Sashe 170
Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baba uwani ta waiwaya sannan ta ce "Ranki ya daɗe, muna cikin aiki muka ga ya biyota afujajan, a kan wani littafi, sai dai kan ya cimmata ta tura shi a wuta, na ji yana magana cewa, abun da ya shafi aisha ne, baki ga shaƙar da yayi mata ba, ƙarshe dai ya shiga da ita ɗakinsa, ya rufe su, sai yanzun nan ta fito".
Mummy ta ce "Good, kin fuskanci ya yi mata wani abu ne?"
"Ban san me yayi mata ba da ya rufe su, amma na ga ta fito tana kamar magagin bacci".
"Kin sanar da samha ne?"
"A'a Allah ya baki nasara".
"Kar ki sanar da ita komai, sai abun da na umarce ki".
"In Allah ya yarda".
"Ki koma, ki cigaba da sanya mini ido a kan duk wani motsinsu".
Baba uwani ta ce "An gama uwar É—akina". Ta katse wayar ta koma.
Adam kuwa ya yi sallar azahar, ya jingina da jikin gado, ya yi shiru yana tuna abubuwan da suka shuÉ—e, gaba É—aya jikinsa ya yi sanyi.
Kiraye-kirayen, sallar azahar ne ya tashi rumaisa, ta je ta yi alwala, ta saka kaya, ta tsaya a gaban mudubi, ta na kallon wuyanta, da ya shata yake mata zafi.
Shiru ta yi tana tunanin tabbas ta taɓa ganin wannan abun a mafarki, ko kuma ya taɓa faruwa.
"Wallahi sai na gaya wa mama, tun da kasheni zai yi, sai na gudu na bar gidan nan"
Can kuma sai wata zuciyar ta tunatar da ita, muddin mama ta ji a kan meye, ya yi mata abun da yayi mata, ba zata goya mata baya ba, faÉ—a za su yi, a bata rashin gaskiya, kuma a kirsheta ace sai ta faÉ—i abun da ta sani, bayan ta riga ta ce ita ba ta san komai ba.
'Subhanallah, na fasa faɗa, bari na yafe masa, wataran ya na da kirki, amma wallahi ko zai kasheni ba zan faɗa masa komai ba, sai lokacin da na ga dama, bari na lallaɓa na san yanzu ji yake kamar ya kashe ni' sai kuma ta ɗan yi shiru ta ce "To da ya shaƙe ni kuma sai na yi bacci, oho dai? Ta gama abun da Allah ya nufe ta da yi, ta yi salla ta fito dan yunwa take ji.
Adam ya tashi ya nufi É—akinta, domin ya duba ko ta na lafiya ta gama wartsakewa, sai dai ya jiyo motsi a kitchen.
Ya leƙa kitchen ɗin, ya hango ta taka kujera, tana saka ɗan wake, kamar babu abun da ya sameta.
Abun har mamaki ya bashi, kamar ya yi mata magana, sai kuma ya fasa ya fita.
Baba Uwani na ganin fitar Adam, ta lallaɓo ta hawo benen.
"Sannu Æ´ar nan, ina fatan bai yi miki komai ba?"
Rumaisa ta waiwayo ta kalli baba uwani ta ce "Yayi mini me?".
"Ai ganin yadda ya janyo ki ɗin nan, abun ya tsoratani, ke ma da ko me yake buƙata kin bashi kin wuce wurin, idan ransa ya ɓaci hankalinsa gushewa yake wasu lokutan, zai iya yi miki illa. Ko dai hakkinsa ki ka hana shi ne?"
Rumaisa ta juyo gaba ɗaya ta kalli baba uwani ta ce "Wane irin haƙƙi kuma?".
"A'a haƙƙin aure mana".
"Meye haƙƙin aure kuma?"
Baba uwani ta ce "Ahh shikenan, bari maganar kawai".
Har baba uwani za ta fita ta ce "Kenan papa da gaske maye ne?"
A razane baba uwani ta waiwayo ta ce "Me ki ka ce?"
"Kin ji me na ce ai".
"Ke waye ya gaya miki?"
Rumaisa ta ce "Ke ce ki ka gaya mini yanzu"
Baba uwani ta ce "Ke, yaushe na gaya miki? Ki ji tsoron Allah"
"Ke ki ka faÉ—a, wannan ne karo na biyu ki na gaya mini, zan kuma tambaye shi".
"Dan girman Allah ki rufa mini asiri, da wasa nake yi ma fa, dan Allah kar ki gaya masa"
Rumaisa ta juya ta cigaba da saka ɗan wakenta, baba uwani kuwa ta toshe baki ta na fatan, Allah ya sa kar garin neman gulma, ta janyo kwaɓarta ta yi ruwa, domin kuwa ta lura bayan ƙuriciya, har da wauta ke damun rumaisa.
***
"Hajiya Lubabatu, ki na free gobe in Allah ya kaimu". Mummy ta yi maganar da waya a kunneta.
"Ya aka yi ne?".
Mummy ta ce "wurin malam na gidan dutse, zaki rakani, akwai case ne".
Hajiya Lubabatu ta ce "Wane irin case kuma?".
"Ɗan maje ne ya turo mini saƙo, wai ya ji mai martaba zai wakilta turaki, zuwa taron bunƙasa al'adu da harsunan afrika, rainon burtaniya, wai ya ɗauki mutum biyu a matasan yaran nan ya tafi da su, kuma da alama za a samu cigaba, wai ya ji turaki ya ce har da Adam za ayi tafiyar".
Hajiya Lubabatu ta ce "To ba sai su yi ta yi ba"
"Ina ba fa zai yiwu ba, wai ke meyasa ki ke ɗaukar al'amuran nan da sauƙi, komai sai dai shi, duk wannan miyagun fentin da suke tare da shi, komai sai dai a saka shi, ke me zai hana a tafi da Jabir, ga mahmud, ga Jamil nan, ina su yarima jikokin mai marataba, duk ba a ɗau kowa ba sai shi? A dalilin me?".
"Kuma fa da gaskiyarki Jamila"
"Dan Allah ki shirya, na ga da yadda zai tafi ai".
"Ke dole ma, zan shigo da wuri ma yi maganar, ni Jabir ne yadda ki ka san an yi masa asiri,gaba É—aya hankalinsa ba ya kan harkar sarautar nan, mussman idan abu da adam a ciki, sai ka ce ya yi masa asiri".
"Ni ma na fuskanci kamar aikin da ake yi wa Mahmud ba kamar da ba, zamu haÉ—u kawai".
***
Ko da Adam ya dawo da yamma, ya iske ruma, tana kwance a doguwar kujera, tana kallon cartoon.
Ya kalleta ya na jiran ya ji ko za ta ce wani abu, suna haÉ—a ido ta galla masa harara, bai dai tanka mata ba, ya wuce É—akinsa.
Adam dai hatta abincin sa bai iya ci ba, yadda aka kawo su, haka ruma ta É—auka ta mayar musu.
bacci sai ɓarawo, kwana ya yi ya na juyi, kuma yau sai ya kasa tashi ya yi sallar dare kamar yadda ya saba, tasbihi ma sai ya kasa saɓanin da, sai ajiyar zuciya da istigfari, ji yake komai ya yi masa zafi, ba ya jin daɗin komai, ko abinci ya kasa ci, ya rasa ta ina zai fara.
Sai gefin asuba barcci ya É—auke shi, ana kiran salla shi ma ya tashi.
Ko da ya dawo daga sallar asuba, neman wuri ya yi ya zauna, ya cigaba da Adduoi, sai da rana ta É—aga, sannan ya tashi ya shiga wanka.
Har ya kammala shirinsa, bai ji motsin ruma ba, gashi yau Monday.
Gaba É—aya ba shi da kuzari, balle karsashi, ya nufi É—akinta.
Ta na tsaye a gaban mudubi, yau ta fara saka uniform ɗin ta, ta saka skirt ɗin ya zauna a jikinta cif, da taimakon jigidar da ke ɗaure a ƙugun na ta.
Ta saka ƴar cikin, ta ɗaga kai tana ƙarewa wuyanta kallo, ta na shafa wurin da ya yi mata rauni. Uniform ɗin sun yi mata kyau sosai.
ÆŠan gyaran murya ya yi ya ce "Haryanzu ba ki shirya ba, balle ki karya yau monday fa"
"Na gama shiryawa, uniform nake ƙarasa sakawa".
Ya juya ya tafi dining ya zauna, da niyyar ko yaya ya ci wani abu, dan ya na jin yunwa, amma ya ji bakinsa babu É—anÉ—ano.
Ta fito ta ajiye jakarta a kan kujera, ta nufo dining É—in.
Ta buɗe food flask ɗin abincin, soyayyiyar doya ce da miyar ƙwai.
Ta ce "Bari na yi bisimillah, na ci abincinka, yau ban yi girki ba, ko sallar asuba ba ka tashe ni ba, da safe na yi salla kuma alhaki a kan ka".
Ta kama kujera, ta haye saman dining ta zauna.
Kallon ta yake, yana jiran ta yi maganar abun da ya faru jiya, amma ya ga ba ta yi ba, ta haÉ—a shayi ta tura masa kofin gabansa, ta É—au na ta.
Jujjuya cokali ya din ga yi, amma ya gaza kai wa bakinsa ya sha.
"Wai da zafi ne shayin?" Bai ce mata komai ba, ya cigaba da kallon shayin.
"To in ƙara maka madara?" Sai a wannan karon ya girgiza mata kai alamar a'a.
"To ka sha mana, ka ci abincin"
A hankali ya kai kofin bakinsa, sai dai zuƙa ɗayan da ya yi, sai da yayi ta fama sannan ya haɗiye shi, ƙarshe ya tashi ya ce mata, ta same shi a mota.
Kasancewar rumaisa tana son shayi, haka ta haÉ—e nasa da nata ta shanye abun ta, ta É—auki jakarta, ta ga tasa jakar ma ya bar ta a wurin, ta É—auki jakarta da tasa, ta fita.
Ta tarar da shi, ya kifa kansa a sitiyarin motar, sai da ta buɗe motar, sannan ya ɗago. Idanunsa sun yi ja, kamar am zuba masa abu a cikin su, har sai da ta fara fargabar ko hayaƙin ne zai fara fitowa, amma ta ga idon ya tsaya a haka, ya fara jan motar a hankali.
"Wai zazzaɓi ka ke yi ne?" Bai amsa ba, sai lumshe ido da yake ya na buɗewa.
"Yauwwa papa ka san me? Na san ba zaka amsa ba, haka mai sunan baba yake yi, shiyasa bakomai ka ke yi mini na ji haushi ba, na san ka na ji na. Dan Allah ka sai mini lunch box mana, in din ga zuba abinci ina tafiya da shi makaranta".
"Lunchbox na Æ´an primary ne"ya faÉ—a a hankali.
"Eh, ni shi nake so, ƙarami mai kyau" tana cikin maganar traffic ta tsayar da su, sai ga mai alawar madara, rumaisa ta tsayar da shi ta kalli Adam ta ce "Papa ɗan sai mini". Ya kawar da kansa gefe, yana kallon wajen window.
Ta saka hannu ta zuge jakarsa da ke hannunta, ta ga kuɗi a ciki, ta ƙyalƙyale da dariya ta ce "Allah ya kama ka, ga jakarka a hannuna ai, na ranci dubu ɗaya, idan na gama makaranta, na samu aiki, salaryna na farko zan biyaka" sai da Adam ya kalleta jin abun da ta ce, ta bawa mai alwar madara, ta ce ya bata ta duka.
Mummy ta ce "Good, kin fuskanci ya yi mata wani abu ne?"
"Ban san me yayi mata ba da ya rufe su, amma na ga ta fito tana kamar magagin bacci".
"Kin sanar da samha ne?"
"A'a Allah ya baki nasara".
"Kar ki sanar da ita komai, sai abun da na umarce ki".
"In Allah ya yarda".
"Ki koma, ki cigaba da sanya mini ido a kan duk wani motsinsu".
Baba uwani ta ce "An gama uwar É—akina". Ta katse wayar ta koma.
Adam kuwa ya yi sallar azahar, ya jingina da jikin gado, ya yi shiru yana tuna abubuwan da suka shuÉ—e, gaba É—aya jikinsa ya yi sanyi.
Kiraye-kirayen, sallar azahar ne ya tashi rumaisa, ta je ta yi alwala, ta saka kaya, ta tsaya a gaban mudubi, ta na kallon wuyanta, da ya shata yake mata zafi.
Shiru ta yi tana tunanin tabbas ta taɓa ganin wannan abun a mafarki, ko kuma ya taɓa faruwa.
"Wallahi sai na gaya wa mama, tun da kasheni zai yi, sai na gudu na bar gidan nan"
Can kuma sai wata zuciyar ta tunatar da ita, muddin mama ta ji a kan meye, ya yi mata abun da yayi mata, ba zata goya mata baya ba, faÉ—a za su yi, a bata rashin gaskiya, kuma a kirsheta ace sai ta faÉ—i abun da ta sani, bayan ta riga ta ce ita ba ta san komai ba.
'Subhanallah, na fasa faɗa, bari na yafe masa, wataran ya na da kirki, amma wallahi ko zai kasheni ba zan faɗa masa komai ba, sai lokacin da na ga dama, bari na lallaɓa na san yanzu ji yake kamar ya kashe ni' sai kuma ta ɗan yi shiru ta ce "To da ya shaƙe ni kuma sai na yi bacci, oho dai? Ta gama abun da Allah ya nufe ta da yi, ta yi salla ta fito dan yunwa take ji.
Adam ya tashi ya nufi É—akinta, domin ya duba ko ta na lafiya ta gama wartsakewa, sai dai ya jiyo motsi a kitchen.
Ya leƙa kitchen ɗin, ya hango ta taka kujera, tana saka ɗan wake, kamar babu abun da ya sameta.
Abun har mamaki ya bashi, kamar ya yi mata magana, sai kuma ya fasa ya fita.
Baba Uwani na ganin fitar Adam, ta lallaɓo ta hawo benen.
"Sannu Æ´ar nan, ina fatan bai yi miki komai ba?"
Rumaisa ta waiwayo ta kalli baba uwani ta ce "Yayi mini me?".
"Ai ganin yadda ya janyo ki ɗin nan, abun ya tsoratani, ke ma da ko me yake buƙata kin bashi kin wuce wurin, idan ransa ya ɓaci hankalinsa gushewa yake wasu lokutan, zai iya yi miki illa. Ko dai hakkinsa ki ka hana shi ne?"
Rumaisa ta juyo gaba ɗaya ta kalli baba uwani ta ce "Wane irin haƙƙi kuma?".
"A'a haƙƙin aure mana".
"Meye haƙƙin aure kuma?"
Baba uwani ta ce "Ahh shikenan, bari maganar kawai".
Har baba uwani za ta fita ta ce "Kenan papa da gaske maye ne?"
A razane baba uwani ta waiwayo ta ce "Me ki ka ce?"
"Kin ji me na ce ai".
"Ke waye ya gaya miki?"
Rumaisa ta ce "Ke ce ki ka gaya mini yanzu"
Baba uwani ta ce "Ke, yaushe na gaya miki? Ki ji tsoron Allah"
"Ke ki ka faÉ—a, wannan ne karo na biyu ki na gaya mini, zan kuma tambaye shi".
"Dan girman Allah ki rufa mini asiri, da wasa nake yi ma fa, dan Allah kar ki gaya masa"
Rumaisa ta juya ta cigaba da saka ɗan wakenta, baba uwani kuwa ta toshe baki ta na fatan, Allah ya sa kar garin neman gulma, ta janyo kwaɓarta ta yi ruwa, domin kuwa ta lura bayan ƙuriciya, har da wauta ke damun rumaisa.
***
"Hajiya Lubabatu, ki na free gobe in Allah ya kaimu". Mummy ta yi maganar da waya a kunneta.
"Ya aka yi ne?".
Mummy ta ce "wurin malam na gidan dutse, zaki rakani, akwai case ne".
Hajiya Lubabatu ta ce "Wane irin case kuma?".
"Ɗan maje ne ya turo mini saƙo, wai ya ji mai martaba zai wakilta turaki, zuwa taron bunƙasa al'adu da harsunan afrika, rainon burtaniya, wai ya ɗauki mutum biyu a matasan yaran nan ya tafi da su, kuma da alama za a samu cigaba, wai ya ji turaki ya ce har da Adam za ayi tafiyar".
Hajiya Lubabatu ta ce "To ba sai su yi ta yi ba"
"Ina ba fa zai yiwu ba, wai ke meyasa ki ke ɗaukar al'amuran nan da sauƙi, komai sai dai shi, duk wannan miyagun fentin da suke tare da shi, komai sai dai a saka shi, ke me zai hana a tafi da Jabir, ga mahmud, ga Jamil nan, ina su yarima jikokin mai marataba, duk ba a ɗau kowa ba sai shi? A dalilin me?".
"Kuma fa da gaskiyarki Jamila"
"Dan Allah ki shirya, na ga da yadda zai tafi ai".
"Ke dole ma, zan shigo da wuri ma yi maganar, ni Jabir ne yadda ki ka san an yi masa asiri,gaba É—aya hankalinsa ba ya kan harkar sarautar nan, mussman idan abu da adam a ciki, sai ka ce ya yi masa asiri".
"Ni ma na fuskanci kamar aikin da ake yi wa Mahmud ba kamar da ba, zamu haÉ—u kawai".
***
Ko da Adam ya dawo da yamma, ya iske ruma, tana kwance a doguwar kujera, tana kallon cartoon.
Ya kalleta ya na jiran ya ji ko za ta ce wani abu, suna haÉ—a ido ta galla masa harara, bai dai tanka mata ba, ya wuce É—akinsa.
Adam dai hatta abincin sa bai iya ci ba, yadda aka kawo su, haka ruma ta É—auka ta mayar musu.
bacci sai ɓarawo, kwana ya yi ya na juyi, kuma yau sai ya kasa tashi ya yi sallar dare kamar yadda ya saba, tasbihi ma sai ya kasa saɓanin da, sai ajiyar zuciya da istigfari, ji yake komai ya yi masa zafi, ba ya jin daɗin komai, ko abinci ya kasa ci, ya rasa ta ina zai fara.
Sai gefin asuba barcci ya É—auke shi, ana kiran salla shi ma ya tashi.
Ko da ya dawo daga sallar asuba, neman wuri ya yi ya zauna, ya cigaba da Adduoi, sai da rana ta É—aga, sannan ya tashi ya shiga wanka.
Har ya kammala shirinsa, bai ji motsin ruma ba, gashi yau Monday.
Gaba É—aya ba shi da kuzari, balle karsashi, ya nufi É—akinta.
Ta na tsaye a gaban mudubi, yau ta fara saka uniform ɗin ta, ta saka skirt ɗin ya zauna a jikinta cif, da taimakon jigidar da ke ɗaure a ƙugun na ta.
Ta saka ƴar cikin, ta ɗaga kai tana ƙarewa wuyanta kallo, ta na shafa wurin da ya yi mata rauni. Uniform ɗin sun yi mata kyau sosai.
ÆŠan gyaran murya ya yi ya ce "Haryanzu ba ki shirya ba, balle ki karya yau monday fa"
"Na gama shiryawa, uniform nake ƙarasa sakawa".
Ya juya ya tafi dining ya zauna, da niyyar ko yaya ya ci wani abu, dan ya na jin yunwa, amma ya ji bakinsa babu É—anÉ—ano.
Ta fito ta ajiye jakarta a kan kujera, ta nufo dining É—in.
Ta buɗe food flask ɗin abincin, soyayyiyar doya ce da miyar ƙwai.
Ta ce "Bari na yi bisimillah, na ci abincinka, yau ban yi girki ba, ko sallar asuba ba ka tashe ni ba, da safe na yi salla kuma alhaki a kan ka".
Ta kama kujera, ta haye saman dining ta zauna.
Kallon ta yake, yana jiran ta yi maganar abun da ya faru jiya, amma ya ga ba ta yi ba, ta haÉ—a shayi ta tura masa kofin gabansa, ta É—au na ta.
Jujjuya cokali ya din ga yi, amma ya gaza kai wa bakinsa ya sha.
"Wai da zafi ne shayin?" Bai ce mata komai ba, ya cigaba da kallon shayin.
"To in ƙara maka madara?" Sai a wannan karon ya girgiza mata kai alamar a'a.
"To ka sha mana, ka ci abincin"
A hankali ya kai kofin bakinsa, sai dai zuƙa ɗayan da ya yi, sai da yayi ta fama sannan ya haɗiye shi, ƙarshe ya tashi ya ce mata, ta same shi a mota.
Kasancewar rumaisa tana son shayi, haka ta haÉ—e nasa da nata ta shanye abun ta, ta É—auki jakarta, ta ga tasa jakar ma ya bar ta a wurin, ta É—auki jakarta da tasa, ta fita.
Ta tarar da shi, ya kifa kansa a sitiyarin motar, sai da ta buɗe motar, sannan ya ɗago. Idanunsa sun yi ja, kamar am zuba masa abu a cikin su, har sai da ta fara fargabar ko hayaƙin ne zai fara fitowa, amma ta ga idon ya tsaya a haka, ya fara jan motar a hankali.
"Wai zazzaɓi ka ke yi ne?" Bai amsa ba, sai lumshe ido da yake ya na buɗewa.
"Yauwwa papa ka san me? Na san ba zaka amsa ba, haka mai sunan baba yake yi, shiyasa bakomai ka ke yi mini na ji haushi ba, na san ka na ji na. Dan Allah ka sai mini lunch box mana, in din ga zuba abinci ina tafiya da shi makaranta".
"Lunchbox na Æ´an primary ne"ya faÉ—a a hankali.
"Eh, ni shi nake so, ƙarami mai kyau" tana cikin maganar traffic ta tsayar da su, sai ga mai alawar madara, rumaisa ta tsayar da shi ta kalli Adam ta ce "Papa ɗan sai mini". Ya kawar da kansa gefe, yana kallon wajen window.
Ta saka hannu ta zuge jakarsa da ke hannunta, ta ga kuɗi a ciki, ta ƙyalƙyale da dariya ta ce "Allah ya kama ka, ga jakarka a hannuna ai, na ranci dubu ɗaya, idan na gama makaranta, na samu aiki, salaryna na farko zan biyaka" sai da Adam ya kalleta jin abun da ta ce, ta bawa mai alwar madara, ta ce ya bata ta duka.