Sashe 92
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"D'iyar Bashiru nefa d'an abokin babanmu,
kin tuna malamin su Saifuddeen na islamiya?."
Da sauri Ummi tace.
"La Bashir kam ai bazan mantashi ba,
lokacin da muke karatu su sunyi sauk'a, kusan sune manyanmu a wurinsu muke biyawa in kawu baya kusa."
Cikin dariya malam Ashiru yace.
"Ato baki mance mu ba ashe."
Kai ta gyad'a cikin jin Kunya dan tuno k'uruciya.
Dirankadi ne yace.
"To Zaleeha d'iyarshi ce ai?."
Ahmad ne yace.
"La Zaleehan Malam Bashir ce? D'alibar Saifuddeen lokacin in bashine zai bata haddaba sam bata tab'a iya kawoshi dai-dai."
Sai ya kuma juyawa ya kalli Saifuddeen da ya kauda kanshi kamar ba shiba.
Baffa Ali ne ya shafa kanshi, tare dayi mishi cikekken bayanin irin tarbar da suka samu, da irin karra masu da akayi, da kuma basu izinin ya fara zuwa zance duk sanda ya shirya.
Wani irin tarin farin ciki yakeji a ransa, a fili kuwa sai hannu ya bawa Dirankadi da Malam Ashiru tare da yi musu alamun godiya da jinjina.
sosai Ummi ke lura da irin yadda fuskarsa ke cike da farin ciki,
Amman kunyarsa ta boye hakan.
Sosai sukaji daɗi daga nan Ahmad ya ɗauki su Baffa Ali ya maidasu Dukku,
Ishaq kuwa yabi babanshi suka tafi.
Bayan duk sun fitane,
Saifuddeen ya sarrafa whellchair ɗinshi har zuwa gaban Ummi dake tsaye,
yana isa inda take ya ruggumeta cikin farinciki da salama.
Murmushi tayi itama tare da tallafo haɓarshi cikin son abinda ɗan nata keso tace.
"Allah ya sanya al'khairi a cikin wannan lamarin naka,
Allah ya shige maka gaba ya tabbatar maka da ingantaccen farin ciki!!."
A saman lips ɗinshi ya amsa da "Amin Amin my Ummi."
Sai ya kuma sarrafa whellchair ɗin nashi ya nufi falonsa.
Ummi kuwa da sauri ta haura sama, inda Hayatuddeen ya tasa Raliya a gaba ala dole sai ta share mishi d'akinshi.
A parlour ta samesu ita tana shara, shi kuwa yanata zuba mata surutu, hannunshi rik'e da pillet d'in kifin margi special yanaci yanata zuba mata zance, kana yana watsar da k'asusuwan a bayan inda ta share.
Cikin gajiya tace.
"Wlh na gaji Ummi autanki zai samin ciwon baya dana kunne, duk inda na share yana b'atawa kuma ya cikamin kunne da surutu kamar kabari."
Baki ya turo gaba tare da cewa.
"Ummi wai dan ina bata labarin wata mawaƙiya, Asma'u Ahmad Matawalle ce da take son Hammana kamar ta mutu, ɗazu muka gama waya da ita wai in gaisheki."
Cikin mamaki Ummi tace.
"Mawaƙiya kuma?."
"Eh" Yace yana lumshe ido tare da kurb'ar juice d'in dake hannunshi.
Kauda zancen Ummi tayi da cewa.
"Su Baffanku sun dawo harma sun koma."
Cikin tsalle Hayatuddeen ya diro daga kan firijin da yake zaune tare da wurga kwalin juice d'in yace.
"An bawa Hamma na ita ko yaushe ne auren?."
Cikin dariya Ummi tace .
"Oh ya Allah ka kimtsa min autana ya zama nitsastse kamar Saifuddeen."
Jin Raliya na cewa.
"Ummi an bashi izini zuwa zancen?."
Cikin gyad'a kai tace.
"Eh an bashi sosaima suka samu karramawa, d'iyar Malaminshi nefa Malam bashir, wanda kuma yake shirin Hanyar tsira na gidan radion vission FM."
Tsalle Hayatuddeen ya kumayi tare da cewa.
"Yanzu kuwa zan tafi gidan Adda Rahma inje musha hira."
Kafinma su ankara tuni ya fice abinsa.
Nan Raliya ta samu daman gyara mishi ɗakin nashi.
Ummi kuwa falonta ta dawo ta zauna taci gaba da karatun da takeyi.
Shi kuwa Saifuddeen dake zaune akan lumtsuma -lumtsuman sofan dake falonshi, gyara zamansa yeyi.
Wayarshi ne a hannunshi da alamu hira yakeyi da ishaq.
"Kai yaro kaji dai ko mun samu karɓuwa.
Yanzu yaushe zamuje ne dan gabatar da kanmu?."
Cikin tsokana Ishaq yace.
"Sai next week ko?."
Da sauri ya rubuta mishi.
"Kayi hauka ne, ai zuciyata zata narke kafin nan."
Dariya sosai Ishaq yayi kana yace.
"To yaushe zamuje?."
Cikin gyara zamanshi yace.
"Anjima da yamma zamuje, kafin nan Ahmad ya dawo."
Dariya Ishaq ya kumayi kana yace.
"A a sarkin sauri, gsky ka bari sai gobe da yamma.
Dan yau zata gabatar da program ɗinta na mushaƙata."
Badan ya soba sai don dole haka ya haƙura.
6:00 pm. Zaleeha ce ke cikin ɗakin watsa shirye-shiryen su.
Zamanta ta gyara bisa kujerar da take kai, tare da ɗan rage sautin waƙar da tasa, kana cikin irin muryarsu na ma'aikatan gidajen radio tace.
"Assalamu alaikum, al'ummar jihar gombe da kewaye, barkanmu da war haka sannunmu da sake saduwa cikin shirin Mushaƙata, tare dani Zaleeha Bashir Sulaiman Dukku."
Sai kuma ta ɗan dakata tare da ƙara sautin waƙar nan ta. Nura M Inuwa mai taken.
"Kaso a soka yafi ƙawance cika taso a soka kanaso."
sai kuma ta ɗan range sautin tana mai bin waƙar, yadda ake iyajin muryarta dana mawaƙan na tafiya atare.
Raveel dake ɗakin kula da shirin dake fita, dariya yayi domin yasan dashi da manager akeyi.
Ita kuwa Zaleeha tuni shauƙin sonshi ya rufeta, saboda zafafan waƙoƙin so da take sakawa.
Cikin shauƙi ta katse wata waƙan Nura M Inuwa mai taken.
"So makaho ne, kamar walƙiya ya kamani, gashi na zautu al'umma sunata nunani!."
Sai kuma ta yi magana a hankali, inda tace.
"Da fatan dai kuna jin daɗin waɗan nan zafafan waƙoƙin da muke kawo muku daga tasharmu ta Vission FM.
Ku gyara zama domin jin waƙarmu ta ƙarshe sakamakon ganin lokaci na hararanmu.
Sai ta kuma saki wata zazzafar waƙa mai tsuma zuciya, inda jarumar ciki ke cewa.
"Zo muyi zance masoyi na kajiya."
Sai ta kuma sai-sai-ta waƙar tare da dai-dai-ta muryarta data waƙar tana bin baitin.
"Karda ka kauce, kasa ai mini dariya.
Saida na tace na zaɓo ka guda ɗaya, babu irinka aduk faɗin duniya."
Sosai akejin muryarta na tafiya da sautin waƙar.
Dai-dai lokacin kuma Baba malam da Ya Ahmad da Aminu, suna gidan Inna wacce ya samu tana jin radio.
Cikin kaɗa kai tace mishi.
"Ka jiko Bashiru ka haifi zabiya mawaƙiya,
Kaji da kunnen ka ko,
Yanzu aka gama gabatar da shirinka na masu imani, Kajita ko ita kuma amara zabiya kantalla mai son kiɗe-kiɗe da raye-raye kamar jikar dujjal."
Shiru baba malam yayi cikin jin kiɗan da Zaleeha ta ƙure ta haɗe da muryarta yana hawa mishi kai.
Kai ya jujjuya dai-dai lokacin da take bin waƙar inda ake cewa.
"Kai d'aya gaiyya mazaje kubi baya.
Babu irinka na duba duk nahiya!."
Cikin takaici Ahmad yasa hannu ya kashe radio'n, dan ya lura ran mahaifin nasu ya ɓaci sosai da sosai, shi kuma sam baya ƙaunar duk abinda zai ɓata mishi rai ko ya taɓa ƙimarshi.
Ita kuwa Zaleeha cikin Shauƙi ta gama gabatar da shirinta kana ta fito.
A bakin ƙofa suka haɗu da Bilkeesu mai gado, dan zata shiga gabatar da shirin labaran duniya.
Cikin kula tace.
"Kadafa ki manta Dukku, gobe da yamma zamuzo gidanku nida Rashida zamuje gidan Adama ta haihu muyi mata barka."
Kai ta jinjina tare da cewa.
"Ba matsala sai kunzo dama gobe ba inda zanje."
Daga nan sukayi sallama,
a bakin motarta ta samu Raveel dariya ya mata tare da cewa.
"Gani nazo muyi zance kar ai miki dariya, ni d'aya gaiya na isheki a duniya, dukka buƙatunki zanmiki ba inkiya."
Murmushi tayi dan dama ai Raveel natane yanada abin dariya dasa mutun Shauƙi.
Motarta ta shiga tare da cewa.
"Kafi kyau a hakanka ka zauna matsayin abokina."
Murmushi yayi tare da rufe mata k'ofar motar.
Kai tsaye gidan Addanta Maryam ta biya dan tace mata,
Yau awaran couscous takeso tayi mata.
A dinning table suka zauna tana cin awaran da aka soya da ƙwai.
Sai miyan tarugu damn albasa da dusan kifi.
Cikin kula Maryam tace.
"Kina addu'o'in da na baki ko?."
Kai ta kaɗa mata tare da cewa.
"Inayi Addana inata rok'on Allah ya baiyana minshi ya kawo minshi gareni in har shidin al'kairi ne a gareni."
Cikin sanyinta da haƙuri tace.
"Yauwa yar uwata, ki kuma rage jin kiɗe-kiɗe ki yawaita jin karatun Al'Qur'ani. Ƙinga inma aljanine kamar yadda mama ke faɗi zai rabu da ke."
Kunun ayan dake gefenta ta kurɓa tare da cewa.
"Mutun nema my Adda na, ina sonshi, ina son abuna."
Murmushi maryam tayi kana tace.
"Allah ya tabbatar miki da al'khairi!."
"Amin Amin." Tace tare da miƙewa, ta ɗauki kular da Maryam ɗin ta cika da awaran tace a kaiwa Aunty Lubna da ya Ahmad.
cikin kula Maryam tace.
"Ki tsaya kiyi salla mana."
Kai ta jujjuya tare da rataya hand bag ɗinta kana tace.
"Kin san baba malam baya son in kaiwa dare a waje."
Kai ta gyaɗa mata kana ta rakata har wojen motarta.
Bayan anyi sallan ishane, Ya Habu ya shigo falon Mama inda ya samu Zaleeha da Zahira da Aunty Lubna suna hira,
cikin yanayinshi na rashin sakin fuska dan shi ya gadi rashin fara'ar Mama amman shi yanada mutunci fuska a haɗe yace.
"Ke Zaleeha kije Baba malam na ƙira."
Da sauri ta dafe ƙirjinta tare da cewa.
"Ya Habu meya faru?."
"In kinje ai zakiji."
ya bata amsa ataƙaice,
jin hakane yasanya ta miƙe da sauri tare da zumbula hijabin sallanta, wanda yake har ƙasa ta nufi parlour'n Baba malam ɗin.
A bakin ƙofar parlour'n tayi kiciɓis da ya Ahmad, cikin sauri ta kamo hannunshi tare da cewa.
"Please ya Ahmad muje ka rakani dan Allah!."
Murmushi yayi sannan yace.
"To muje."
kin tuna malamin su Saifuddeen na islamiya?."
Da sauri Ummi tace.
"La Bashir kam ai bazan mantashi ba,
lokacin da muke karatu su sunyi sauk'a, kusan sune manyanmu a wurinsu muke biyawa in kawu baya kusa."
Cikin dariya malam Ashiru yace.
"Ato baki mance mu ba ashe."
Kai ta gyad'a cikin jin Kunya dan tuno k'uruciya.
Dirankadi ne yace.
"To Zaleeha d'iyarshi ce ai?."
Ahmad ne yace.
"La Zaleehan Malam Bashir ce? D'alibar Saifuddeen lokacin in bashine zai bata haddaba sam bata tab'a iya kawoshi dai-dai."
Sai ya kuma juyawa ya kalli Saifuddeen da ya kauda kanshi kamar ba shiba.
Baffa Ali ne ya shafa kanshi, tare dayi mishi cikekken bayanin irin tarbar da suka samu, da irin karra masu da akayi, da kuma basu izinin ya fara zuwa zance duk sanda ya shirya.
Wani irin tarin farin ciki yakeji a ransa, a fili kuwa sai hannu ya bawa Dirankadi da Malam Ashiru tare da yi musu alamun godiya da jinjina.
sosai Ummi ke lura da irin yadda fuskarsa ke cike da farin ciki,
Amman kunyarsa ta boye hakan.
Sosai sukaji daɗi daga nan Ahmad ya ɗauki su Baffa Ali ya maidasu Dukku,
Ishaq kuwa yabi babanshi suka tafi.
Bayan duk sun fitane,
Saifuddeen ya sarrafa whellchair ɗinshi har zuwa gaban Ummi dake tsaye,
yana isa inda take ya ruggumeta cikin farinciki da salama.
Murmushi tayi itama tare da tallafo haɓarshi cikin son abinda ɗan nata keso tace.
"Allah ya sanya al'khairi a cikin wannan lamarin naka,
Allah ya shige maka gaba ya tabbatar maka da ingantaccen farin ciki!!."
A saman lips ɗinshi ya amsa da "Amin Amin my Ummi."
Sai ya kuma sarrafa whellchair ɗin nashi ya nufi falonsa.
Ummi kuwa da sauri ta haura sama, inda Hayatuddeen ya tasa Raliya a gaba ala dole sai ta share mishi d'akinshi.
A parlour ta samesu ita tana shara, shi kuwa yanata zuba mata surutu, hannunshi rik'e da pillet d'in kifin margi special yanaci yanata zuba mata zance, kana yana watsar da k'asusuwan a bayan inda ta share.
Cikin gajiya tace.
"Wlh na gaji Ummi autanki zai samin ciwon baya dana kunne, duk inda na share yana b'atawa kuma ya cikamin kunne da surutu kamar kabari."
Baki ya turo gaba tare da cewa.
"Ummi wai dan ina bata labarin wata mawaƙiya, Asma'u Ahmad Matawalle ce da take son Hammana kamar ta mutu, ɗazu muka gama waya da ita wai in gaisheki."
Cikin mamaki Ummi tace.
"Mawaƙiya kuma?."
"Eh" Yace yana lumshe ido tare da kurb'ar juice d'in dake hannunshi.
Kauda zancen Ummi tayi da cewa.
"Su Baffanku sun dawo harma sun koma."
Cikin tsalle Hayatuddeen ya diro daga kan firijin da yake zaune tare da wurga kwalin juice d'in yace.
"An bawa Hamma na ita ko yaushe ne auren?."
Cikin dariya Ummi tace .
"Oh ya Allah ka kimtsa min autana ya zama nitsastse kamar Saifuddeen."
Jin Raliya na cewa.
"Ummi an bashi izini zuwa zancen?."
Cikin gyad'a kai tace.
"Eh an bashi sosaima suka samu karramawa, d'iyar Malaminshi nefa Malam bashir, wanda kuma yake shirin Hanyar tsira na gidan radion vission FM."
Tsalle Hayatuddeen ya kumayi tare da cewa.
"Yanzu kuwa zan tafi gidan Adda Rahma inje musha hira."
Kafinma su ankara tuni ya fice abinsa.
Nan Raliya ta samu daman gyara mishi ɗakin nashi.
Ummi kuwa falonta ta dawo ta zauna taci gaba da karatun da takeyi.
Shi kuwa Saifuddeen dake zaune akan lumtsuma -lumtsuman sofan dake falonshi, gyara zamansa yeyi.
Wayarshi ne a hannunshi da alamu hira yakeyi da ishaq.
"Kai yaro kaji dai ko mun samu karɓuwa.
Yanzu yaushe zamuje ne dan gabatar da kanmu?."
Cikin tsokana Ishaq yace.
"Sai next week ko?."
Da sauri ya rubuta mishi.
"Kayi hauka ne, ai zuciyata zata narke kafin nan."
Dariya sosai Ishaq yayi kana yace.
"To yaushe zamuje?."
Cikin gyara zamanshi yace.
"Anjima da yamma zamuje, kafin nan Ahmad ya dawo."
Dariya Ishaq ya kumayi kana yace.
"A a sarkin sauri, gsky ka bari sai gobe da yamma.
Dan yau zata gabatar da program ɗinta na mushaƙata."
Badan ya soba sai don dole haka ya haƙura.
6:00 pm. Zaleeha ce ke cikin ɗakin watsa shirye-shiryen su.
Zamanta ta gyara bisa kujerar da take kai, tare da ɗan rage sautin waƙar da tasa, kana cikin irin muryarsu na ma'aikatan gidajen radio tace.
"Assalamu alaikum, al'ummar jihar gombe da kewaye, barkanmu da war haka sannunmu da sake saduwa cikin shirin Mushaƙata, tare dani Zaleeha Bashir Sulaiman Dukku."
Sai kuma ta ɗan dakata tare da ƙara sautin waƙar nan ta. Nura M Inuwa mai taken.
"Kaso a soka yafi ƙawance cika taso a soka kanaso."
sai kuma ta ɗan range sautin tana mai bin waƙar, yadda ake iyajin muryarta dana mawaƙan na tafiya atare.
Raveel dake ɗakin kula da shirin dake fita, dariya yayi domin yasan dashi da manager akeyi.
Ita kuwa Zaleeha tuni shauƙin sonshi ya rufeta, saboda zafafan waƙoƙin so da take sakawa.
Cikin shauƙi ta katse wata waƙan Nura M Inuwa mai taken.
"So makaho ne, kamar walƙiya ya kamani, gashi na zautu al'umma sunata nunani!."
Sai kuma ta yi magana a hankali, inda tace.
"Da fatan dai kuna jin daɗin waɗan nan zafafan waƙoƙin da muke kawo muku daga tasharmu ta Vission FM.
Ku gyara zama domin jin waƙarmu ta ƙarshe sakamakon ganin lokaci na hararanmu.
Sai ta kuma saki wata zazzafar waƙa mai tsuma zuciya, inda jarumar ciki ke cewa.
"Zo muyi zance masoyi na kajiya."
Sai ta kuma sai-sai-ta waƙar tare da dai-dai-ta muryarta data waƙar tana bin baitin.
"Karda ka kauce, kasa ai mini dariya.
Saida na tace na zaɓo ka guda ɗaya, babu irinka aduk faɗin duniya."
Sosai akejin muryarta na tafiya da sautin waƙar.
Dai-dai lokacin kuma Baba malam da Ya Ahmad da Aminu, suna gidan Inna wacce ya samu tana jin radio.
Cikin kaɗa kai tace mishi.
"Ka jiko Bashiru ka haifi zabiya mawaƙiya,
Kaji da kunnen ka ko,
Yanzu aka gama gabatar da shirinka na masu imani, Kajita ko ita kuma amara zabiya kantalla mai son kiɗe-kiɗe da raye-raye kamar jikar dujjal."
Shiru baba malam yayi cikin jin kiɗan da Zaleeha ta ƙure ta haɗe da muryarta yana hawa mishi kai.
Kai ya jujjuya dai-dai lokacin da take bin waƙar inda ake cewa.
"Kai d'aya gaiyya mazaje kubi baya.
Babu irinka na duba duk nahiya!."
Cikin takaici Ahmad yasa hannu ya kashe radio'n, dan ya lura ran mahaifin nasu ya ɓaci sosai da sosai, shi kuma sam baya ƙaunar duk abinda zai ɓata mishi rai ko ya taɓa ƙimarshi.
Ita kuwa Zaleeha cikin Shauƙi ta gama gabatar da shirinta kana ta fito.
A bakin ƙofa suka haɗu da Bilkeesu mai gado, dan zata shiga gabatar da shirin labaran duniya.
Cikin kula tace.
"Kadafa ki manta Dukku, gobe da yamma zamuzo gidanku nida Rashida zamuje gidan Adama ta haihu muyi mata barka."
Kai ta jinjina tare da cewa.
"Ba matsala sai kunzo dama gobe ba inda zanje."
Daga nan sukayi sallama,
a bakin motarta ta samu Raveel dariya ya mata tare da cewa.
"Gani nazo muyi zance kar ai miki dariya, ni d'aya gaiya na isheki a duniya, dukka buƙatunki zanmiki ba inkiya."
Murmushi tayi dan dama ai Raveel natane yanada abin dariya dasa mutun Shauƙi.
Motarta ta shiga tare da cewa.
"Kafi kyau a hakanka ka zauna matsayin abokina."
Murmushi yayi tare da rufe mata k'ofar motar.
Kai tsaye gidan Addanta Maryam ta biya dan tace mata,
Yau awaran couscous takeso tayi mata.
A dinning table suka zauna tana cin awaran da aka soya da ƙwai.
Sai miyan tarugu damn albasa da dusan kifi.
Cikin kula Maryam tace.
"Kina addu'o'in da na baki ko?."
Kai ta kaɗa mata tare da cewa.
"Inayi Addana inata rok'on Allah ya baiyana minshi ya kawo minshi gareni in har shidin al'kairi ne a gareni."
Cikin sanyinta da haƙuri tace.
"Yauwa yar uwata, ki kuma rage jin kiɗe-kiɗe ki yawaita jin karatun Al'Qur'ani. Ƙinga inma aljanine kamar yadda mama ke faɗi zai rabu da ke."
Kunun ayan dake gefenta ta kurɓa tare da cewa.
"Mutun nema my Adda na, ina sonshi, ina son abuna."
Murmushi maryam tayi kana tace.
"Allah ya tabbatar miki da al'khairi!."
"Amin Amin." Tace tare da miƙewa, ta ɗauki kular da Maryam ɗin ta cika da awaran tace a kaiwa Aunty Lubna da ya Ahmad.
cikin kula Maryam tace.
"Ki tsaya kiyi salla mana."
Kai ta jujjuya tare da rataya hand bag ɗinta kana tace.
"Kin san baba malam baya son in kaiwa dare a waje."
Kai ta gyaɗa mata kana ta rakata har wojen motarta.
Bayan anyi sallan ishane, Ya Habu ya shigo falon Mama inda ya samu Zaleeha da Zahira da Aunty Lubna suna hira,
cikin yanayinshi na rashin sakin fuska dan shi ya gadi rashin fara'ar Mama amman shi yanada mutunci fuska a haɗe yace.
"Ke Zaleeha kije Baba malam na ƙira."
Da sauri ta dafe ƙirjinta tare da cewa.
"Ya Habu meya faru?."
"In kinje ai zakiji."
ya bata amsa ataƙaice,
jin hakane yasanya ta miƙe da sauri tare da zumbula hijabin sallanta, wanda yake har ƙasa ta nufi parlour'n Baba malam ɗin.
A bakin ƙofar parlour'n tayi kiciɓis da ya Ahmad, cikin sauri ta kamo hannunshi tare da cewa.
"Please ya Ahmad muje ka rakani dan Allah!."
Murmushi yayi sannan yace.
"To muje."