi gida.
Ya bita gidan, ya dinga yi mata masifa, kamar zai cinye ta É—anya.
*****
"Hutawarki lafiya uwar ɗakina ta kai na, jirgin sama maƙurar tafiya komai nisan ta"
Gyara zama ta yi ta dubeta ta ce "Bani labari, me ake ciki ne?"
"A'a, labarin bai gama nuna ba, amma ki bari ya ƙarasa tukuna, amma fa gida ya ƙara hargitsewa, ina ta gwara kawuna ta ko ina, na hanata sukuni, kusan tun bayan da Mahmud ya sa ƙafa yayi fatali da ƙudurinta"
"Hajiya Jamila, idan har muka tafi a kan tsarin da muka yi da farko, to tabbas zamu cimma buri, sarautar ta bar gidanku har abada"
Hajiya Jamila ta yi murmushi ta ce "Ai hakan na fi so, gara ai ayi biyu babu, sai na yi mata kassarawar da zata bar gidan nan da ƙafafuwanta, tun da dai na fuskanci asiri ba ya cin ta, gara ayi mutuwar kasko"
Dariya suka yi a tare, suna tafawa cike da duniyanci, tare da cigaba da tattaunawa a kan cikar muradansu.
****
Tamkar mai shirin zarewa, haka yake kai gwauro, ya kai mari a cikin katafaren falon, da ya sha ado da kayan alatu kamar ba za a bar duniyar ba.
Gefe guda wani babban mutum ne, zaune a ɗaya daga cikin jerin kujerun da suke falon, hannunsa riƙe da wani kwagiri, fuskarsa ɗauke damuwa.
Matashin ya daki teburi ya ce "Daddy meye abin yi ne? Ka na zaune ba ka ce komai ba?"
Dattijon ya numfasa sannan ya ce "Ka bini a hankali, ina tunanin wani abu ne"
"Daddy ba mu da isasshen lokaci fa, you know am following your footsteps, idan aka ɓata siyasarka, zai shafeni, mutum mai girma da daraja, kamar kai wannan ɗan ƙaramin alhakin zai kawowa barazana, gaba ɗaya gidajen jaridu, da dandalin sada zumunta, an buga labarin nan, kamar kai ka cancanci haka a ƙasar nan"
Murmushi mutumin ya yi ya ce "Easy Khalifa, ai ja da baya ga zaki ba tsoro bane ba, shirin yaƙi ne, haka zalika yaro bai san wuta ba sai ya taka, ka ƙyale shi, a yanzu ba ta tasa ma nake yi ba, na zuba ido ne in ga wani mataki za a ɗauka a kansa. Saboda idan ya matsa sai ya fasa ƙwai, to ba ni kaɗai za ta shafa ba, zata shafi manyan ƙasar nan da dama, yaron tone-tonensa ya yiwa, amma yana daf da tona wuƙar da za ta yi ajalinsa"
"Ohh my God, Daddy sai wasu irin maganganu ka ke yi, amma haryanzu ba ka gaya mini menene mafita ba"
Alama ya yiwa Khalifa da ya je, Khalifa ya ƙarasa gabansa ya durƙusa. Ya tallafo kan Khalifa ya yi masa raɗa a kunne.
A take damuwar kan fuskarsa ta gushe, murmushi ya mamaye fuskar ta sa ya yiwa mahaifin na sa alamar jinjina da hannunsa.
"Tabbas Deluwa kin kwaso mana abin kunya, yanzu abin da zai faru shi ne, ki haɗa kayanki a ɓoye, cikin dare na kai ki tasha ki bar gidan nan, dan idan mai sunan Baba ya sani sai ya jefa ki a rijiya"
Sake rushewa ta yi da kuka har da majina, ya yi saurin cewa "Sai mama ta jiyo kina kuka asirinki ya tonu ko?"
Ta goge hawanyeta ta ce "To ya zan yi?"
"Shikenan, zan rufa miki asiri, amma zaki din ga yi mini wankin uniform".
"Eh na yadda, amma dan Allah kar ka faÉ—awa mama, bana son a koreni dan Allah"
Huzaifa ya yi wani murmushi cikin mugunta ya ce "To na ji, goge hawayen ba zan tona miki asiri ba"
Abu kamar wasa, ruma ko abinci ba ta iya ci, gashi kullum sai ta wanke wa Huzaifa kayan uniform.
Mama ta gaji ta ritsa ruma, har da bulala sannan ta zauna ta yiwa mama bayanin abin da yake damunta.
Mama ta yi salati ta sanar da Ubangiji, gaba ɗaya ruma ba ta da wayo, ga shegiyar tambaya idan kuma ka yi mata bayani yadda za ta fahimta, nan ma ta yi wata kwaɓar.
Sai da mama ta yi da gaske, sannan Ruma ta yadda ba ta da ciki, dan har da nunawa mama cikinta wai ya kumbura É—a ne a ciki.
******
Ta na zaune a kan sallaya ta idar da salla, sai dai ta lula duniyar tunani, ba lazamin take yi ba.
Kamar daga sama ta ji ana kiran sunanta, ta yi firgigit ta dawo hayyacinta.
"Ohh Nusaiba, an gama girkin daren ne?"
Nusaiba cikin damuwa ta dubi Ammi sannan ta ce, "Ammi, tunanin me ki ke yi haka ne? kin san fa ba ki da cikakkiyar lafiya"
Ammi ta yi ajiyar zuciya ta ce "Nusaiba tunanin nan na dole ne, shi yake yin kansa, abubuwa sun yi mini yawa, bana son na nuna gazawata amma ni na san na gaza na kasa shawo kan komai, al'amura na ta ƙara dagule mini"
"Me kuma ya faru ne?"
"Mahmud, lamarinsa yana damuna, ga kuma yadda aka addabawa yarinyar nan a cikin gidan nan, haƙurina ya fara ƙarewa, duk wanda ya taɓa Iman ni ya taɓa raina ya na ɓaci fiye da tunaninki"
Nusaiba ta gyara zamanta ta ce "Ammi, kin san wannan duk shirin Mummy ne, so take ki magantu ku raba abin faɗa a cikin garin nan, ita take buga miki wannan wasan, ki ƙyaketa kuma ki yi haƙuri ki ɗauke kan ki daga Mahmud, ba ga takawa nan ba, mu da shi mun isheki rayuwa su je su ƙarata mana"
Ammi ta girgiza kai ta ce "Nusaiba kenan, ba zaki gane ba, tashi maza ki je ki tabattar an gama komai, sannan ki kira mini Iman, ba na son zamanta ita kaÉ—ai"
Nusaiba ta ce "To shikenan Ammi, bari na je".
Sannu a hankali yake tafiya, tamkar ya na tausayawa ƙasar da yake takawa, har wani rangaji yake kamar wanda ake yiwa kiɗa.
Fuskar nan a murtuke babu annuri, in da ya sa a gaba kawai yake kallo, yake burin cinmma. Babu tsammani suka yi kiciɓis a baranda, ba tare da ɗaya ya san ɗaya ya taho ba, kuma aka rasa wanda zai bawa wani hanya ya wuce.
Kallon-kallo suka yi na wani É—an lokaci, sannan ya lumshe idonsa a hankali ya buÉ—e. "Banihanya"
Kallonsa ya yi irin kallon ba ka isa ba ya ce "Ni da kai waye ya tarewa wani hanya?"
Cikin tsawa da zafin zuciya ya ce "Ka bani hanya na ce"
Murmushin gefen baki yayi, tare da rausayar da kai, yayi taku biyu ya koma gefe ya bashi hanya.
Sai da ya ƙare masa kallo, kamar ba zai wuce ba, sannan ya cigaba da takawa sannu a hankali ya wuce.
Ya waiwaya ya bi bayansa da kallo, yayi wani murmushi sannan ya ce "Zamu ga wanda ya fi iya buga wasan sa"
(A mini afuwa ban editing ba)
AYSHERCOOL
08081012143
[19/07, 8:42 am] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
        Â
Na Aisha Adam (Ayshercool)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Ku yi subscribing YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daÉ—aÉ—an litattafan hausa na sauraro.
P13
Kwanci tashi asarar mai rai, ruma ta kammala primary school za ta shiga sakandare, sai murna take yi, sai dai babu abin da ya sauya a halayenta na rashin ji, ta hanasu sakat,a gidan, da an jima sai ta buga tsalle ta ce "Wooo ni zan shiga sakanni in dire"
Yasir ya ce "Ji banza, me aka yi da maza meye wata sakandare, ai yanzu aka fara"
"A'a bar ni na yi tsalle, na samu cigaba a rayuwa ta, Sakandire fa, zan shiga jss1 ai girma ya zo, yanzu ni ma zan yi tsayi tun da zan shiga Sakandire"
Usman ne ya miƙo mata kuɗi ya ce "Yi sauri ki je wurin mai shayi, ki karɓo mini madara zan karya"
Ɗan ɓata fuska ta yi ta ce "Mama fa ta hana ni zuwa wurin mai shayi, da mai kifi da mai nama"
"Za ki wuce ki je ko sai na zo kan ki?"
Ba dan ta na son aiken ba, ta karɓa ta saka hijjabi ta fita, tama tafe tana shan farar ƙasa, bakinta yayi fari tas, kai ka ce akuya ce ta dumbuji dusa.
Ko da ta isa rumfar, dandzon matasa ne a ciki, sun cika kuma galibi abokan yayyenta ne, ba wanda ta kula a cikinsu ta miƙa kuɗi a bata madara.
"Rumaisa, ina Dambele?" Cewar wani matashi da yake ƙoƙarin kai lomar indomie.
Ta kalleshi ta ce "waye kuma dambele?"
"Ussy mana, na gidanku"
"Sai ka ce mini wani dambele kuma, kamar sunan rago, yana gida ya aka yi?"
"A'a ba komai, kawai na tambayeki ne, kin san Usman dambele wani É—an ball ne, shi ma haka ake ce masa a filin ball".
"Ni zaka gayawa dambele É—an ball me, ai sai dai na baka labari"
Kan kace me, aka ɓarke da hirar ball a teburin mai shayi tare da ruma, yadda take bayanin ball ya isa ka gane ƙanwar maza ce, gaba ɗaya ta manta da aike da aka yi mata, ta tsaya ana sharhi da ita.
A ƙalla ta kai mintuna arba'in a wurin, ta manta da aiken gaba ɗaya, ga wurin shayin a ƙofar gidan su yaje, ya ci ace ta je ta dawo, amma babu ruma babu dalilinta.
Ba shiri Usman ya sanya riga, ya fito nemanta, 'yar muryarta kawai yake jiyowa, tana bayani, har da dukan teburin mai shayi tana mayar da yadda aka yi.
"Ke! Meye haka?" Firgigit ta waiwaya, ta ga Usman a tsaye a bayanta.
"Aiken da na yi miki kenan?"
Kame-kame ta tsaya yi, dan har ga Allah ta manta da wani aike, musun ball na É—ibarta a rumfar mai shayi.
"Dambele yanzu nake tambayar ruma kai, ashe kana gidan ma, yarinyar nan ta burgeni, ta san ta kan ball abin mamaki, gaskiya na yarda ƙanwar maza ce"
A ƙule ya ce "Kai dilla ware, wannan ai hauka ne, kawai kun saka yarinya a gaba, kuna wani surutu, meye alaƙarku da ita?"
"Haba Usman, Ruma ai ƙanwarmu ce"
"Ba wani ƙanwarku, baku haɗa alaƙar komai da ita ba, ke kuma wuce kan na saka ƙafata, na kifa ki a wurin" sumi-sumi ta bar rumfar mai shayin ta nufi gida.
Ya bita gidan, ya dinga yi mata masifa, kamar zai cinye ta É—anya.
*****
"Hutawarki lafiya uwar ɗakina ta kai na, jirgin sama maƙurar tafiya komai nisan ta"
Gyara zama ta yi ta dubeta ta ce "Bani labari, me ake ciki ne?"
"A'a, labarin bai gama nuna ba, amma ki bari ya ƙarasa tukuna, amma fa gida ya ƙara hargitsewa, ina ta gwara kawuna ta ko ina, na hanata sukuni, kusan tun bayan da Mahmud ya sa ƙafa yayi fatali da ƙudurinta"
"Hajiya Jamila, idan har muka tafi a kan tsarin da muka yi da farko, to tabbas zamu cimma buri, sarautar ta bar gidanku har abada"
Hajiya Jamila ta yi murmushi ta ce "Ai hakan na fi so, gara ai ayi biyu babu, sai na yi mata kassarawar da zata bar gidan nan da ƙafafuwanta, tun da dai na fuskanci asiri ba ya cin ta, gara ayi mutuwar kasko"
Dariya suka yi a tare, suna tafawa cike da duniyanci, tare da cigaba da tattaunawa a kan cikar muradansu.
****
Tamkar mai shirin zarewa, haka yake kai gwauro, ya kai mari a cikin katafaren falon, da ya sha ado da kayan alatu kamar ba za a bar duniyar ba.
Gefe guda wani babban mutum ne, zaune a ɗaya daga cikin jerin kujerun da suke falon, hannunsa riƙe da wani kwagiri, fuskarsa ɗauke damuwa.
Matashin ya daki teburi ya ce "Daddy meye abin yi ne? Ka na zaune ba ka ce komai ba?"
Dattijon ya numfasa sannan ya ce "Ka bini a hankali, ina tunanin wani abu ne"
"Daddy ba mu da isasshen lokaci fa, you know am following your footsteps, idan aka ɓata siyasarka, zai shafeni, mutum mai girma da daraja, kamar kai wannan ɗan ƙaramin alhakin zai kawowa barazana, gaba ɗaya gidajen jaridu, da dandalin sada zumunta, an buga labarin nan, kamar kai ka cancanci haka a ƙasar nan"
Murmushi mutumin ya yi ya ce "Easy Khalifa, ai ja da baya ga zaki ba tsoro bane ba, shirin yaƙi ne, haka zalika yaro bai san wuta ba sai ya taka, ka ƙyale shi, a yanzu ba ta tasa ma nake yi ba, na zuba ido ne in ga wani mataki za a ɗauka a kansa. Saboda idan ya matsa sai ya fasa ƙwai, to ba ni kaɗai za ta shafa ba, zata shafi manyan ƙasar nan da dama, yaron tone-tonensa ya yiwa, amma yana daf da tona wuƙar da za ta yi ajalinsa"
"Ohh my God, Daddy sai wasu irin maganganu ka ke yi, amma haryanzu ba ka gaya mini menene mafita ba"
Alama ya yiwa Khalifa da ya je, Khalifa ya ƙarasa gabansa ya durƙusa. Ya tallafo kan Khalifa ya yi masa raɗa a kunne.
A take damuwar kan fuskarsa ta gushe, murmushi ya mamaye fuskar ta sa ya yiwa mahaifin na sa alamar jinjina da hannunsa.