Sashe 38
Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Waiwaya ta yi, ta kalli mai sunan Baba da ya shimfiÉ—a tabarma ya baje litattafai yana dubawa, ta kalli Abubakar, ta kai bakinta kunnensa ta ce "Wallahi hussaininka ya É—au hakkina, ba dan yayana bane ba ko? Hmmm"
Ya kalli mai sunan Baba ya yi murmushi ya ce "Kai, a wani dalilin ya sa ka É—aga mana hankali haka fisabilillahi?" Ko É—agowa bai yi ba, balle ya kallesu. Ruma ta kama hannunsa suka shiga É—akin mama.
Mama ta ce "Ta barka ka ƙaraso in ganka kenan? Na ga ta je ta tsareka da zance, kamar ba yanzu ta gama kuka da neman taimako ba"
Abubakar ya yi murmushi, ya zauna ya ce "Sannu da gida Hajiya mama, uwar 'yan maza da 'yar budurwa, na sameku lafiya?"
Mama ta yi murmushi ta ce "Lafiya lau Alhamdilillah, amma ba ka da lafiya ne?"
Ya É—an kalli jikinsa sannan ya ce "Me ki ka gani?"
"To ai ganinka nayi wuri-wuri duk ka rame Saddiƙu"
Ya shafi sumar kansa da taru sosai ya ce "Mama wannan karatun namu, ai ba sauƙi ne da shi ba, pressure ce kawai, ruma zubo mini abinci" miƙewa ruma ta yi, ta fita ta kawo masa kulolin abincin ta dire masa, ta zauna ta saka shi a gaba, tana ta zuba masa surutu, mama kuwa kallon yadda yake zira abincin nan yake babu ji babu gani, kai da ganin yadda yake cin abincin ka san akwai yunwa a tare da shi, ba dai ta ce komai ba suka cigaba da hira.
Da la'asar shi da mai sunan Baba suka tafi masallaci, bayan sun dawo kuma suka zauna a tsakar gida suna hira.
Ruma so take ta zauna da Yaya Abubakar, ta yi masa hira sosai dan ya fi kowa tsayawa ya saurareta, amma ta ga hankalinsa yana kan É—an uwansa.
Ganin ta zauna daga nesa tana ta kallonsu, ya sanya yaya Abubakar cewa "Ruma, É—auko comb ki zo mu yi tsifa, na ga kitson kanki ya tsufa" ta jinjina masa kai, ta shiga É—aki ta É—auko comb da kibiya ta kawo masa, ta zauna a kusa da shi, tana yi tana kallon fuskar Umar, dan kar ya hantareta ko ya koreta.
Yaya Abubakar ya karɓi kayan tsifar, ya kwantar da kanta a kan cinyarsa, ya fara tsfefe mata kai.
Rai a haɗe mai sunan Baba ya ce "Amma dai ka san bana son ƙazanta ko?"
"Ƙazantar me kuma?"
"Dan me zaka zo kusa da ni kana aikin gashi, ko ƙyanƙyami ba ka ji"
Abubakar ya yi murmushi ya ce "Kayi karatunka ka ƙyalemu mu yi tsifar mu" a hankali ruma ta fara lumshe ido, bacci yana ɗibarta, cikin gyangyaɗinta ta ji Abubakar yana cewa mai sunan Baba "Ka ga ƙoshin nan da na yi cikina har wani ciwo yake yi"
Mai sunan Baba ya kalle shi ya ce "Kamar yaya, da ba ka ƙoshi ne?"
"Wallahi Akhi rabona da Abinci kusan kwana biyu yau, a ƙafa fa na taho tasha, na samu mota na taho gida shi ma daga tasha na ninko, Allah ya haɗani da wani ɗan unguwar nan ya goyoni a babur"
Cikin mamaki Umar ya ce "Garin yaya?"
"Wallahi kamfanin 'yan chinan da muke yiwa aiki ne suka koremu, suka kawo mutanensu. Ni kuma na ga ban aiko da komai gidan nan ba, ta yaya zan bugo na faɗi matsala, na sayar da wayata na sai ƙarama ina ta fama, gashi mun kusa exam, shiyasa ban zo gida ba, shekaranjiya garrin kwaki na ci ko jiƙawa ban yi ba, na wahala a semester nan wallahi"
Umar yayi tsaki ya ce "Akhi kana da matsala, amma ko baka gaya wa mama ba, ni mai ya hana ka gaya mini, sai ka je ka kashe kan ka da yunwa, idan ba abinci ta yaya karatu zai yiwu?"
"Kai ba fa ban gaya maka ne dan ka yi mini masifa ba, ko nima ƙaninka ne?. Na tafi na barku kuma kuna ta fama da yadda zaku yi, ni ban muku ba, kuma na ɗoro muku matsala, gashi na yiwa yarinyar nan alƙawarin sabuwar jakar makaranta ban samu saya mata ba, har kunyarta nake ji wallahi".
Mai sunan Baba ya numfasa ya ce "Dole mu din ga gaya wa juna matsalolinmu, watarana sai labari, ni kaina abubuwan sai a hankali, na saya wa yarinyar nan sabuwar katifa kusan dubu talatin, ta ta ta lalace, da so nake na sauya mata makaranta, makarantar gwamnatin nan ba ta iya komai, an ce mini registration dubu Arba'in, duk term kuma dubu Ashirin da biyar, gashi muma an yi mana ƙarin kuɗin makaranta, ga komai ya yi tsada, rayuwar ƙasar nan sai dai Allah ya sassauta mana, ina jin su Huzaifa ma suna zancen zasu yi sauka, suma kusan dubu sittin ake nema su biyu, ga garin a tsaye yake cak, sai dai Allah ya iya mana kawai, ita kanta mama ba ƙaramin ƙoƙari take ba, yakamata ace zuwa yanzu ta fara hutawa, ta sha wahala domin mu rayu mu zama mutane".
Abubakar ya ce "Haka ne, amma komai lokaci ne, daga cikin godiyar da nake yiwa Allah shi ne kasancewar dukkaninmu Allah sa babu wani wanda yake fita ya É—auko mata magana a waje, ko ba komai hankalinta a kwance yake "
"Sai wannan abar" mai sunan Baba yayi maganar yana nuna ruma, da tayi pretending kamar bacci take.
"Ba wani É—aukar magana, guda nawa take"
"Kai ba zaka gane ba, da ta je ta karya 'yar mutane a makaranta, sai da aka kusa korarta, har wurin 'yan sanda aka kaita"
Abubakar ya waro ido ya ce "Autar"
"Hmm kai ba ka nan, ba ka san wainar da ake toyawa ba kawai, wannan yarinyar ba ta da kai sam, kullum cikin nemo magana take ana ta abin da za a ci"
"To a daina faÉ—a, gara ayi ta mata addu'a "
Mai sunan Baba ya ce "Ai Addu'ar ce kamar ba ta kamata, duk gidan nan babu mai ibada kamar mama, kuma babu wanda zai yi mata addu'a ta karɓu sama da wadda take mata, amma haryanzu shiru, kullum rashin jin ta gaba yake yi, ni tausayi take bani wasu lokutan, tana da zaɓe-zaɓen abinci, and we can't provide what she wants, kuma ba ta san babu ba, sai ta zauna tana kuka, wai an bata kunu ba suga, ko ba za ta ci tuwo ba, could you imagine?"
Abubakar yayi murmushi ya ce"Allah dai ya yassare mana, in sha Allah za su huta, ita da mama"
Ruma da ta yi bakamm ta na jin su, wani irin tausayinsu ne ya kama ta, wato duk wannan zare idon da hantarar da mai sunan Baba yake yi mata, yana son ta har yana tausayinta haka.
Tana wannan tunane-tunanen har baccin gaske ya yi awon gaba da ita, sai magariba ta tashi, Yaya Abubakar ya tsefe mata kai tas ya taje, dama ya saba yi mata tsifa idan har yana gari.
Duk in da suka gilma sai tayi ta kallonsu cike da jin tausayinsu, tabbas tun da ta buɗi ido a duniya, yayyen nan na ta maza kowa ƙoƙarinsa ya ga ya kawo abin da za a rufa kai asiri, haka mama kullum cikin faɗi tashi take.
Ta zubo abincin dare ta zauna tana kallon yadda kowa ke ta walwala kamar ba su da wata damuwa, ta zubawa su Mai sunan Baba ido, da suka zuba Abinci kwano É—aya, tausayin Abubakar ya kamata, da tuna yadda yake gaya wa É—an uwansa ya kwan biyu bai ci abinci ba, kuma ya sha garri ba ruwa balle suga, kuma ba wanda ya gayawa.
Ta kalli Abincin gabanta, Usman ya sayo kifi ya ɗora mata a kan abinci, kifin da shi bai ci ba, bai kuma bawa kowa ba sai ita, gefe ga ƙullin lemon fata da Aliyu ya shigo da shi, shi ma bai sha ba ita ya bawa.
A hankali ta ture abincin, ta shiga ɗaki ta zauna tayi shiru, sai kuka wani irin ƙauna da tausayin yayyen nata ya kamata.
Babu tsammani ta ga mama ta hasketa da fitila.
"Kukan me ki ke yi a duhu haka, ga abincin ki ba ki ci ba?"
Da sauri ta girgiza kai ta ce "Ba kuka nake ba"
"To me ki ke yi idan ba kuka ba, ƙarya nake kenan?"
"A'a mama ni fa ba kuka nake yi ba"
"To meya hana ki cin abinci ki ka dawo É—aki ki na kuka?"
Ta girgiza kai ta ce "ba komai"
"Wai ba ance miki batun auren nan wasa bane ba, shi ne ki ka cigaba da takura kanki, ba zaki tashi ki je ki ci abincin ba?"
"Ba magana ake yi miki ba, ko sai na zo kan ki?" Ta jiyo muryar Yaya Umar daga tsakar gida. Jiki na rawa ta taso ta fito.
Cikin haÉ—e rai ya ce "zauna ki cinye abincin nan, sai wani ciwon ya kama ki ki cazawa mutane"
Ƙoƙarin kai abincin bakinta take, amma ta kasa kuka ya kuma ƙwace mata.
Aliyu ne ya dubeta ya ce "Ko Abincin ne ba kya so, ki ke yiwa mutane kuka? Me zaki ci?"
"A'a zan ci"
"To kukan me ki ke yi?"
"Ku ƙyaleni dan Allah, na ƙoshi ne" tayi maganar tana share hawaye.
Abubakar ya ce "Ikon Allah, taso dawo nan kusa da ni, zo ki saka hannu mu ci namu abincin tare" ba ta son ɓata masa rai, dan haka ta tashi ta je kusa da shi ta zauna, ya dinga ɗebo abincin yana bata a baki tana karɓa yana rarrashinta ba tare da sanin dalilin kukan nata ba, sai dai ba rarrashin da yake yi mata ne ya sanya ta yi shiru ba, hararar da mai sunan Baba ya jefeta da ita ne, ta sanyata haɗiye kukan da take yi.
Haka ya dinga lallaɓa ruma, da kansa ya gyara mata wurin da zata kwanta, ya saka mata net, har da yi mata addu'a, hakan ya ƙara sanya tsananin tausayinsa a ranta.
Sai da ya tabattar ta ɗan nutsu, sannan ya tashi ya fita, Mai sunan baba kuwa sai tsaki yake yi, yana hararar Abubakar, ya san da ya yi wani yinƙuri na yiwa ruma tsawa, zasu yi faɗa.
Ya kalli mai sunan Baba ya yi murmushi ya ce "Kai, a wani dalilin ya sa ka É—aga mana hankali haka fisabilillahi?" Ko É—agowa bai yi ba, balle ya kallesu. Ruma ta kama hannunsa suka shiga É—akin mama.
Mama ta ce "Ta barka ka ƙaraso in ganka kenan? Na ga ta je ta tsareka da zance, kamar ba yanzu ta gama kuka da neman taimako ba"
Abubakar ya yi murmushi, ya zauna ya ce "Sannu da gida Hajiya mama, uwar 'yan maza da 'yar budurwa, na sameku lafiya?"
Mama ta yi murmushi ta ce "Lafiya lau Alhamdilillah, amma ba ka da lafiya ne?"
Ya É—an kalli jikinsa sannan ya ce "Me ki ka gani?"
"To ai ganinka nayi wuri-wuri duk ka rame Saddiƙu"
Ya shafi sumar kansa da taru sosai ya ce "Mama wannan karatun namu, ai ba sauƙi ne da shi ba, pressure ce kawai, ruma zubo mini abinci" miƙewa ruma ta yi, ta fita ta kawo masa kulolin abincin ta dire masa, ta zauna ta saka shi a gaba, tana ta zuba masa surutu, mama kuwa kallon yadda yake zira abincin nan yake babu ji babu gani, kai da ganin yadda yake cin abincin ka san akwai yunwa a tare da shi, ba dai ta ce komai ba suka cigaba da hira.
Da la'asar shi da mai sunan Baba suka tafi masallaci, bayan sun dawo kuma suka zauna a tsakar gida suna hira.
Ruma so take ta zauna da Yaya Abubakar, ta yi masa hira sosai dan ya fi kowa tsayawa ya saurareta, amma ta ga hankalinsa yana kan É—an uwansa.
Ganin ta zauna daga nesa tana ta kallonsu, ya sanya yaya Abubakar cewa "Ruma, É—auko comb ki zo mu yi tsifa, na ga kitson kanki ya tsufa" ta jinjina masa kai, ta shiga É—aki ta É—auko comb da kibiya ta kawo masa, ta zauna a kusa da shi, tana yi tana kallon fuskar Umar, dan kar ya hantareta ko ya koreta.
Yaya Abubakar ya karɓi kayan tsifar, ya kwantar da kanta a kan cinyarsa, ya fara tsfefe mata kai.
Rai a haɗe mai sunan Baba ya ce "Amma dai ka san bana son ƙazanta ko?"
"Ƙazantar me kuma?"
"Dan me zaka zo kusa da ni kana aikin gashi, ko ƙyanƙyami ba ka ji"
Abubakar ya yi murmushi ya ce "Kayi karatunka ka ƙyalemu mu yi tsifar mu" a hankali ruma ta fara lumshe ido, bacci yana ɗibarta, cikin gyangyaɗinta ta ji Abubakar yana cewa mai sunan Baba "Ka ga ƙoshin nan da na yi cikina har wani ciwo yake yi"
Mai sunan Baba ya kalle shi ya ce "Kamar yaya, da ba ka ƙoshi ne?"
"Wallahi Akhi rabona da Abinci kusan kwana biyu yau, a ƙafa fa na taho tasha, na samu mota na taho gida shi ma daga tasha na ninko, Allah ya haɗani da wani ɗan unguwar nan ya goyoni a babur"
Cikin mamaki Umar ya ce "Garin yaya?"
"Wallahi kamfanin 'yan chinan da muke yiwa aiki ne suka koremu, suka kawo mutanensu. Ni kuma na ga ban aiko da komai gidan nan ba, ta yaya zan bugo na faɗi matsala, na sayar da wayata na sai ƙarama ina ta fama, gashi mun kusa exam, shiyasa ban zo gida ba, shekaranjiya garrin kwaki na ci ko jiƙawa ban yi ba, na wahala a semester nan wallahi"
Umar yayi tsaki ya ce "Akhi kana da matsala, amma ko baka gaya wa mama ba, ni mai ya hana ka gaya mini, sai ka je ka kashe kan ka da yunwa, idan ba abinci ta yaya karatu zai yiwu?"
"Kai ba fa ban gaya maka ne dan ka yi mini masifa ba, ko nima ƙaninka ne?. Na tafi na barku kuma kuna ta fama da yadda zaku yi, ni ban muku ba, kuma na ɗoro muku matsala, gashi na yiwa yarinyar nan alƙawarin sabuwar jakar makaranta ban samu saya mata ba, har kunyarta nake ji wallahi".
Mai sunan Baba ya numfasa ya ce "Dole mu din ga gaya wa juna matsalolinmu, watarana sai labari, ni kaina abubuwan sai a hankali, na saya wa yarinyar nan sabuwar katifa kusan dubu talatin, ta ta ta lalace, da so nake na sauya mata makaranta, makarantar gwamnatin nan ba ta iya komai, an ce mini registration dubu Arba'in, duk term kuma dubu Ashirin da biyar, gashi muma an yi mana ƙarin kuɗin makaranta, ga komai ya yi tsada, rayuwar ƙasar nan sai dai Allah ya sassauta mana, ina jin su Huzaifa ma suna zancen zasu yi sauka, suma kusan dubu sittin ake nema su biyu, ga garin a tsaye yake cak, sai dai Allah ya iya mana kawai, ita kanta mama ba ƙaramin ƙoƙari take ba, yakamata ace zuwa yanzu ta fara hutawa, ta sha wahala domin mu rayu mu zama mutane".
Abubakar ya ce "Haka ne, amma komai lokaci ne, daga cikin godiyar da nake yiwa Allah shi ne kasancewar dukkaninmu Allah sa babu wani wanda yake fita ya É—auko mata magana a waje, ko ba komai hankalinta a kwance yake "
"Sai wannan abar" mai sunan Baba yayi maganar yana nuna ruma, da tayi pretending kamar bacci take.
"Ba wani É—aukar magana, guda nawa take"
"Kai ba zaka gane ba, da ta je ta karya 'yar mutane a makaranta, sai da aka kusa korarta, har wurin 'yan sanda aka kaita"
Abubakar ya waro ido ya ce "Autar"
"Hmm kai ba ka nan, ba ka san wainar da ake toyawa ba kawai, wannan yarinyar ba ta da kai sam, kullum cikin nemo magana take ana ta abin da za a ci"
"To a daina faÉ—a, gara ayi ta mata addu'a "
Mai sunan Baba ya ce "Ai Addu'ar ce kamar ba ta kamata, duk gidan nan babu mai ibada kamar mama, kuma babu wanda zai yi mata addu'a ta karɓu sama da wadda take mata, amma haryanzu shiru, kullum rashin jin ta gaba yake yi, ni tausayi take bani wasu lokutan, tana da zaɓe-zaɓen abinci, and we can't provide what she wants, kuma ba ta san babu ba, sai ta zauna tana kuka, wai an bata kunu ba suga, ko ba za ta ci tuwo ba, could you imagine?"
Abubakar yayi murmushi ya ce"Allah dai ya yassare mana, in sha Allah za su huta, ita da mama"
Ruma da ta yi bakamm ta na jin su, wani irin tausayinsu ne ya kama ta, wato duk wannan zare idon da hantarar da mai sunan Baba yake yi mata, yana son ta har yana tausayinta haka.
Tana wannan tunane-tunanen har baccin gaske ya yi awon gaba da ita, sai magariba ta tashi, Yaya Abubakar ya tsefe mata kai tas ya taje, dama ya saba yi mata tsifa idan har yana gari.
Duk in da suka gilma sai tayi ta kallonsu cike da jin tausayinsu, tabbas tun da ta buɗi ido a duniya, yayyen nan na ta maza kowa ƙoƙarinsa ya ga ya kawo abin da za a rufa kai asiri, haka mama kullum cikin faɗi tashi take.
Ta zubo abincin dare ta zauna tana kallon yadda kowa ke ta walwala kamar ba su da wata damuwa, ta zubawa su Mai sunan Baba ido, da suka zuba Abinci kwano É—aya, tausayin Abubakar ya kamata, da tuna yadda yake gaya wa É—an uwansa ya kwan biyu bai ci abinci ba, kuma ya sha garri ba ruwa balle suga, kuma ba wanda ya gayawa.
Ta kalli Abincin gabanta, Usman ya sayo kifi ya ɗora mata a kan abinci, kifin da shi bai ci ba, bai kuma bawa kowa ba sai ita, gefe ga ƙullin lemon fata da Aliyu ya shigo da shi, shi ma bai sha ba ita ya bawa.
A hankali ta ture abincin, ta shiga ɗaki ta zauna tayi shiru, sai kuka wani irin ƙauna da tausayin yayyen nata ya kamata.
Babu tsammani ta ga mama ta hasketa da fitila.
"Kukan me ki ke yi a duhu haka, ga abincin ki ba ki ci ba?"
Da sauri ta girgiza kai ta ce "Ba kuka nake ba"
"To me ki ke yi idan ba kuka ba, ƙarya nake kenan?"
"A'a mama ni fa ba kuka nake yi ba"
"To meya hana ki cin abinci ki ka dawo É—aki ki na kuka?"
Ta girgiza kai ta ce "ba komai"
"Wai ba ance miki batun auren nan wasa bane ba, shi ne ki ka cigaba da takura kanki, ba zaki tashi ki je ki ci abincin ba?"
"Ba magana ake yi miki ba, ko sai na zo kan ki?" Ta jiyo muryar Yaya Umar daga tsakar gida. Jiki na rawa ta taso ta fito.
Cikin haÉ—e rai ya ce "zauna ki cinye abincin nan, sai wani ciwon ya kama ki ki cazawa mutane"
Ƙoƙarin kai abincin bakinta take, amma ta kasa kuka ya kuma ƙwace mata.
Aliyu ne ya dubeta ya ce "Ko Abincin ne ba kya so, ki ke yiwa mutane kuka? Me zaki ci?"
"A'a zan ci"
"To kukan me ki ke yi?"
"Ku ƙyaleni dan Allah, na ƙoshi ne" tayi maganar tana share hawaye.
Abubakar ya ce "Ikon Allah, taso dawo nan kusa da ni, zo ki saka hannu mu ci namu abincin tare" ba ta son ɓata masa rai, dan haka ta tashi ta je kusa da shi ta zauna, ya dinga ɗebo abincin yana bata a baki tana karɓa yana rarrashinta ba tare da sanin dalilin kukan nata ba, sai dai ba rarrashin da yake yi mata ne ya sanya ta yi shiru ba, hararar da mai sunan Baba ya jefeta da ita ne, ta sanyata haɗiye kukan da take yi.
Haka ya dinga lallaɓa ruma, da kansa ya gyara mata wurin da zata kwanta, ya saka mata net, har da yi mata addu'a, hakan ya ƙara sanya tsananin tausayinsa a ranta.
Sai da ya tabattar ta ɗan nutsu, sannan ya tashi ya fita, Mai sunan baba kuwa sai tsaki yake yi, yana hararar Abubakar, ya san da ya yi wani yinƙuri na yiwa ruma tsawa, zasu yi faɗa.