Sashe 134
Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Adam ya dafa kafaɗar Jamil ya ce "Ba sai mun zurfafa ba, ka san abun da nake nufi, kai ɗan uwana ne Jamil, Samha ma ƙanwata ce, ba na son zumuncin mu ya samu matsala saboda wani dalili, a madadina dan Allah ka bawa Samha haƙuri, ina fatan Allah ya zaɓa mana abun da ya fi alkhairi daga ni har ita"
Daga haka Adam ya fice ya bar Jamil a tsaye da buÉ—aÉ—É—en baki.
Ammi kuwa waya suke yi da rumaisa, rumaisa tana ba ta labarin yadda takawa ya fito da Aliyu bayan rigimar da suka yi aka rufe shi, wanda shi Adam É—in sam bai gaya mata ba.
Ammi ta jinjina al'amarin, tare da yi mata Allah ya kyauta.
Gaba ɗaya rumaisa ba ta san wani abu wai kunyar suruka ba, mama na ta ƙifta mata ido, amma sosai take ta yi wa ammi surutu.
Ammi ta numfasa ta ce "Rumaisa na bayar da saƙo a kawo miki ki ka ƙi karɓa ko?"
Rumaisa ta ce "Laa ashe da gaske yake, na zata shi ya bani, na ce ba zan karɓa ba, bana son wataran yayi mini gori"
"Ahh haba dai, ba zai taɓa yi miki gori ba, duk abun da ya baki ki karɓa ba zai cutar da ke ba, sannan ki din ga yi muku Addu'a a kan lamarin auren nan na ku, turaki na daf da dawowa".
Ita gaba É—aya ma ta manta da maganar auren, sai yanzu da ammin ta tuna mata.
"To, ammi kin san wani abu?"
Ammi ta ce "Sai kin faÉ—a"
"Kewar sabir nake yi sosai, daurewa nake yi dan kar na din ga takura muku"
Ammi ta ce "Subhanallah, rumaisa zan ci gidanku fa, ni akwai wani abu mai kama da takura tsakanina da ke, ba ni na ce duk lokacin da ki ke so ki gaya mini a kawo shi ba? Za'a kawo miki shi ranar da babu makaranta, na san shi ma yana kewarki".
Rumaisa ta yi murmushi ta ce "To ammi, na gode sosai ki gaida kowa da kowa"
"Yauwwa ko ke fa, za su ji in sha Allah" Ammi ta katse wayar tana murmushi.
A can falo kuwa, Iman ce take bawa sabir abinci, an fara gwada masa abu mai ruwa-ruwa.
Baba uwani na ta tsokanar iman "Ohh tsakanin uwa da É—a sai Allah, tsakanin Sabir da iman sai Allah"
Iman ta yi murmushi ta ce "Tsakanin kaka da jikarta ma sai Allah ba"
Baba uwani ta ce "Uhumm kakar da yake yi wa ƙyuya, daga ke sai ammi sai babansa, sai kuma Nusaiba idan ya ga dama, yaro ba ya yadda da kowa"
"Kar ki damu baba uwani, zai yadda da ke ne"
"Mhmm, ni kuwa Iman, ina yarinyar da aka ce ta tsinci yaron nan, Haryanzu tana nan kuwa?"
"Laa tana nan baba uwani, baki taɓa ganinta ba?"
"Oho, yo ni a ina zan ganta ma"
Iman ta ce "Kai haba, ta zazzo gidan nan fa sosai da sosai, ai duk ƙyuyar nan da yake yi, ba ya yi mata, dariya sosai ke ba kya ce shine ba".
Baba uwani cikin son bugun ciki da gulma, ta sake ƙasa da murya ta ce "Ni kuwa wai babba ce ko yarinya?"
"Gaskiya Yarinya ce sosai, dan duk mun girmeta"
"Ikon Allah, Æ´ar nan unguwar ce kuma? Na ji kin ce tana zuwa gidan nan, ai ni fa ban zaci ma Æ´ar nan garin ce ba".
"A'a ba unguwar nan take ba, zuwa take yi, amma kwana biyu ma ba ta zo ba".
"Ikon Allah, ni kuwa dan Allah duk ranar da Allah ya kawota ki nuna mini ita"
Iman ta yi murmushi ta ce "Maman sabir, to shikenan in sha Allah" Baba uwani ta yi gaba tana jin alamun nasara.
Tafiyar baba uwani babu jimawa, sai ga Jabir yayi sallama, cikin sauri Iman ta rufe kanta da hula, ta gyara zamanta, tare da mayar da hankalinta sosai a kan Sabir.
Murmushi Jabir yayi, ya ƙarasa kusa da ita ya zauna ya ce "Gashin ake yi mini rowar gani kuma?" Ta yi masa shiru ba ta ce komai ba.
"Talk mana iman, ko miskilanci ne?"
Ta yi masa shiru, ta cigaba da bawa Sabir abinci, Jabir ya miƙe hannu ya ɗauki Sabir, yana ƙure Iman da wani irin kallo, wani irin abu yana fuzgar zuciyarsa game da ita.
Wuyanta yake bi da kallo, ya haÉ—iye wani irin yawu, ya zaunar da sabir a jikinsa, amma Sabir ya ce bai san zance ba ya sanya kuka.
"Ka bani shi abinci nake ba shi".
"Ba zan baki ba, sai kin kalleni kin amsa mini"
Ammi ce ta fito falon, cikin fara'a ta ce "Jabir, kwana biyu ina ka ɓuya ne?"
Yayi murmushi ya ce "Tuba nake ammi, ayyuka ne suka yi mini yawa sosai"
Ammi ta kalli Sabir ta ce "Rigimamme, kai ba ka gane iyayenka ne, kowa ma ba zai É—auke ka ba?"
Iman ta tashi daga kan kujerar, ta karɓi Sabir ta bar falon, yadda ya ɗan shagala yana kallon iman ne ya sanya ammi jinjina kai a ranta ta ce "Yaushe wannan lamarin kuma ya kunno kai? Akwai ƙura idan Hajiya Lubabatu ta sani, amma da zan so faruwar hakan jabir ba shi da matsala'
"To ya gidan ya hajiyar taka?"
"Tana nan ƙalau Ammi, na je na duba Mahmud ne, na ji abun da ya faru sam bai yi mini daɗi ba ammi"
Ammi ta nemi wuri ta zauna ta ce "Kai dai bari jabir, lamarin É—an uwan nan na ku sai addu'a kawai, dan ku din ga yi masa faÉ—a, yanzu a garin wannan zafin zuciyar ta sa da ya yi masa illla ko ha salwantar masa da rayuwa fa?"
"Kai, ai takawa sai haƙuri, iya masa sai Allan da ya yi shi, amma iya ƙoƙari muna gaya masa gaskiya, sai dai ayi ta yi masa addu'a, Allah ya yaye masa wannan azababbiyar zuciyar"
"To Amin, Allah ya iya mana"
Nan suka cigaba da hira da shi da ammi, sai dai hankalinsa ya fi karkata ga yadda yake jin iman a ransa.
***
Cike da zullumi Samha ke cin abincin da yake gabanta, ba dan yana yi mata daÉ—i ba, sai domin zullumin abun da Jamil zai zo ya gaya mata, tun da ya gaya mata sun yi magana da turaki adam zai yi aure ta rasa nutsuwarta, so take ya zo ya gaya mata idan har hakan da gaske ne.
"Wai Samha ba zaki kwantar da hankalinki, ki nutsu ki ci abincin nan ba, sai jagwalgwala shi ki ke yi?"
Samha ta ce "Mama yaya jamil nake jira, hankalina ba zai kwanta ba sai na ji abun da nake son ji".
Ƙanwar Samha, wadda daga ita sai ita mai suna Zainab ta ce "Ni wallahi Samha mamaki ki ke bani, wallahi babu yadda za a yi namiji yayi mini abun da Adam yayi mini na sake kallonsa, ke kam kamar mara zuciya, shiyasa na koma zaman hostel ma na bar miki gidan, yadda ki ke zubar da classic ɗin ki a kan gayen nan yana bani haushi, kamar wani ɗan gold"
"Enough zainab, kar ki sake saka mini baki a maganata, idan ba so ki ke na yi miki rashin mutunci ba".
Mama ta ce "Ya isa haka, ni bana son faÉ—a, daga dawowarki".
"Mama kin san dai babu yadda za a yi ina ganin gaskiya in ƙi faɗa, Allah ya taimaki soyayyar wahala" ta ƙarasa maganar tana tashi ta bar dining ɗin.
Samha gaba É—aya ba ta yanayi na yin faÉ—a, dan haka ba ta tankawa zainba ba ta shareta.
Jamil ne yayi sallama, mama ta amsa masa, Samha kuwa kasa amsa masan ta yi sai bin sa da ido da ta yi.
Ya nemi wuri ya zauna a É—aya daga cikin jerin kujerun falon.
Samha ta taso cikin sauri, ta ce "Yaya Jamil ya ake ciki ne? Tun É—azu nake jiranka"
Yayi shiru bai ce mata komai ba, "Yaya magana nake fa"
Ba tare da ya kalleta ba, ya ce "Samha ki na ji na?"
"Eh ina jin ka"
Ya taso ya zauna sosai ya ce "Samha, ina son ki saurareni da kyau, ki yi haƙuri ki cire Adam a ranki, a wannan karon ma ba zai aureki ba, domin kuwa ya tabattar mini da cewa mahaifiyarsa ta zaɓa masa wata matar, kuma turaki na dawowa za a kai masa kuɗin aure"
Ras! Gaban Samha ya faɗi, ta dafe ƙirjinta ta ce "What, again ta sama mata? Iman ko? Iman ce na sani, wai dan Allah me na yi wa matar nan ta tsaneni haka? A wancan karon ma ita ta yi uwa da makarɓiya ban auri Adam ba, a wannan karon ma ta kuma yi mini, na san ba wadda za ta zaɓa masa sai Iman"
Mama ta ce "To, ai a wannan karon sai ki kwantar da hankalinki, tun da an kuma kwatawa, sun nuna muraran ba sa ƙaunarki, sai ki ƙyale mata ɗanta ko?"
Samha ba ta iya cewa komai ba kawai ta tafi ɗakint, tamkar wadda take shirin zarewa, kaiwa ta din ga yi tana komowa a ɗakin, cikin zafin rai ta furta "Giwa me na yi miki, ki ke ƙyamar haɗa zuriya da ni ne? To wallahi a wannan karon ba zan yadda ba, ko ni ko ke ko mu rasa Adam daga ni har ke, har wadda zaki aura masan" ta yi maganar tana zubewa a kan gadonta cikin ƙunar rai.
***
Dukan teburin gabansa yayi, tare da tura kujerar da yake kai baya, ya ce "Aikin banza kawai, wai shi adam ɗin wanene da ganin ƙarshensa ya gagara, duk wannan abubuwan da aka yi a kansa, na gidajen jaridu da social media, yayi burus ya ƙi cewa uffan, sai ma wasu da yake turowa suna kare shi, wannan wane irin abu ne haka, ta ina kuma ya rage a ɓullo masa?"
Usman wakili yayi murmushi ya ce "Yaro man kaza, kai fa ka ce da na sakar maka ragamar komai, zaka iya komai ka san ta yadda zaka ɓullowa lamarin"
Daga haka Adam ya fice ya bar Jamil a tsaye da buÉ—aÉ—É—en baki.
Ammi kuwa waya suke yi da rumaisa, rumaisa tana ba ta labarin yadda takawa ya fito da Aliyu bayan rigimar da suka yi aka rufe shi, wanda shi Adam É—in sam bai gaya mata ba.
Ammi ta jinjina al'amarin, tare da yi mata Allah ya kyauta.
Gaba ɗaya rumaisa ba ta san wani abu wai kunyar suruka ba, mama na ta ƙifta mata ido, amma sosai take ta yi wa ammi surutu.
Ammi ta numfasa ta ce "Rumaisa na bayar da saƙo a kawo miki ki ka ƙi karɓa ko?"
Rumaisa ta ce "Laa ashe da gaske yake, na zata shi ya bani, na ce ba zan karɓa ba, bana son wataran yayi mini gori"
"Ahh haba dai, ba zai taɓa yi miki gori ba, duk abun da ya baki ki karɓa ba zai cutar da ke ba, sannan ki din ga yi muku Addu'a a kan lamarin auren nan na ku, turaki na daf da dawowa".
Ita gaba É—aya ma ta manta da maganar auren, sai yanzu da ammin ta tuna mata.
"To, ammi kin san wani abu?"
Ammi ta ce "Sai kin faÉ—a"
"Kewar sabir nake yi sosai, daurewa nake yi dan kar na din ga takura muku"
Ammi ta ce "Subhanallah, rumaisa zan ci gidanku fa, ni akwai wani abu mai kama da takura tsakanina da ke, ba ni na ce duk lokacin da ki ke so ki gaya mini a kawo shi ba? Za'a kawo miki shi ranar da babu makaranta, na san shi ma yana kewarki".
Rumaisa ta yi murmushi ta ce "To ammi, na gode sosai ki gaida kowa da kowa"
"Yauwwa ko ke fa, za su ji in sha Allah" Ammi ta katse wayar tana murmushi.
A can falo kuwa, Iman ce take bawa sabir abinci, an fara gwada masa abu mai ruwa-ruwa.
Baba uwani na ta tsokanar iman "Ohh tsakanin uwa da É—a sai Allah, tsakanin Sabir da iman sai Allah"
Iman ta yi murmushi ta ce "Tsakanin kaka da jikarta ma sai Allah ba"
Baba uwani ta ce "Uhumm kakar da yake yi wa ƙyuya, daga ke sai ammi sai babansa, sai kuma Nusaiba idan ya ga dama, yaro ba ya yadda da kowa"
"Kar ki damu baba uwani, zai yadda da ke ne"
"Mhmm, ni kuwa Iman, ina yarinyar da aka ce ta tsinci yaron nan, Haryanzu tana nan kuwa?"
"Laa tana nan baba uwani, baki taɓa ganinta ba?"
"Oho, yo ni a ina zan ganta ma"
Iman ta ce "Kai haba, ta zazzo gidan nan fa sosai da sosai, ai duk ƙyuyar nan da yake yi, ba ya yi mata, dariya sosai ke ba kya ce shine ba".
Baba uwani cikin son bugun ciki da gulma, ta sake ƙasa da murya ta ce "Ni kuwa wai babba ce ko yarinya?"
"Gaskiya Yarinya ce sosai, dan duk mun girmeta"
"Ikon Allah, Æ´ar nan unguwar ce kuma? Na ji kin ce tana zuwa gidan nan, ai ni fa ban zaci ma Æ´ar nan garin ce ba".
"A'a ba unguwar nan take ba, zuwa take yi, amma kwana biyu ma ba ta zo ba".
"Ikon Allah, ni kuwa dan Allah duk ranar da Allah ya kawota ki nuna mini ita"
Iman ta yi murmushi ta ce "Maman sabir, to shikenan in sha Allah" Baba uwani ta yi gaba tana jin alamun nasara.
Tafiyar baba uwani babu jimawa, sai ga Jabir yayi sallama, cikin sauri Iman ta rufe kanta da hula, ta gyara zamanta, tare da mayar da hankalinta sosai a kan Sabir.
Murmushi Jabir yayi, ya ƙarasa kusa da ita ya zauna ya ce "Gashin ake yi mini rowar gani kuma?" Ta yi masa shiru ba ta ce komai ba.
"Talk mana iman, ko miskilanci ne?"
Ta yi masa shiru, ta cigaba da bawa Sabir abinci, Jabir ya miƙe hannu ya ɗauki Sabir, yana ƙure Iman da wani irin kallo, wani irin abu yana fuzgar zuciyarsa game da ita.
Wuyanta yake bi da kallo, ya haÉ—iye wani irin yawu, ya zaunar da sabir a jikinsa, amma Sabir ya ce bai san zance ba ya sanya kuka.
"Ka bani shi abinci nake ba shi".
"Ba zan baki ba, sai kin kalleni kin amsa mini"
Ammi ce ta fito falon, cikin fara'a ta ce "Jabir, kwana biyu ina ka ɓuya ne?"
Yayi murmushi ya ce "Tuba nake ammi, ayyuka ne suka yi mini yawa sosai"
Ammi ta kalli Sabir ta ce "Rigimamme, kai ba ka gane iyayenka ne, kowa ma ba zai É—auke ka ba?"
Iman ta tashi daga kan kujerar, ta karɓi Sabir ta bar falon, yadda ya ɗan shagala yana kallon iman ne ya sanya ammi jinjina kai a ranta ta ce "Yaushe wannan lamarin kuma ya kunno kai? Akwai ƙura idan Hajiya Lubabatu ta sani, amma da zan so faruwar hakan jabir ba shi da matsala'
"To ya gidan ya hajiyar taka?"
"Tana nan ƙalau Ammi, na je na duba Mahmud ne, na ji abun da ya faru sam bai yi mini daɗi ba ammi"
Ammi ta nemi wuri ta zauna ta ce "Kai dai bari jabir, lamarin É—an uwan nan na ku sai addu'a kawai, dan ku din ga yi masa faÉ—a, yanzu a garin wannan zafin zuciyar ta sa da ya yi masa illla ko ha salwantar masa da rayuwa fa?"
"Kai, ai takawa sai haƙuri, iya masa sai Allan da ya yi shi, amma iya ƙoƙari muna gaya masa gaskiya, sai dai ayi ta yi masa addu'a, Allah ya yaye masa wannan azababbiyar zuciyar"
"To Amin, Allah ya iya mana"
Nan suka cigaba da hira da shi da ammi, sai dai hankalinsa ya fi karkata ga yadda yake jin iman a ransa.
***
Cike da zullumi Samha ke cin abincin da yake gabanta, ba dan yana yi mata daÉ—i ba, sai domin zullumin abun da Jamil zai zo ya gaya mata, tun da ya gaya mata sun yi magana da turaki adam zai yi aure ta rasa nutsuwarta, so take ya zo ya gaya mata idan har hakan da gaske ne.
"Wai Samha ba zaki kwantar da hankalinki, ki nutsu ki ci abincin nan ba, sai jagwalgwala shi ki ke yi?"
Samha ta ce "Mama yaya jamil nake jira, hankalina ba zai kwanta ba sai na ji abun da nake son ji".
Ƙanwar Samha, wadda daga ita sai ita mai suna Zainab ta ce "Ni wallahi Samha mamaki ki ke bani, wallahi babu yadda za a yi namiji yayi mini abun da Adam yayi mini na sake kallonsa, ke kam kamar mara zuciya, shiyasa na koma zaman hostel ma na bar miki gidan, yadda ki ke zubar da classic ɗin ki a kan gayen nan yana bani haushi, kamar wani ɗan gold"
"Enough zainab, kar ki sake saka mini baki a maganata, idan ba so ki ke na yi miki rashin mutunci ba".
Mama ta ce "Ya isa haka, ni bana son faÉ—a, daga dawowarki".
"Mama kin san dai babu yadda za a yi ina ganin gaskiya in ƙi faɗa, Allah ya taimaki soyayyar wahala" ta ƙarasa maganar tana tashi ta bar dining ɗin.
Samha gaba É—aya ba ta yanayi na yin faÉ—a, dan haka ba ta tankawa zainba ba ta shareta.
Jamil ne yayi sallama, mama ta amsa masa, Samha kuwa kasa amsa masan ta yi sai bin sa da ido da ta yi.
Ya nemi wuri ya zauna a É—aya daga cikin jerin kujerun falon.
Samha ta taso cikin sauri, ta ce "Yaya Jamil ya ake ciki ne? Tun É—azu nake jiranka"
Yayi shiru bai ce mata komai ba, "Yaya magana nake fa"
Ba tare da ya kalleta ba, ya ce "Samha ki na ji na?"
"Eh ina jin ka"
Ya taso ya zauna sosai ya ce "Samha, ina son ki saurareni da kyau, ki yi haƙuri ki cire Adam a ranki, a wannan karon ma ba zai aureki ba, domin kuwa ya tabattar mini da cewa mahaifiyarsa ta zaɓa masa wata matar, kuma turaki na dawowa za a kai masa kuɗin aure"
Ras! Gaban Samha ya faɗi, ta dafe ƙirjinta ta ce "What, again ta sama mata? Iman ko? Iman ce na sani, wai dan Allah me na yi wa matar nan ta tsaneni haka? A wancan karon ma ita ta yi uwa da makarɓiya ban auri Adam ba, a wannan karon ma ta kuma yi mini, na san ba wadda za ta zaɓa masa sai Iman"
Mama ta ce "To, ai a wannan karon sai ki kwantar da hankalinki, tun da an kuma kwatawa, sun nuna muraran ba sa ƙaunarki, sai ki ƙyale mata ɗanta ko?"
Samha ba ta iya cewa komai ba kawai ta tafi ɗakint, tamkar wadda take shirin zarewa, kaiwa ta din ga yi tana komowa a ɗakin, cikin zafin rai ta furta "Giwa me na yi miki, ki ke ƙyamar haɗa zuriya da ni ne? To wallahi a wannan karon ba zan yadda ba, ko ni ko ke ko mu rasa Adam daga ni har ke, har wadda zaki aura masan" ta yi maganar tana zubewa a kan gadonta cikin ƙunar rai.
***
Dukan teburin gabansa yayi, tare da tura kujerar da yake kai baya, ya ce "Aikin banza kawai, wai shi adam ɗin wanene da ganin ƙarshensa ya gagara, duk wannan abubuwan da aka yi a kansa, na gidajen jaridu da social media, yayi burus ya ƙi cewa uffan, sai ma wasu da yake turowa suna kare shi, wannan wane irin abu ne haka, ta ina kuma ya rage a ɓullo masa?"
Usman wakili yayi murmushi ya ce "Yaro man kaza, kai fa ka ce da na sakar maka ragamar komai, zaka iya komai ka san ta yadda zaka ɓullowa lamarin"