Sashe 58
Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Eh mana, wani abu fa ka bugeni da shi a bayana, ai ka waiwayo ka bani haƙuri ko?"
Zai yinƙura kenan ya ji an danƙi hannunsa an ja shi. Wani mutum ne shima mai rufaffiyar fuska ya riƙe shi.
Cikin tsiwa ta ce "Bana yi wa manya Allah ya isa, amma wallahi ban yafe ba, Allah ya haɗaka da wanda yafi ƙarfinka kaima ya ci zalinka"
Idon kowa ya dawo kan ruma, ita kuwa ko a jikinta, ta koma ta sai gyaÉ—arta da ruwan leda, ta koma shagon mai awo.
Ko da ta koma, ta bi su ta bawa kowa leda ɗaya ta gyɗa, har da wannan mutumin da ya shigo ya zauna.
Ta kalli mutumin ta ce "ÆŠan uwanmu kana da 'ya'ya?" Ya jinjina mata kai alamar eh.
Ta kuma bashi ɗauri biyu ta ce "To ka kai musu wannan, ga ruwa ma na baka. Ku kuma ku tashi mu tafi, 'yan garin nan ba su da mutunci, wani ya bugeni da wani abu a baya, kuma yaƙi bani haƙuri ni kuwa na masa Allah ya isa, kuma wallahi na koma gida sai na je na gaya wa 'yan sanda, abin da ske a garin nan da abin da na gani ana yi! Sai na faɗi komai"
Ayshercool.
*Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*
Ba ta ji ko ɗar ba da ta yi maganar, ta ɗau abubuwan da ta saya, mutumin nan ya bi ruma da kallo, har zata fita daga shagon ya ce "Ƙawata yaushe zan zo kano na kawo miki ziyara, in ga Kanon da ake cewa ta fi garinmu kyau?"
Murmushi ta yi ta ce "Idan ka zo kano ka ce wurina ka zo sai yayyena sun naÉ—a maka na jaki ni ma su karairayani, cewa za su yi kai saurayina ne, amma dai Kano tana da kyau sosai, sai watarana É—an uwanmu"
Ta yi waje, su lawisa suka bita kamar munafukai.
Jerin babura ne suka din ga shigowa cikin kasuwar ko ta ko ina, suna É—aukar mutanen nan masu rufaffiyar fuska suna barin cikin kasuwar.
Ruma ta ce "Zaliha wai wannan mutanen idan suka idan su ka bar nan ina suke tafiya a kan bauran nan?"
Jiki a sanyaye zaliha ta ce "Cikin daji suke tafiya, ruma mutumin nan fa na cikin rumfar nan shima fa sune, É—an uwansu ne" waro ido ruma ta yi ta ce "Haba dai? Amma nake hira da shi?".
"Shiyasa ake ce miki ki iya bakinki, kin zage sai zuba ki ke har da cewa zaki gaya wa 'yan sanda".
"To ba gara a gaya wa 'yan sandan ba, tun da ku tsoronsu ku ke ba za ku iya ba, ai taimakonku zan yi, ke nifa DPO É—in unguwarmu ma ya sanni, tun da na karya wata yarinya ya sanni, dan haka sai na je na gaya masa".
Lawisa ta ce "Ke waye ya ce miki aikin 'yan sanda ne?, sojoji ma fa ake turowa, amma haryanzu abu ya gagara mu samu tsaro "
Tunawa ta yi da batun da aka yi, na da sanin wasu daga jami'an tsaro ake zirga-zirga da makamai amma ba yadda suka iya.
Ƙarar wani abu ruma ta ji, da bata taɓa jin sauti irinsa ba, sai gani tayi mutane suna gudu, mutumin da yake tafiya a kusa da su ya faɗi cikin jini.
Aka buÉ—ewa mutanen kasuwar wuta. Tuni ta nemi su lawisa ta rasa sun arta, ita kuwa ta kasa gudun, ta kasa gaba ta kasa baya, sai rungume kayan sayayyar ta da tayi tana rarraba ido, mutane sai faÉ—uwa suke cikin jini.
Ji ta yi an kama hannunta an ja ta da gudu, an bi ta bayan kasuwar da ita, ba ta san ko waye ba, sai da suka bar cikin kasuwar, sannan suka tsaya.
Mutumin da ya zauna a rumfar mai awo ne, sai dai shima a wannan karon fuskarsa a rufe take, da kayansa da kuma muryarsa ta gane shi ya ce mata "Yi sauri ki bar wurin nan, ki tafi gida" daga haka ya juya ya barta.
Ikon Allah ne ya kai ruma gida, dan ba ta taɓa ganin tashin hankali kamar wannan ba, mutane kwance a cikin jini an kashe su.
Ko da ta je gidan babu kowa, ta zube kayan hannunta a tsakar gida ta zauna, ta yi shiru tana cigaba da jiyo ƙarar harbe-harbe sama-sama.
Ta yi kusan mintuna ashirin, sai ga iya da su lawisa sun shigo, da alama ita suka tafi nema.
A gigice iya ta ƙaraso in da ruma take tana faɗin "Rumaisa babu abin da ya sameki ko? Bari gobe in Allah ya kaimu da sassafe azo a mayar da ke, mutanen nan sun sake waiwayo mu, ina fatan babu abin da suka yi miki"
Ta kalli jikinta, ba abin da ya sameta sai dai jini duk ya taɓata. Iya ta saka ruma ta yi wanka ta canza kaya.
Sai dai ruma ta kasa magana, dan ta tsorata da abin da ta gani, gawar mutane kwance a cikin jini.
Da ƙyar ta iya cin abinci, ta nemi wuri ta kwanta, sai dai bacci ya gagari ruma sai tsananin zurfin tunani.
Ruma tana jiyo iya da sauran mutan gidan, suna mayar da zance da irin ɓarnar da aka yi a harin na yau, a nan ta ji irin masifu da tashin hankalin da suka fuskanta a baya, wanda haryanzu suna kai.
Tun da Allah ya sa ruma ta buɗi ido, ba ta taɓa ganin tashin hankali kamar wannan ba.
****
Takawa jiki yayi kyau, ya daina jin abin da yake ji, ya cigaba da sabgoginsa a Abuja, sai dai duk yadda ya so ya gama abin da yake ya dawo kano abu ya gagara.
Tattaunawa ce ta musamman suka yi, ita ma tattaunawar sai dare suka yi ta, sai bayan sha biyun dare sannan suka gama, ya fito zai tafi masaukinsa, dan ko direban bai nema ba yau.
Ya biya wani restaurant ya ci abinci, sannan ya nufi makwanci. Tun safiyar yau yake fama da fargaba da ya rasa dalilinta. Yana tsaka da tuƙi gabansa yayi wata irin mummunar faɗuwa gabansa ya faɗi, ƙirjinsa yayi wani irin bugawa da sai da burki ya kusa ƙwace masa a tsakiyar titi. Da ƙyar yayi parkinh ya kifa kansa a kan sitiyari, ya dafe ƙirjinsa sa hannu ɗaya, yana jin yadda zuciyarsa ke tsananta bugu.
***
Gari yayi tsit kamar an yi ruwa an shanye, duk wannan balahira da ta faru har aka yi aka gama, babu jami'in tsaro ko ɗaya da ya bayyana a wurin, sai da ƙura ta lafa waɗanda aka karkashe wa 'yan uwa, suka je suka ɗebo gawarwaki, aka yi musu sutura ana jiran gari ya waye a sallacesu, wasu gawarwakin ma ba a samu ɗebo su ba saboda tsoro.
Dare ya tsala sosai, farin wata ya haske gari, ko ƙwaƙwƙwaran motsin wani abu ba ka ji, ciki har da ƙwari.
Idanunta tarwai, babu alamar bacci zai ɗauketa ko da kuwa ɓarawo ne. Daga can ƙasa-ƙasa ta fara jiyo jiniyar babura suna kusantowa. Ta runtse idanunta tana hango yadda a abubuwa suka faru ɗazu a kasuwa, sai dai ƙarar baburan suka cigaba da kusantowa yana cika mata kunne.
Hannu ta saka ta toshe kunnuwanta, tare da sake rintse idanuwanta. Dan ƙarar baburan na sake hasko mata abun da ya faru
Ba ta san iya adadin lokacin da ta kwashe a haka ba, ta sauke hannuwanta, iface-iface ta din ga jiyowa ana salatuttuka, hayaniya ta yi yawa a ilahirin kewayen gidan.
Muryar mijin iya ta jiyo yana faɗin "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, mutanen nan sun sake dawowa, mai kuma suke nema da mu? Me suke buƙata?"
Iya ma cikin kuka take salati tana "Allah kana gani, Allah bamu da wani gata sai kai, Allah ka duba mu".
Wani irin ihu da gurnani kunnuwan ruma suka jiyo mata, kai daga jin ihun ka san wadda take yi a cikin masifa take.
Muryar wani magidanci suka ji yana ta magiya "Dan girman Allah ku yi mini rai, 'ya ta dan Allah ku rufa mini asiri"
Ƙarar harbi suka ji, daga nan basu sake jin muryar mutumin ba, sai kuka da ihun yarinyar. Wadda ruma sukan yi wasa tare.
Gaba ɗaya kururuwar mata da hargowar mutanen ta karaɗe ƙauyen, haɗi da harbe-harben bindiga.
Kan iya suyi wani yunƙuri, wasu irin zaratan maza su kusan huɗu sun afko cikin gidan.
Mijin iya ya tsaya ƙyam, babu tsoro a tare da shi ya ce 'Haka muka yi da ku? Kun saɓa alƙawari mun yi duk abin da kuke so, amma bamu tsira ba, so kuke lallai sai mun fita mun bar muku garin, idan mun fita ina kuke son mu je?"
Cikin tsawa wani ya ce "Ba tuna mana alƙawari muka zo ka yi ba, aiki muka fito yi, kai ku kama shi ku ɗaure mana shi" aikuwa suka kama dattijon suka yi masa ɗaurin huhun goro, suka rufe masa baki, sannan suka afko cikin ɗakin.
Lawisa da zaliha sai kyarma suke yi, ruma kuwa tayi zuruu da ido, tana ganin sarautar Allah, abin da take ji a radion mama yau gashi a zahiri ba labari ba.
Hargitse kayan É—akin suka shiga yi, wasu kuma suka zaga suka kwance garken dabbobin da ake kiwo a gidan, suka yi waje da su.
Ɗaya daga cikin su, ya zo ya danƙi ruma ya fara janta.
Cikin kururuwa iya take faɗin "Ka yi wa Allah da ma'aikinsa ka ƙyale yarinyar nan, baƙuwace 'yar amana ce, dan Allah karku cutar da ita".
"Kai wuce da ita" ɗayan yayi umarni cikin tsawa. Iya ta yinƙura zata yi magana, ɗayan ya saka bakin bindiga ya buga mata a ka ta zube a ƙasa sumammiya.
Ruma ta zura silifas É—in ta, É—ayan yayi waje da ita yana janta. Ko da suka fita ko waiwayowa ba sa yi, su Zaliha sai kuka suke suna kiran ruma, amma suka ce idan suka kuma magana sai sun harbesu.
Ko da suka fita tuni duk sun tattara waÉ—anda zasu tafi da su, a cikin daren suka ingiza su zuwa cikin daji, ciki har da ruma.
Zai yinƙura kenan ya ji an danƙi hannunsa an ja shi. Wani mutum ne shima mai rufaffiyar fuska ya riƙe shi.
Cikin tsiwa ta ce "Bana yi wa manya Allah ya isa, amma wallahi ban yafe ba, Allah ya haɗaka da wanda yafi ƙarfinka kaima ya ci zalinka"
Idon kowa ya dawo kan ruma, ita kuwa ko a jikinta, ta koma ta sai gyaÉ—arta da ruwan leda, ta koma shagon mai awo.
Ko da ta koma, ta bi su ta bawa kowa leda ɗaya ta gyɗa, har da wannan mutumin da ya shigo ya zauna.
Ta kalli mutumin ta ce "ÆŠan uwanmu kana da 'ya'ya?" Ya jinjina mata kai alamar eh.
Ta kuma bashi ɗauri biyu ta ce "To ka kai musu wannan, ga ruwa ma na baka. Ku kuma ku tashi mu tafi, 'yan garin nan ba su da mutunci, wani ya bugeni da wani abu a baya, kuma yaƙi bani haƙuri ni kuwa na masa Allah ya isa, kuma wallahi na koma gida sai na je na gaya wa 'yan sanda, abin da ske a garin nan da abin da na gani ana yi! Sai na faɗi komai"
Ayshercool.
*Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*
Ba ta ji ko ɗar ba da ta yi maganar, ta ɗau abubuwan da ta saya, mutumin nan ya bi ruma da kallo, har zata fita daga shagon ya ce "Ƙawata yaushe zan zo kano na kawo miki ziyara, in ga Kanon da ake cewa ta fi garinmu kyau?"
Murmushi ta yi ta ce "Idan ka zo kano ka ce wurina ka zo sai yayyena sun naÉ—a maka na jaki ni ma su karairayani, cewa za su yi kai saurayina ne, amma dai Kano tana da kyau sosai, sai watarana É—an uwanmu"
Ta yi waje, su lawisa suka bita kamar munafukai.
Jerin babura ne suka din ga shigowa cikin kasuwar ko ta ko ina, suna É—aukar mutanen nan masu rufaffiyar fuska suna barin cikin kasuwar.
Ruma ta ce "Zaliha wai wannan mutanen idan suka idan su ka bar nan ina suke tafiya a kan bauran nan?"
Jiki a sanyaye zaliha ta ce "Cikin daji suke tafiya, ruma mutumin nan fa na cikin rumfar nan shima fa sune, É—an uwansu ne" waro ido ruma ta yi ta ce "Haba dai? Amma nake hira da shi?".
"Shiyasa ake ce miki ki iya bakinki, kin zage sai zuba ki ke har da cewa zaki gaya wa 'yan sanda".
"To ba gara a gaya wa 'yan sandan ba, tun da ku tsoronsu ku ke ba za ku iya ba, ai taimakonku zan yi, ke nifa DPO É—in unguwarmu ma ya sanni, tun da na karya wata yarinya ya sanni, dan haka sai na je na gaya masa".
Lawisa ta ce "Ke waye ya ce miki aikin 'yan sanda ne?, sojoji ma fa ake turowa, amma haryanzu abu ya gagara mu samu tsaro "
Tunawa ta yi da batun da aka yi, na da sanin wasu daga jami'an tsaro ake zirga-zirga da makamai amma ba yadda suka iya.
Ƙarar wani abu ruma ta ji, da bata taɓa jin sauti irinsa ba, sai gani tayi mutane suna gudu, mutumin da yake tafiya a kusa da su ya faɗi cikin jini.
Aka buÉ—ewa mutanen kasuwar wuta. Tuni ta nemi su lawisa ta rasa sun arta, ita kuwa ta kasa gudun, ta kasa gaba ta kasa baya, sai rungume kayan sayayyar ta da tayi tana rarraba ido, mutane sai faÉ—uwa suke cikin jini.
Ji ta yi an kama hannunta an ja ta da gudu, an bi ta bayan kasuwar da ita, ba ta san ko waye ba, sai da suka bar cikin kasuwar, sannan suka tsaya.
Mutumin da ya zauna a rumfar mai awo ne, sai dai shima a wannan karon fuskarsa a rufe take, da kayansa da kuma muryarsa ta gane shi ya ce mata "Yi sauri ki bar wurin nan, ki tafi gida" daga haka ya juya ya barta.
Ikon Allah ne ya kai ruma gida, dan ba ta taɓa ganin tashin hankali kamar wannan ba, mutane kwance a cikin jini an kashe su.
Ko da ta je gidan babu kowa, ta zube kayan hannunta a tsakar gida ta zauna, ta yi shiru tana cigaba da jiyo ƙarar harbe-harbe sama-sama.
Ta yi kusan mintuna ashirin, sai ga iya da su lawisa sun shigo, da alama ita suka tafi nema.
A gigice iya ta ƙaraso in da ruma take tana faɗin "Rumaisa babu abin da ya sameki ko? Bari gobe in Allah ya kaimu da sassafe azo a mayar da ke, mutanen nan sun sake waiwayo mu, ina fatan babu abin da suka yi miki"
Ta kalli jikinta, ba abin da ya sameta sai dai jini duk ya taɓata. Iya ta saka ruma ta yi wanka ta canza kaya.
Sai dai ruma ta kasa magana, dan ta tsorata da abin da ta gani, gawar mutane kwance a cikin jini.
Da ƙyar ta iya cin abinci, ta nemi wuri ta kwanta, sai dai bacci ya gagari ruma sai tsananin zurfin tunani.
Ruma tana jiyo iya da sauran mutan gidan, suna mayar da zance da irin ɓarnar da aka yi a harin na yau, a nan ta ji irin masifu da tashin hankalin da suka fuskanta a baya, wanda haryanzu suna kai.
Tun da Allah ya sa ruma ta buɗi ido, ba ta taɓa ganin tashin hankali kamar wannan ba.
****
Takawa jiki yayi kyau, ya daina jin abin da yake ji, ya cigaba da sabgoginsa a Abuja, sai dai duk yadda ya so ya gama abin da yake ya dawo kano abu ya gagara.
Tattaunawa ce ta musamman suka yi, ita ma tattaunawar sai dare suka yi ta, sai bayan sha biyun dare sannan suka gama, ya fito zai tafi masaukinsa, dan ko direban bai nema ba yau.
Ya biya wani restaurant ya ci abinci, sannan ya nufi makwanci. Tun safiyar yau yake fama da fargaba da ya rasa dalilinta. Yana tsaka da tuƙi gabansa yayi wata irin mummunar faɗuwa gabansa ya faɗi, ƙirjinsa yayi wani irin bugawa da sai da burki ya kusa ƙwace masa a tsakiyar titi. Da ƙyar yayi parkinh ya kifa kansa a kan sitiyari, ya dafe ƙirjinsa sa hannu ɗaya, yana jin yadda zuciyarsa ke tsananta bugu.
***
Gari yayi tsit kamar an yi ruwa an shanye, duk wannan balahira da ta faru har aka yi aka gama, babu jami'in tsaro ko ɗaya da ya bayyana a wurin, sai da ƙura ta lafa waɗanda aka karkashe wa 'yan uwa, suka je suka ɗebo gawarwaki, aka yi musu sutura ana jiran gari ya waye a sallacesu, wasu gawarwakin ma ba a samu ɗebo su ba saboda tsoro.
Dare ya tsala sosai, farin wata ya haske gari, ko ƙwaƙwƙwaran motsin wani abu ba ka ji, ciki har da ƙwari.
Idanunta tarwai, babu alamar bacci zai ɗauketa ko da kuwa ɓarawo ne. Daga can ƙasa-ƙasa ta fara jiyo jiniyar babura suna kusantowa. Ta runtse idanunta tana hango yadda a abubuwa suka faru ɗazu a kasuwa, sai dai ƙarar baburan suka cigaba da kusantowa yana cika mata kunne.
Hannu ta saka ta toshe kunnuwanta, tare da sake rintse idanuwanta. Dan ƙarar baburan na sake hasko mata abun da ya faru
Ba ta san iya adadin lokacin da ta kwashe a haka ba, ta sauke hannuwanta, iface-iface ta din ga jiyowa ana salatuttuka, hayaniya ta yi yawa a ilahirin kewayen gidan.
Muryar mijin iya ta jiyo yana faɗin "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, mutanen nan sun sake dawowa, mai kuma suke nema da mu? Me suke buƙata?"
Iya ma cikin kuka take salati tana "Allah kana gani, Allah bamu da wani gata sai kai, Allah ka duba mu".
Wani irin ihu da gurnani kunnuwan ruma suka jiyo mata, kai daga jin ihun ka san wadda take yi a cikin masifa take.
Muryar wani magidanci suka ji yana ta magiya "Dan girman Allah ku yi mini rai, 'ya ta dan Allah ku rufa mini asiri"
Ƙarar harbi suka ji, daga nan basu sake jin muryar mutumin ba, sai kuka da ihun yarinyar. Wadda ruma sukan yi wasa tare.
Gaba ɗaya kururuwar mata da hargowar mutanen ta karaɗe ƙauyen, haɗi da harbe-harben bindiga.
Kan iya suyi wani yunƙuri, wasu irin zaratan maza su kusan huɗu sun afko cikin gidan.
Mijin iya ya tsaya ƙyam, babu tsoro a tare da shi ya ce 'Haka muka yi da ku? Kun saɓa alƙawari mun yi duk abin da kuke so, amma bamu tsira ba, so kuke lallai sai mun fita mun bar muku garin, idan mun fita ina kuke son mu je?"
Cikin tsawa wani ya ce "Ba tuna mana alƙawari muka zo ka yi ba, aiki muka fito yi, kai ku kama shi ku ɗaure mana shi" aikuwa suka kama dattijon suka yi masa ɗaurin huhun goro, suka rufe masa baki, sannan suka afko cikin ɗakin.
Lawisa da zaliha sai kyarma suke yi, ruma kuwa tayi zuruu da ido, tana ganin sarautar Allah, abin da take ji a radion mama yau gashi a zahiri ba labari ba.
Hargitse kayan É—akin suka shiga yi, wasu kuma suka zaga suka kwance garken dabbobin da ake kiwo a gidan, suka yi waje da su.
Ɗaya daga cikin su, ya zo ya danƙi ruma ya fara janta.
Cikin kururuwa iya take faɗin "Ka yi wa Allah da ma'aikinsa ka ƙyale yarinyar nan, baƙuwace 'yar amana ce, dan Allah karku cutar da ita".
"Kai wuce da ita" ɗayan yayi umarni cikin tsawa. Iya ta yinƙura zata yi magana, ɗayan ya saka bakin bindiga ya buga mata a ka ta zube a ƙasa sumammiya.
Ruma ta zura silifas É—in ta, É—ayan yayi waje da ita yana janta. Ko da suka fita ko waiwayowa ba sa yi, su Zaliha sai kuka suke suna kiran ruma, amma suka ce idan suka kuma magana sai sun harbesu.
Ko da suka fita tuni duk sun tattara waÉ—anda zasu tafi da su, a cikin daren suka ingiza su zuwa cikin daji, ciki har da ruma.