Sashe 132
Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rumaisa ta ce "Ai ya tafi" mama ta harareta ta yi mata shiru, dan haryanzu ba ta huce ba, da abun da rumaisan ta aikata.
Usman ya ce "Ina saƙon da na ji ya ce ki tsaya ki karɓa?"
Ta kwaɓe fuska ta ce "Ni ban karɓa ba, cewa na yi ya koma da abun sa ba na so"
Cikin takaici ya ce "Dalla matsa ƴar baƙin ciki, ke da ba roƙarsa ki ka yi ba, kawai sai ki ƙi karɓowa"
"Taɓ, haka kurum yayi mini gori wataran"
"Uban waye ya ce miki wanda aka haifa a cikin arziki yana gori? Ai idan kin ga mai kuɗi yayi gori, to dama matsiyaci ne, daga baya yayi arzikin kuma wataƙila a tsiyarsa zai mutu" ba wani fahimtar abun da yake faɗa ta yi ba, ta shiga harkokin ta. Sai dai ta kasa sakin jikinta, duba da yadda mama ta haɗe rai, taƙi kulata.
Aliyu ya yi ta basu labarin irin abubuwan da malam shamsu ya din ga faɗa a kansu da rumaisa, na ɓatanci da yadda ya ziga a ka kulleshi, duk ba a same shi da makami ko wani laifi ba.
Usman ya ce "Gajiyayyen wahalalle, irinsu ne masu ƙarewa a tsiya, kuma idan bai yi wasa ba, sai na ɗaga shi na buga da ƙasa. Ai ni abun da gayen nan yayi masa ya burgeni wallahi, da ya ce shi ne uban ɗan kuma ya karɓi abun sa".
Rumaisa ta yi farat ta ce "Yauwwa, na ji ya ce wai shi ne yayi mini cikin, to dama shi cikin yin sa ake yi, yi wa mutum ciki ake yi"
Aliyu ya ce "Bismillahi, ashe haryanzu hankalin da saura".
Ganin kowa ya yi mata shiru ya sanya ta ce "Yaya usy baka bani amsa ba".
"To me zan ce miki, wai ke haryanzu kanki a tukunya yake, baki san meye rayuwa ba, baki san me yakamata ki din ga tambaya ba, Allah ya sa mai sunan baba ya ji ki, shi sai ya baki amsa"
"To me na yi daga tambaya?"
"Idan kun yi auren sai ya baki amsar"
Aliyu ya kalli usman ya ce "Kai fa wasu lokutan sai a hankali, kai ba ka ji kunya ba kake gaya mata hakan?".
"To yaya zan yi mata bayani, ita kai kamar computer abun da ka zuba mata kawai shi ta sani, idan suka yi auren ai aikace za ta gani"
Aliyu ya ce "Kaii usman lafiyarka kuwa? Kar ka gurɓata mata tunani malam"
Mama da ke ɗakin ta ce "Ke, ki taso ki zo ki kunno mini maganin sauro" mama ta kirata, dan katse waccan hirar da suke yi, dan idan aka zurafafa rumaisan ba ganewa zata yi ba, kuma wani zancen za ta ɓallo.
***
Yanayin fuskar Ammi kawai ya kalla, ya san akwai matsala.
A nutse ya ce "Ammi na dawo"
Ta kalleshi, ta kalli ledar hannunsa ta ce "Wannan ledar fa?"
Ya kalli ledar ya ce "Saƙon da ki ka bani ne, ta ƙi karɓa"
"Saboda me?" Ammi ta tambayeshi cike da tuhuma.
"Ta ce baku yi waya ba, baki ce mata zaki aika mata da saƙo ba, dan haka ba zata karɓi abun hannuna ba na zo daga na yi mata gori wataran"
ÆŠan jimm ta yi, ta wani fannin rumaisa tana da gaskiya, kuma ammi ta sake jinjina lallai rumaisa tana da tarbiyya.
"Dole fa ka sauke wannan shan ƙamshin, da sarautar ka dawo dai-dai level ɗin ta, domin ku fuskanci juna kai da ita, dan ba zan lamunci ku yi aure, ku din ga zaman doya da manja ba, kamar wasu maƙiya"
Adam ya ce "To in sha Allah" dan ya rasa mai zai cewa ammin.
Ta sake nisawa ta ce "Sannan na ji abun da ka aikata, Jamila ta zo har falon nan ta nuna ni da yatsa, ka saka mota zaka kashe mata ɗa, adam ƙiyayyar da ka ke yi wa ɗan uwanka har ta kai haka dama? Ka yi yinƙurin kashe shi?"
Adam ya yi shiru, ba tare da ƙoƙarin kare kansa ba.
"Kai a rayuwarka duk yadda nake tausaya maka, da yin iya ƙoƙarina a kan ka, baka gani ko? Kullum burinka ka tsokano abun da za ayi ta yi mana surutu, saboda wannan zafin zuciyar ta ka ko? Gobe in Allah ya kaimu ka je ka yi masa sannu, sannan ka bata haƙuri, magana kuma har ta kai kunnen wambai yana nemanka"
Dam ƙirjin Adam ya buga, ya je ya duba Mahmud, ya bawa Mummy haƙuri, sannan wambai yana nemansa.
Cikin dakiya ya ce "To, in sha Allah duk za a yi" ya juya ya fice daga É—akin.
Ko abinci kasa ci yayi, abubuwa sun yi masa zafi sosai kwanan nan, ya tara ayyuka sosai a office, gashi duk iya binciken da yake ya gano, ko garkuwa da aisha shiri ne ya kasa samun komai, amma wasu daga cikin bayanan rumaisa, na nuni kamar da akwai wani abu a ƙasa,gata gardamammiya ya san idan jajjagenta zai yi ba zata yi magana ba, sai ta ga dama. Ga wannan batun auren nasa da ammi ta sako shi a gaba a ƴan kwanakin nan, babu damar ya motsa, sai ta yi zancen rumaisa, shi gaba ɗaya baya farin ciki da wannan auren.
Ga surutan da ake ta yi a kansa a media, kullum ƙazafi kala-kala, ayyukansa da ya ɗauko kan sace Aisha hankalinsa ya rabu biyu duk yayi sanyi, bai samu sun kammalu ba, tun sa shi ne jagoran aikin.
Ji yayi kansa ya fara ciwo, ga wani irin jiri da ya fara É—ibarsa daga zaune, a hankali ya ja jikinsa ya kwanta, gaba É—aya bai san ta ina zai fara ba da matsalolin nasa.
***
Yau mama ko sallar asuba ba ta tashi ruma ba, sai da Usman ya tsula mata wayar caji a ƙafa ta tashi, ta yo alwala ta yi salla, ta gaida mama, amma maman taƙi amsawa.
"Mama wai dan Allah ba zaki kulani ba?" Ta yi maganar cikin damuwa.
"In kulaki in ce miki me? Ai ki je ki yi rayuwarki ruma nima zan yi tawa, ƴaƴana suna buƙatar rayuwata, ɓacin ranki ba zai ƙarasani ba, na yi magana a samo langa-langa ayi miki ɗakinki, dan ba zan cigaba da zama ɗaki ɗaya da ke, kina zucguna mini ba"
Ba ƙaramin mamaki mama ta bawa rumaisa ba, dan a ganinta mama ta daina sonta, ta tashi jiki a sanyaye, ta je yi shirin makaranta, ta tafi ba tare da ta sake kula mama ba, sai dai abun yayi ta damunta, ga wani irin son ganin sabir da take yi, ga kuma alwashin da ta ci a kan sa.
Ita kanta wasu fitintinun da take yi, tana son ta daina amma Allah ya gani, ba za a taɓa ta ta ƙyale ba.
Adam kuwa, Yau kamar wanda aka gayawa wani mummunan saƙo haka yake jin sa, komai ba ya yi masa daɗi, tasbihi kawai yake yi ko ya samu sassauci, ammi kuma ta sake nanata masa cewar ya je ya aiwatar da abun da ta ce na bawa Mummy haƙuri da duba Mahmud domin komai ya wuce.
Ba a son ransa ba sai domin cika umarnin ammi, ya nufi sashin Mummy.
Sai dai da ya tambayi Fauziyya, ta ce masa suna É—akin Mahmud.
Kai tsaye bai jira wani iso ba, ya shiga sashin da Mahmud yake, yana zaune a kan gado, an ɗaure ƙafarsa da bandeji, da alama ƙashin ƙafar ya taɓu, amma ba irin so serious ɗin nan ba.
Mummy na gefen Mahmud tana takura shi ya ci abinci.
Mummy ta wani haÉ—e rai, Mahmud ya yi wa Adam kallo É—aya, ya mayar kan abincinsa, aka rasa wanda zai amsa masa sallamar da yayi.
Hakan ba ƙatamkn ƙulara da shi ya yi ba , ya ji kamar yayi ficewarsa, amma ya san makircin Mummy.
Ya dubi Mummy ya ce "Na ji baki ji daɗin abun da ya faru ba, am sorry for it, shi kuma Allah ya bashi lafiya" ya juya zai fita Mummy ta ce "Dan Allah Adam wace irin ƙiyayyace kake nuna mana haka? Har ka taka ɗan uwanka da mota, meyake damunka ne?"
"Ba mayar da magana, ko bibiyar tarihi na zo mu yi ba, na baki haƙuri kar a sake saka mahaifiyata a duk wani abu da zan yi, ni na yi laifi ba ita ba"
"Amma Adam ni kake gayawa haka? Da na isa da kai, ko giwa ta nuna maka ina da muhimmanci a wurinka ai da ban tunkareta ba, kai zan yi wa sanin yi maka maganar ba shi da amfani, ba zaka saurara ba ya sanya na sameta".
"Kuma shine har da gayawa wambai? Idan haka ne maiyasa maganar ba ta tsaya iya nan ba?"
"Magana ake yi ta rai fa adam, yinƙurin taka shi da mota ka yi".
Mahmud ya ce "Mummy ki ƙyale shi dan Allah, kin san abnormal yake, kuma ko da ya takani da mota, za a iya ɓugewa da cewa ba shi da lafiyar ƙwaƙwalwa, sai dai zan sake ɗaukar nauyi, gidan jaridar fallasa su wallafa cewa ka yi yinƙirin takani da mota ka kashe ni" Mahmud yayi maganar cikin zunzurutun izgilanci.
A zafafe Adam ya juyo, ya ɓarar da kayan abincin, ya shaƙe Mahmud zuciyarsa na tafasa.
Mahmud ya kalli cikin idon Adam ya ce "Ka daina jin haushi idan an ce baka da lafiyar ƙwaƙwalwa, duk mutumin da bai iya sarrafa fushinsa ba, ƙwaƙwalwarsa babu lafiya ".
"Kai adam, ka cika shi kar ka kashe shi mana, jama'a ba kowa a kusa ne?" Mummy ta fara kwarmato.
Sanin cewa mutuncinsa zai sake zubewa, muddin aka sake zuwa aka gansu a yanayi mara daɗi shi da Mahmud, kuma ran ammi zai sake ɓaci, ya sanya shi sakin Mahmud, ya fice da sauri.
***
Maƙwabta suka yi ta shigowa yi wa mama jajen abun da ya faru, na kama Aliyu, sai dai a wannan karon mama a tsorace take da mutanen, dan kar su je su yi musu wani sharrin.
Usman ya ce "Ina saƙon da na ji ya ce ki tsaya ki karɓa?"
Ta kwaɓe fuska ta ce "Ni ban karɓa ba, cewa na yi ya koma da abun sa ba na so"
Cikin takaici ya ce "Dalla matsa ƴar baƙin ciki, ke da ba roƙarsa ki ka yi ba, kawai sai ki ƙi karɓowa"
"Taɓ, haka kurum yayi mini gori wataran"
"Uban waye ya ce miki wanda aka haifa a cikin arziki yana gori? Ai idan kin ga mai kuɗi yayi gori, to dama matsiyaci ne, daga baya yayi arzikin kuma wataƙila a tsiyarsa zai mutu" ba wani fahimtar abun da yake faɗa ta yi ba, ta shiga harkokin ta. Sai dai ta kasa sakin jikinta, duba da yadda mama ta haɗe rai, taƙi kulata.
Aliyu ya yi ta basu labarin irin abubuwan da malam shamsu ya din ga faɗa a kansu da rumaisa, na ɓatanci da yadda ya ziga a ka kulleshi, duk ba a same shi da makami ko wani laifi ba.
Usman ya ce "Gajiyayyen wahalalle, irinsu ne masu ƙarewa a tsiya, kuma idan bai yi wasa ba, sai na ɗaga shi na buga da ƙasa. Ai ni abun da gayen nan yayi masa ya burgeni wallahi, da ya ce shi ne uban ɗan kuma ya karɓi abun sa".
Rumaisa ta yi farat ta ce "Yauwwa, na ji ya ce wai shi ne yayi mini cikin, to dama shi cikin yin sa ake yi, yi wa mutum ciki ake yi"
Aliyu ya ce "Bismillahi, ashe haryanzu hankalin da saura".
Ganin kowa ya yi mata shiru ya sanya ta ce "Yaya usy baka bani amsa ba".
"To me zan ce miki, wai ke haryanzu kanki a tukunya yake, baki san meye rayuwa ba, baki san me yakamata ki din ga tambaya ba, Allah ya sa mai sunan baba ya ji ki, shi sai ya baki amsa"
"To me na yi daga tambaya?"
"Idan kun yi auren sai ya baki amsar"
Aliyu ya kalli usman ya ce "Kai fa wasu lokutan sai a hankali, kai ba ka ji kunya ba kake gaya mata hakan?".
"To yaya zan yi mata bayani, ita kai kamar computer abun da ka zuba mata kawai shi ta sani, idan suka yi auren ai aikace za ta gani"
Aliyu ya ce "Kaii usman lafiyarka kuwa? Kar ka gurɓata mata tunani malam"
Mama da ke ɗakin ta ce "Ke, ki taso ki zo ki kunno mini maganin sauro" mama ta kirata, dan katse waccan hirar da suke yi, dan idan aka zurafafa rumaisan ba ganewa zata yi ba, kuma wani zancen za ta ɓallo.
***
Yanayin fuskar Ammi kawai ya kalla, ya san akwai matsala.
A nutse ya ce "Ammi na dawo"
Ta kalleshi, ta kalli ledar hannunsa ta ce "Wannan ledar fa?"
Ya kalli ledar ya ce "Saƙon da ki ka bani ne, ta ƙi karɓa"
"Saboda me?" Ammi ta tambayeshi cike da tuhuma.
"Ta ce baku yi waya ba, baki ce mata zaki aika mata da saƙo ba, dan haka ba zata karɓi abun hannuna ba na zo daga na yi mata gori wataran"
ÆŠan jimm ta yi, ta wani fannin rumaisa tana da gaskiya, kuma ammi ta sake jinjina lallai rumaisa tana da tarbiyya.
"Dole fa ka sauke wannan shan ƙamshin, da sarautar ka dawo dai-dai level ɗin ta, domin ku fuskanci juna kai da ita, dan ba zan lamunci ku yi aure, ku din ga zaman doya da manja ba, kamar wasu maƙiya"
Adam ya ce "To in sha Allah" dan ya rasa mai zai cewa ammin.
Ta sake nisawa ta ce "Sannan na ji abun da ka aikata, Jamila ta zo har falon nan ta nuna ni da yatsa, ka saka mota zaka kashe mata ɗa, adam ƙiyayyar da ka ke yi wa ɗan uwanka har ta kai haka dama? Ka yi yinƙurin kashe shi?"
Adam ya yi shiru, ba tare da ƙoƙarin kare kansa ba.
"Kai a rayuwarka duk yadda nake tausaya maka, da yin iya ƙoƙarina a kan ka, baka gani ko? Kullum burinka ka tsokano abun da za ayi ta yi mana surutu, saboda wannan zafin zuciyar ta ka ko? Gobe in Allah ya kaimu ka je ka yi masa sannu, sannan ka bata haƙuri, magana kuma har ta kai kunnen wambai yana nemanka"
Dam ƙirjin Adam ya buga, ya je ya duba Mahmud, ya bawa Mummy haƙuri, sannan wambai yana nemansa.
Cikin dakiya ya ce "To, in sha Allah duk za a yi" ya juya ya fice daga É—akin.
Ko abinci kasa ci yayi, abubuwa sun yi masa zafi sosai kwanan nan, ya tara ayyuka sosai a office, gashi duk iya binciken da yake ya gano, ko garkuwa da aisha shiri ne ya kasa samun komai, amma wasu daga cikin bayanan rumaisa, na nuni kamar da akwai wani abu a ƙasa,gata gardamammiya ya san idan jajjagenta zai yi ba zata yi magana ba, sai ta ga dama. Ga wannan batun auren nasa da ammi ta sako shi a gaba a ƴan kwanakin nan, babu damar ya motsa, sai ta yi zancen rumaisa, shi gaba ɗaya baya farin ciki da wannan auren.
Ga surutan da ake ta yi a kansa a media, kullum ƙazafi kala-kala, ayyukansa da ya ɗauko kan sace Aisha hankalinsa ya rabu biyu duk yayi sanyi, bai samu sun kammalu ba, tun sa shi ne jagoran aikin.
Ji yayi kansa ya fara ciwo, ga wani irin jiri da ya fara É—ibarsa daga zaune, a hankali ya ja jikinsa ya kwanta, gaba É—aya bai san ta ina zai fara ba da matsalolin nasa.
***
Yau mama ko sallar asuba ba ta tashi ruma ba, sai da Usman ya tsula mata wayar caji a ƙafa ta tashi, ta yo alwala ta yi salla, ta gaida mama, amma maman taƙi amsawa.
"Mama wai dan Allah ba zaki kulani ba?" Ta yi maganar cikin damuwa.
"In kulaki in ce miki me? Ai ki je ki yi rayuwarki ruma nima zan yi tawa, ƴaƴana suna buƙatar rayuwata, ɓacin ranki ba zai ƙarasani ba, na yi magana a samo langa-langa ayi miki ɗakinki, dan ba zan cigaba da zama ɗaki ɗaya da ke, kina zucguna mini ba"
Ba ƙaramin mamaki mama ta bawa rumaisa ba, dan a ganinta mama ta daina sonta, ta tashi jiki a sanyaye, ta je yi shirin makaranta, ta tafi ba tare da ta sake kula mama ba, sai dai abun yayi ta damunta, ga wani irin son ganin sabir da take yi, ga kuma alwashin da ta ci a kan sa.
Ita kanta wasu fitintinun da take yi, tana son ta daina amma Allah ya gani, ba za a taɓa ta ta ƙyale ba.
Adam kuwa, Yau kamar wanda aka gayawa wani mummunan saƙo haka yake jin sa, komai ba ya yi masa daɗi, tasbihi kawai yake yi ko ya samu sassauci, ammi kuma ta sake nanata masa cewar ya je ya aiwatar da abun da ta ce na bawa Mummy haƙuri da duba Mahmud domin komai ya wuce.
Ba a son ransa ba sai domin cika umarnin ammi, ya nufi sashin Mummy.
Sai dai da ya tambayi Fauziyya, ta ce masa suna É—akin Mahmud.
Kai tsaye bai jira wani iso ba, ya shiga sashin da Mahmud yake, yana zaune a kan gado, an ɗaure ƙafarsa da bandeji, da alama ƙashin ƙafar ya taɓu, amma ba irin so serious ɗin nan ba.
Mummy na gefen Mahmud tana takura shi ya ci abinci.
Mummy ta wani haÉ—e rai, Mahmud ya yi wa Adam kallo É—aya, ya mayar kan abincinsa, aka rasa wanda zai amsa masa sallamar da yayi.
Hakan ba ƙatamkn ƙulara da shi ya yi ba , ya ji kamar yayi ficewarsa, amma ya san makircin Mummy.
Ya dubi Mummy ya ce "Na ji baki ji daɗin abun da ya faru ba, am sorry for it, shi kuma Allah ya bashi lafiya" ya juya zai fita Mummy ta ce "Dan Allah Adam wace irin ƙiyayyace kake nuna mana haka? Har ka taka ɗan uwanka da mota, meyake damunka ne?"
"Ba mayar da magana, ko bibiyar tarihi na zo mu yi ba, na baki haƙuri kar a sake saka mahaifiyata a duk wani abu da zan yi, ni na yi laifi ba ita ba"
"Amma Adam ni kake gayawa haka? Da na isa da kai, ko giwa ta nuna maka ina da muhimmanci a wurinka ai da ban tunkareta ba, kai zan yi wa sanin yi maka maganar ba shi da amfani, ba zaka saurara ba ya sanya na sameta".
"Kuma shine har da gayawa wambai? Idan haka ne maiyasa maganar ba ta tsaya iya nan ba?"
"Magana ake yi ta rai fa adam, yinƙurin taka shi da mota ka yi".
Mahmud ya ce "Mummy ki ƙyale shi dan Allah, kin san abnormal yake, kuma ko da ya takani da mota, za a iya ɓugewa da cewa ba shi da lafiyar ƙwaƙwalwa, sai dai zan sake ɗaukar nauyi, gidan jaridar fallasa su wallafa cewa ka yi yinƙirin takani da mota ka kashe ni" Mahmud yayi maganar cikin zunzurutun izgilanci.
A zafafe Adam ya juyo, ya ɓarar da kayan abincin, ya shaƙe Mahmud zuciyarsa na tafasa.
Mahmud ya kalli cikin idon Adam ya ce "Ka daina jin haushi idan an ce baka da lafiyar ƙwaƙwalwa, duk mutumin da bai iya sarrafa fushinsa ba, ƙwaƙwalwarsa babu lafiya ".
"Kai adam, ka cika shi kar ka kashe shi mana, jama'a ba kowa a kusa ne?" Mummy ta fara kwarmato.
Sanin cewa mutuncinsa zai sake zubewa, muddin aka sake zuwa aka gansu a yanayi mara daɗi shi da Mahmud, kuma ran ammi zai sake ɓaci, ya sanya shi sakin Mahmud, ya fice da sauri.
***
Maƙwabta suka yi ta shigowa yi wa mama jajen abun da ya faru, na kama Aliyu, sai dai a wannan karon mama a tsorace take da mutanen, dan kar su je su yi musu wani sharrin.