Sashe 136
Kanwar Maza 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Adam na shigowa da rumaisa ya fara tozali, ta taƙarƙare tana kankarar ƙanzon tukunya tana ci, kamar mayuwanciya, ga kuma abinci mai kyau a gaban iman, Sabir kamar zai shiga cikin tukunyar, yana son ya duntsi ƙanzon ya kai bakinsa.
Ayshercool.
08081012143
PAID BOOK NE, ₦500 VIA 0009450228,AISHA ADAM JAIZ BANK SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143.
Sallamar Adam bai hana rumaisa cigaba da taƙarƙarewa tana ƙwaƙwalar ƙanzo da cokali tana cin kayanta ba, ba ta da niyyar tashi ma ta saya jikinta, abun da ya dameta kawai take yi.
Usman da tun zuwan iman yana cikin ɗakinsu, ya leƙa ta window, ji yayi kamar ya fito ya kifawa rumaisa mari.
Adam ya wuce su, ya shiga wurin mama, Iman ta kalli rumaisa ta ce "Anty rumaisa baki gaida takawa ba?"
Ruma ta kwaɓe baki ta ce "Kin ga ya kulani ne?"
"Amma da kin yi masa magana zai kula ki"
Rumaisa ta ce "Wallahi ba zai amsa ba"
Cikin mamaki iman ta ce "Meyasa ki ka rantse"
Ruma ta ce "Mufa gidan nan babu mai kalar halin da babu, dan haka ko sau ɗaya na haɗu da mutum zan gane halinsa, ni ba dan Sabir ba kuma a daina ce mini ƴar iska ba, ba abun da zai saka na aure shi, kuma dai ina son ammi ita ma ina jin maganarta, amma wannan mak faɗan da zuciyar taɓ"
Iman ta ce "Wai ni, meyasa ba kwa shiri ne, wallahi takawa mutumin kirki ne sosai Anty rumaisa, ko wani abun yayi miki?"
"Hmm ba ruwanki a wannan faÉ—an"
Iman ta ce "Haka ne, faɗan masoya ne" aikuwa rumaisa ta ƙware da ƙanzo jin abun da iman ta ce, "Taɓ lallai kin tafka saɓo"
Iman ta kuma cewa "Allah Anty rumaisa, yaya Adam yana da kirki sosai, ki din ga yi masa uzuri, abubuwa sun saka shi a gaba, kawai kina ganinsa a haka ne, idan ki ka ji abubuwan da yake ciki sai kin tausaya masa".
Ruma ta taɓe baki ta ce "Da zai gane da ya daina ɗaukar damuwowinsa a zuciyarsa, babu abun da zasu ƙara masa sai nauyin zuciya, ya din ga ɗaukar damuwowinsa a ƙwaƙwalwarsa, ita ke da ma'aunin samar da mafita"
Mamaki ne ya kama Iman, jin rumaisa na wani lissafi, da ba ta gane ba.
"Ban gane me ki ke nufi ba".
"Kar ki damu, manta da ni kawai, bari na É—auko takarda da biro ki rubuta mini lambar wayarki, zan din ga kiranki muna hira".
Iman ta yi murmushi ta ce "Akwai jotter a jakata, bari na rubuta miki" Aikuwa ta rubutawa rumaisa lambarta, a lokacin rumaisa ta shagala da wasa da sabir, sai dariya yake yi.
A daidai lokacin Adam ya fito, mama ganin a yadda rumaisa ke zaune ba ƙaramin ƙular da ita ya yi ba.
Iman ta ce "Anty rumaisa kawo shi mu tafi" a take jikin rumaisa yayi sanyi, ta sake rungume Sabir.
Mama ta ce "Ke bana son shirme, ki ba ta shi su tafi"
Kawai ta fara kuka, hawaye wani na bin wani, wanda a ganin adam kawai shagwaɓa ce da wulaƙanci.
"Mama dan Allah a bar mini shi a nan, mu kwana tare" mama ba ta saurari rumaisa ba, ta karɓi sabir ta bawa iman.
Wadda jikinta yayi sanyi, tausayin rumaisa ya mamaye mata zuciya.
Kallon ruma da take kuka Sabir yake yi, Iman ta ce "Ka yi wa maminka bye-bye"
Kwaɓe baki ya shiga yi, zai yi kuka, Adam ya karɓe shi ya yi waje da shi, saboda haka nan ya ji tausayin su ya kama shi, wata irin Soyayya mai ban mamaki tsakanin yaro da zuciyar da ba ta uwassa ba.
Iman ta dafa kafaɗar rumaisa ta ce "Anty ruma ki yi haƙuri kin ji, da kun yi auren nan, za a dawo miki da sabir ɗinki, ki daina kuka" ruma ta jinjina mata kai ta ce "Ki gaida Ammi, da wannan ɗin nan mai kamar da baban sabir"
"Tom za su ji in sha Allah"
Suna tafiya mama ta dirarwa da rumaisa faɗa, mussaman a kan rashin hankalin da ta tafka, a gaban wanda zata aura ta taƙarƙare tana kankarar ƙanzo tana ci, babu ko kunya balle kawaici, ga wannan koke-koken na babu dalili da take yi, a duk lokacin da aka kawo sabir.
Ita dai rumaisa a wurinta, ba ta É—au adam wani na mussaman ba, balle idonsa ya hanata abun da take yi, tun da duk gidansu maza ne, ita ba ta É—au abun da ta yi wani laifi ba.
Maganar Sabir kuwa, ta barwa ranta cewa babu wanda ya san halin da take ciki sai Allah a kan yaron nan, dan haka ta daina damuwa a kan mitar da ake yi mata.
Usman ya fito yana faɗin "Bagidajiya kawai, wannan ai yawa ne ki ka yi, to wallahi nan gaba rainaki zai yi, sai la ce wata budurwar ƙauye, ke ba wani class bakomai"
Abdalla da bai daÉ—e da shigowa ba, ya tambayi mai ta yi, Usman ya gaya masa, ya ce "Kai yanzu har wani aji kake nema a wurin rumaisa, ai tun da suka ce za su aureta a haka, sai fatan Allah ya sanya su gama lafiya"
Ko a jikinta, an mintsini tattaura, abun da ya dameta kawai shi ne a gabanta.
***
Su Iman da suka koma gida kuwa, Ammi ba ta nan, Iman ba ta son ta fita ta koma gida ta tarar Ammi ba ta nan, gashi tare suka fita da Nusaiba, Kasancewar Sabir yayi bacci, da shi Adam ya tafi sashinsa ya kwantar da shi, Iman kuma ta wuce É—akinta.
Sai dai tana zuwa É—akin, ta yi tozali da Samha a tsaye, sai da ta razana ta ce "Anty Samha lafiya kuwa?".
"Ban sani ba, munafuka tsintacciyar mage da ba ta mage" cikin rashin fahimta iman take kallonta, dan ba ta san me ya kawo wannan maganar ba.
"Saboda tsohuwar munafuka ce, shi ne ki ka je ki ka cewa giwa kina son Adam, za a haÉ—a aurensa da ke a maimakon ni, duk da irin kashedin da na yi miki ko?"
Kamar zata yi kuka ta ce "Ni kuma?"
"Ke ɗin fa, algunguma ni zaki yi wa pretending, to ki rubuta ki ajiye, gidan Adam kabarinki ne, yadda aisha ta shige shi ta bar duniya, duk wadda ta shiga bani ba sai ta bita, idan ba haka ba kuwa ayi babu, kowa ya rasa daga ni har ke, da ni ki ke zancen, zan yi maganinki baƙar annamimiya"
Gaban Iman ya faÉ—i da jin furucin da Samha ta yi, tana gama zazzage mata ta yi waje.
Jikin iman har rawa yake yi, saboda tsananin tashin hankali, da yadda hankalinta ya dugunzuma, a take rumaisa ta faɗo mata, wato a zaton Samha Takawa ita zai aura, tausayin rumaisa ya kamata ya ruma za ta yi da wannan manyan al'amura ta ko ina, ga maƙiyan mijinta, ga tarin ƙalubalen gidan, ga kuma masifar Samha, a kaf dangin nan babu wanda bai sarawa masifar Samha ba, an shakkarta sosai da sosai, saboda a tsaye take ba ta da kunya, yaya rumaisa za ta yi da ita, ita da take yarinya ƙanƙanuwa?.
Rasa abun yi ta yi, ta saɓule ta zauna a kan gadonta, ƙirjinta na cigaba da dukan uku-uku saboda tsananin fargaba.
Mintuna kusan sha biyar da fitar Samha, amma iman ta kasa kataɓus, ƙirjinta sai cigaba da bugawa yake yi.
Nusaiba ce ta shigo da sallama ta ce "Ashe kun dawo, bamu zaci zaku rigamu dawowa ba, mun je sai wa Sabir kaya, kin san ya kusa 6months, Ammi sai nuna mini irin kayan da za a zubawa amaryar takawa a lefe take, ya kuka baro ta?" Sai da Nusaiba ta kai aya, sannan ta lura kamar Iman a tsorace take.
"Lafiya kuwa?"
Iman ta jinjina mata kai ta ce "Lafiya lau"
Nusaiba ta ce "Kin ga idonki kuwa kamar mara gaskiya, ko wani abun ya faru a gidan da ku ka je ne?" Iman ta girgiza kai alamar a'a.
"Tsaya, ko jikinki ne ya motsa?"
Iman ta yi ajiyar zuciya ta ce "Babu ko ɗaya, cikina ne ya ɓaci zuciyata ce take tashi"
Nusaiba ta sauke numfashi ta ce "Har kin tsorata ni, bari na kawo miki anti acid, ina da shi a É—akina" iman ta jinjina mata kai.
Da Nusaiba ta fita ta sanarwa da Ammi iman ba ta jin daÉ—i, ulcer ya tayar mata, a rikice ammin ta nufi É—akin Iman, ta je ta tutsiyeta tana tambayar ko jikinta ne ya motsa.
Kamar yadda ta yi wa Nusaiba ƙarya, haka ta dake, ta ɓoye damuwarta, ta tabattarwa da ammi, ulcer ne kawai ya tasar mata.
***
Kwanciya ce ta isheshi, musamman da kwana biyun nan, a gida yake wuni saboda ƙafarsa, amma yanzu ta yi saƙi sosai, kawai dai fita ce bai yi ba, gashi ya kusa komawa makaranta.
Kamar wanda aka tsikara, ya tashi ya fita falo, ya ɗau lemon kwali mai sanyin gaske, ya koma ɗakinsa, corridor ya nufa, ya buɗe tagar a hankali, wata sassanyar iska ta dake shi, ya zuƙe lemon tare da lumshe idanunsa.
Dare ne sosai, manyan security lights, sun haske ko ina na gidan, kukan tsuntsye na ta tashi, da ƙanan ƙwari, ga ƙamshim furannin harabar gidan sun gauraye da sassanyar iskar da ke kaɗawa.
Yanayin yayi masa daɗi sosai, sai dai babu tsammani ya ga wani abu yana dudduƙe, yana motsi ta jikin fulawoyin da zai sadaka da sashinsu.
Tsayawa yayi ya ƙura ido sosai, yanayin inuwar abun, kamar mace ce, dan har da lulluɓinta.
Mamaki ne ya kama Mahmud, ganin maimakon ta shigo direct ƙofa, ta kutsa can ƙarshen ginin da kai tsaye ɗakin Mummy zai kai ka.
Bai yi wata-wata ba ya sauka, ya nufi sashin Mummy a hankali, sai dai bai buÉ—e ya shiga ba.
"Kin shanya ni, tun É—azu nake zaman jiranki, amma baki zo ba"
Baba uwani ta risuna ta ce "Tuba nake Allah ya baki yawan rai, sawu ne bai gama É—aukewa ba"
Mummy ta hura hanci ta ce "Ina jinki, bani labari, meke wakana da ki ke son ganina?"
"Allah ya baki yawan rai, labari ne nake tafe da shi, idan yayi miki daÉ—i haka nake fata, idan bai yi ba ayi mini aikin gafara"
Ayshercool.
08081012143
PAID BOOK NE, ₦500 VIA 0009450228,AISHA ADAM JAIZ BANK SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143.
Sallamar Adam bai hana rumaisa cigaba da taƙarƙarewa tana ƙwaƙwalar ƙanzo da cokali tana cin kayanta ba, ba ta da niyyar tashi ma ta saya jikinta, abun da ya dameta kawai take yi.
Usman da tun zuwan iman yana cikin ɗakinsu, ya leƙa ta window, ji yayi kamar ya fito ya kifawa rumaisa mari.
Adam ya wuce su, ya shiga wurin mama, Iman ta kalli rumaisa ta ce "Anty rumaisa baki gaida takawa ba?"
Ruma ta kwaɓe baki ta ce "Kin ga ya kulani ne?"
"Amma da kin yi masa magana zai kula ki"
Rumaisa ta ce "Wallahi ba zai amsa ba"
Cikin mamaki iman ta ce "Meyasa ki ka rantse"
Ruma ta ce "Mufa gidan nan babu mai kalar halin da babu, dan haka ko sau ɗaya na haɗu da mutum zan gane halinsa, ni ba dan Sabir ba kuma a daina ce mini ƴar iska ba, ba abun da zai saka na aure shi, kuma dai ina son ammi ita ma ina jin maganarta, amma wannan mak faɗan da zuciyar taɓ"
Iman ta ce "Wai ni, meyasa ba kwa shiri ne, wallahi takawa mutumin kirki ne sosai Anty rumaisa, ko wani abun yayi miki?"
"Hmm ba ruwanki a wannan faÉ—an"
Iman ta ce "Haka ne, faɗan masoya ne" aikuwa rumaisa ta ƙware da ƙanzo jin abun da iman ta ce, "Taɓ lallai kin tafka saɓo"
Iman ta kuma cewa "Allah Anty rumaisa, yaya Adam yana da kirki sosai, ki din ga yi masa uzuri, abubuwa sun saka shi a gaba, kawai kina ganinsa a haka ne, idan ki ka ji abubuwan da yake ciki sai kin tausaya masa".
Ruma ta taɓe baki ta ce "Da zai gane da ya daina ɗaukar damuwowinsa a zuciyarsa, babu abun da zasu ƙara masa sai nauyin zuciya, ya din ga ɗaukar damuwowinsa a ƙwaƙwalwarsa, ita ke da ma'aunin samar da mafita"
Mamaki ne ya kama Iman, jin rumaisa na wani lissafi, da ba ta gane ba.
"Ban gane me ki ke nufi ba".
"Kar ki damu, manta da ni kawai, bari na É—auko takarda da biro ki rubuta mini lambar wayarki, zan din ga kiranki muna hira".
Iman ta yi murmushi ta ce "Akwai jotter a jakata, bari na rubuta miki" Aikuwa ta rubutawa rumaisa lambarta, a lokacin rumaisa ta shagala da wasa da sabir, sai dariya yake yi.
A daidai lokacin Adam ya fito, mama ganin a yadda rumaisa ke zaune ba ƙaramin ƙular da ita ya yi ba.
Iman ta ce "Anty rumaisa kawo shi mu tafi" a take jikin rumaisa yayi sanyi, ta sake rungume Sabir.
Mama ta ce "Ke bana son shirme, ki ba ta shi su tafi"
Kawai ta fara kuka, hawaye wani na bin wani, wanda a ganin adam kawai shagwaɓa ce da wulaƙanci.
"Mama dan Allah a bar mini shi a nan, mu kwana tare" mama ba ta saurari rumaisa ba, ta karɓi sabir ta bawa iman.
Wadda jikinta yayi sanyi, tausayin rumaisa ya mamaye mata zuciya.
Kallon ruma da take kuka Sabir yake yi, Iman ta ce "Ka yi wa maminka bye-bye"
Kwaɓe baki ya shiga yi, zai yi kuka, Adam ya karɓe shi ya yi waje da shi, saboda haka nan ya ji tausayin su ya kama shi, wata irin Soyayya mai ban mamaki tsakanin yaro da zuciyar da ba ta uwassa ba.
Iman ta dafa kafaɗar rumaisa ta ce "Anty ruma ki yi haƙuri kin ji, da kun yi auren nan, za a dawo miki da sabir ɗinki, ki daina kuka" ruma ta jinjina mata kai ta ce "Ki gaida Ammi, da wannan ɗin nan mai kamar da baban sabir"
"Tom za su ji in sha Allah"
Suna tafiya mama ta dirarwa da rumaisa faɗa, mussaman a kan rashin hankalin da ta tafka, a gaban wanda zata aura ta taƙarƙare tana kankarar ƙanzo tana ci, babu ko kunya balle kawaici, ga wannan koke-koken na babu dalili da take yi, a duk lokacin da aka kawo sabir.
Ita dai rumaisa a wurinta, ba ta É—au adam wani na mussaman ba, balle idonsa ya hanata abun da take yi, tun da duk gidansu maza ne, ita ba ta É—au abun da ta yi wani laifi ba.
Maganar Sabir kuwa, ta barwa ranta cewa babu wanda ya san halin da take ciki sai Allah a kan yaron nan, dan haka ta daina damuwa a kan mitar da ake yi mata.
Usman ya fito yana faɗin "Bagidajiya kawai, wannan ai yawa ne ki ka yi, to wallahi nan gaba rainaki zai yi, sai la ce wata budurwar ƙauye, ke ba wani class bakomai"
Abdalla da bai daÉ—e da shigowa ba, ya tambayi mai ta yi, Usman ya gaya masa, ya ce "Kai yanzu har wani aji kake nema a wurin rumaisa, ai tun da suka ce za su aureta a haka, sai fatan Allah ya sanya su gama lafiya"
Ko a jikinta, an mintsini tattaura, abun da ya dameta kawai shi ne a gabanta.
***
Su Iman da suka koma gida kuwa, Ammi ba ta nan, Iman ba ta son ta fita ta koma gida ta tarar Ammi ba ta nan, gashi tare suka fita da Nusaiba, Kasancewar Sabir yayi bacci, da shi Adam ya tafi sashinsa ya kwantar da shi, Iman kuma ta wuce É—akinta.
Sai dai tana zuwa É—akin, ta yi tozali da Samha a tsaye, sai da ta razana ta ce "Anty Samha lafiya kuwa?".
"Ban sani ba, munafuka tsintacciyar mage da ba ta mage" cikin rashin fahimta iman take kallonta, dan ba ta san me ya kawo wannan maganar ba.
"Saboda tsohuwar munafuka ce, shi ne ki ka je ki ka cewa giwa kina son Adam, za a haÉ—a aurensa da ke a maimakon ni, duk da irin kashedin da na yi miki ko?"
Kamar zata yi kuka ta ce "Ni kuma?"
"Ke ɗin fa, algunguma ni zaki yi wa pretending, to ki rubuta ki ajiye, gidan Adam kabarinki ne, yadda aisha ta shige shi ta bar duniya, duk wadda ta shiga bani ba sai ta bita, idan ba haka ba kuwa ayi babu, kowa ya rasa daga ni har ke, da ni ki ke zancen, zan yi maganinki baƙar annamimiya"
Gaban Iman ya faÉ—i da jin furucin da Samha ta yi, tana gama zazzage mata ta yi waje.
Jikin iman har rawa yake yi, saboda tsananin tashin hankali, da yadda hankalinta ya dugunzuma, a take rumaisa ta faɗo mata, wato a zaton Samha Takawa ita zai aura, tausayin rumaisa ya kamata ya ruma za ta yi da wannan manyan al'amura ta ko ina, ga maƙiyan mijinta, ga tarin ƙalubalen gidan, ga kuma masifar Samha, a kaf dangin nan babu wanda bai sarawa masifar Samha ba, an shakkarta sosai da sosai, saboda a tsaye take ba ta da kunya, yaya rumaisa za ta yi da ita, ita da take yarinya ƙanƙanuwa?.
Rasa abun yi ta yi, ta saɓule ta zauna a kan gadonta, ƙirjinta na cigaba da dukan uku-uku saboda tsananin fargaba.
Mintuna kusan sha biyar da fitar Samha, amma iman ta kasa kataɓus, ƙirjinta sai cigaba da bugawa yake yi.
Nusaiba ce ta shigo da sallama ta ce "Ashe kun dawo, bamu zaci zaku rigamu dawowa ba, mun je sai wa Sabir kaya, kin san ya kusa 6months, Ammi sai nuna mini irin kayan da za a zubawa amaryar takawa a lefe take, ya kuka baro ta?" Sai da Nusaiba ta kai aya, sannan ta lura kamar Iman a tsorace take.
"Lafiya kuwa?"
Iman ta jinjina mata kai ta ce "Lafiya lau"
Nusaiba ta ce "Kin ga idonki kuwa kamar mara gaskiya, ko wani abun ya faru a gidan da ku ka je ne?" Iman ta girgiza kai alamar a'a.
"Tsaya, ko jikinki ne ya motsa?"
Iman ta yi ajiyar zuciya ta ce "Babu ko ɗaya, cikina ne ya ɓaci zuciyata ce take tashi"
Nusaiba ta sauke numfashi ta ce "Har kin tsorata ni, bari na kawo miki anti acid, ina da shi a É—akina" iman ta jinjina mata kai.
Da Nusaiba ta fita ta sanarwa da Ammi iman ba ta jin daÉ—i, ulcer ya tayar mata, a rikice ammin ta nufi É—akin Iman, ta je ta tutsiyeta tana tambayar ko jikinta ne ya motsa.
Kamar yadda ta yi wa Nusaiba ƙarya, haka ta dake, ta ɓoye damuwarta, ta tabattarwa da ammi, ulcer ne kawai ya tasar mata.
***
Kwanciya ce ta isheshi, musamman da kwana biyun nan, a gida yake wuni saboda ƙafarsa, amma yanzu ta yi saƙi sosai, kawai dai fita ce bai yi ba, gashi ya kusa komawa makaranta.
Kamar wanda aka tsikara, ya tashi ya fita falo, ya ɗau lemon kwali mai sanyin gaske, ya koma ɗakinsa, corridor ya nufa, ya buɗe tagar a hankali, wata sassanyar iska ta dake shi, ya zuƙe lemon tare da lumshe idanunsa.
Dare ne sosai, manyan security lights, sun haske ko ina na gidan, kukan tsuntsye na ta tashi, da ƙanan ƙwari, ga ƙamshim furannin harabar gidan sun gauraye da sassanyar iskar da ke kaɗawa.
Yanayin yayi masa daɗi sosai, sai dai babu tsammani ya ga wani abu yana dudduƙe, yana motsi ta jikin fulawoyin da zai sadaka da sashinsu.
Tsayawa yayi ya ƙura ido sosai, yanayin inuwar abun, kamar mace ce, dan har da lulluɓinta.
Mamaki ne ya kama Mahmud, ganin maimakon ta shigo direct ƙofa, ta kutsa can ƙarshen ginin da kai tsaye ɗakin Mummy zai kai ka.
Bai yi wata-wata ba ya sauka, ya nufi sashin Mummy a hankali, sai dai bai buÉ—e ya shiga ba.
"Kin shanya ni, tun É—azu nake zaman jiranki, amma baki zo ba"
Baba uwani ta risuna ta ce "Tuba nake Allah ya baki yawan rai, sawu ne bai gama É—aukewa ba"
Mummy ta hura hanci ta ce "Ina jinki, bani labari, meke wakana da ki ke son ganina?"
"Allah ya baki yawan rai, labari ne nake tafe da shi, idan yayi miki daÉ—i haka nake fata, idan bai yi ba ayi mini aikin gafara"