Sashe 25
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Cikin k'ank'anin lokaci suka cika randa biyu sun fara sawa ana ukun ne Rahma ta fito daga cikin kitchen d'in tana ganin Saifuddeen ne ke jan ruwan tayi maza ta isa gindin rijiyar cikin sauri tasa hannu ta kamo igiyar gugan tare da cewa.
"Ka bari haka ya isa, Ummi ya za'ayi ki barshi yaja ruwa kinsan yanzu hannunshi zai d'uri ruwa."
cikin kula Ummi tace.
"Yak'i ya barni inja kin san ba yarda zaiba, kuma bazai bari mu zauna ba ruwa ba."
fuska ta kwabe ganin ya amshi gugar yaci gaba da jan ruwan,
cikin sanyi tace.
"To ka rink'a ja nida Hayatuddeen zamu rink'a jida,
ni da ka bari ma dan na aika Mudassir yazo kuma nasan in yazo in na sashi ba k'i zaiyiba."
cikin k'arfin hali ya nuna mata alamun karta damu,
daga nan sukaci gaba da jan ruwan.
Suna gamawa ya cika botikin ya shiga wonka,
tuni Ummi kuma ta gama dama kunun,
inda Raihana da cikinta ya d'an lafa ta tashi zaune ta jingina da bishiyar dimurin dake tsakiyar gidan nasu kusan nanne wurin zamansu,
Rahma kuma duk ta had'a komai na bud'a baki har miyar asuba tayi musu tunda Raihana maiyin bata da lfy,
Hayatuddeen kuwa tuni Ummi ta d'ora mishi kulan masa ya kai ya dawo kana ta d'ora mishi na k'osan tare da bashi robar dake cike da dabino a hannu bayan ya dawone ta kuma aza mishi kulan kunun tare da cewa.
"Zaka iya ko autana?."
cikin dakiya da jarumtar da yake koya a wurin Hamma Safuddeen d'inshi yace.
"Eh Ummi zan iya."
kai ta gyad'a sannan tace.
"To in kaje kace a sauk'eka kada kace zaka sauk'e da kanka dan bazaka iyaba."
juyawa yayi yana fita tare da cewa.
"To, duk da yaso yayi irin na Hamma shi duk abinda ake tunanin bazai iyaba sai ya yin, to amman ina ai shi Autan Ummi akwai ragwanci over.
Shi kuwa Saifuddeen bayan yayi wonka yana fitowa ana kiran salla.
Ummi da kanta yau ta zuba mishi madara da sugar bisa kankanan ta kuma wonke mishi dabinon,
yana isa inda suke ya zauna gefe bisa wani dutse wanda nan suke zama suyi al'wala, Faruq ne ya mik'a mishi buta yayinda Ummi kuma ta mik'o mishi dabinon,
Ummi da Rahma da Raihana duk tafin hannunshi suka zubawa ido ganin sunyi jazir tamkar ka tab'a jini ya tsallo,
kan yatsunshi kuma sunfi ko ina yin ja,
cikin muryar ciwo Raihana tace.
"Dan Allah Hamma kada ka sake jan ruwa kalli yadda tafin hannunka sukayi fa."
yi yayi kamar bai gane me take cewaba.
Ummi kuwa kamar tasa kuka takeji dan tausayinshi,
Rahma kuwa hannunta tasa ta shafi tafin hannun nashi ganin duk inda ta shafa sai jinin wurin ya gudu wurin yayi fari sai kuma a take wurin yayi ja kamar da,
sai kuma duk suka juyo kan Raihana dan ganin ta kamo hannun Umminta ta rik'e gam alamun,
ciwon cikin nata ya murd'a,
gaba d'aya jikinta rawa yakeyi dan azaba,
kusan a tare suke ce mata sannu,
shi kuwa Saifuddeen nuni yayiwa Ummi da ta,
had'awa Raihana zuma da ruwan zafi ta bata tasha."
cikin gane abinda yake nufi tace.
"Na bata ta sha tunda da yamma nace tasha amman tak'i wai ita sai ta kai azuminta, to sai yanzu da auta ya kai dabino masallaci yace ansha ruwa to shine ta amshi ruwan zafin da zuman tasha yanzu kuma inaga cikin ya kuma murd'awane."
sai kuma suka bita da idanu ganin ta mik'e da sauri ta zari butan dake gaban Saifuddeen d'in ta nufi band'akinsu,
tuni kuma Al'adar tata ta iso har ya d'an b'ata mata zani,
ai da sauri Saifuddeen ya rumtse idanunshi dan yanada tsananin k'yank'yani yanzu haka bazai sake cin abin hannun Raihana ba har sai yaga ta samu tsarki tana salla,
Rahma kuwa dariya tayi tare da cewa.
"Hmmmm Deeen kenan tunda kai na mijine ai da sauk'i,
sai dai kuma tunda zakayi aure ba mmki wata ran kayiwa matarka wonki."
kame jikinshi yayi alamun tsikar jikinshi ya tashi da batun wai shi dai yayiwa matarshi wonkin wannan k'azantar,
Ummi kam tuni ta bar wurin shi kuwa yawu ya tofar kana ya d'auki pillet d'in kankana ya mik'e tare da yiwa Adda Rahman tashi alamun Allah ya kiyasheshi da sharrin bakinta, dariya tayi tare da bin bayanshi da ido,
tabbas tasan su duka zuriyarsu kyawawane amman babu wanda ya kai Saifuddeen ita kanta wani lokaci ganinshi take tamkar balarabe ko ba indiye,
gashi komai nashi da nitsuwa da tausayawa,
gashin k'eyanshi ta zubawa idanu har saida ya b'acewa ganinta.
Shiko yana fitowa woje yayi gefen su Warisu nan suka shanye kankanan a tare amman time to time yakan rumtse ido in ya tuno jinin da ya gani sai ya kuma tofar da minyau.
Ana idar da salla suka shiga gida inda suka samu,
yau kuma awaran couscous Adda Rahma tayi musu sai masan da ta d'iba musu cikin na masallaci sannan tayi musu miyan alaiyahu da tontok'oshi wanda da miyar zasuci masan,
sai kuma tea da ta kawo musu amman ba madara, dan azumi yazo k'arshe mafi yawanci cefenensu yayi k'asa
sai kuma kunun gyad'a,
nan sukaci sukasha kamar kullum,
sannan suka tafi jin tabsir wanda yau zasu rufe 27 ga watan Ramadan d'in kenan.
Suna dawowa ta kawo musu tuk'ek'k'en tuwon shinkafa da miyar ganye wanda miyar asubane to da yake miyar da d'an yawa shiyasa ta tuk'a musu tuwo,
a zatonta bazasu wani ciba amman kuma sai gashi sun cinye tas yau harda Saifuddeen da yake abinda yake sone Warisu ne ya d'anci kad'an.
Bayan sun gama cine Ahmad ya firfito musu da d'inku nansu baki d'aya,
sosai sukayi mmkin yadda ya gama d'inkunan cikin k'ank'anin lokaci kuma d'inkunan sunyi kyau sosai da salon tsarin d'inkunan wannan shekarun.
Nan Saifuddeen ya bawa kowa nashi,
duk sukayi godiya dama tuni Saminu ya kawo musu takalmansu da huluna Salisu kuma ya kawo musu ogogunansu.
Daga nan duk sukayi sallama suka tafi sai Ahmad da yace yau nan zai kwana,
to bayan su Mudassir sun tafine Bappa Ali da Aunty Nina ma sukazo yiwa Saifuddeen godiya nan sukaci gaba da hira,
a nanne Saifuddeen yace dasu,
Hayatuddeen zai rink'a zuwa wurin Ahmad ya rink'a koya mishi d'inki,
to kuma duk sunyi na'am da hakan daga nan suka d'an tab'a hira sannan duk sukayi saida safe suka watse.
Washe gari kamar kullum suna isa ya d'an shiga massalaci yayi baccin awa d'aya da rabi yana tashi yayi al'wala yayi walahanshi,
yana fitowa kai tsaye layin da zai sadashi da kantin kori ya shiga,
yana isa d'ab da kantin korin ya tsaya a bakin shagon Malam Habu mai saida mayukan shafa da turatuka powder da dai sauran kayan kolliya na mata,
Sadiq na ganinshi cikin fara'a yace.
"Barka da isowa Balarabe."
murmushi yayi tare da mishi alamun bafulatani dai daga nan suka d'an gaggaisa da mutanen layin sannan ya isa dilansu na ledan yana zuwa aka bashi kamar kullum sannan ya fara zazzagayawa ya rabawa kowa.
Koda ya gama sai ya d'auko omonshi nan yayi ta zagayawa sosai kuwa yau ya sayar koda ya gaji ya koma shagon Malam Habu ya zauna yana d'an hutawa dan yana son yaje gidansu Ishaq to ya kuma yanaga kada yaje ya samu basu isoba da wannan tunanin ya bari sai gobe yaje,
cikin body language ya tambayi Malam Habu ko yasa inda gidan Baba Bella yake?."
kai ya jujjuya alamun gsky bai saniba to amman sai ya bashi shawaran yaje ya tambayi Alhaji Aliyu dilansu na ledodin kenan dan yana kyautata zaton shi zai san unguwar da Dottijon yake,
nan yake cewa Malam Habu ya mantane Alhaji Aliyu baya k'asar ya tafi umrah,
to nan yace ya tambayi yan shagonshi wata k'il zasu sani,
toh fa abu kamar da wasa ya tambayi duk mutanen da yake zaton zasu san gidan Dottijon nan baba Bello amman duk sai kowa yace ko unguwar da yakema basu saniba yayinda wasuma sai suke mmki da ce mishi ba yace kai jikanshi bane to ya za'ayi kai jikanshi baka san gidanshi ba sai mu.
Shi kuwa Saifuddeen ribarshi na yau na omo dana leda harda riban omon jiya ya had'an kud'in 10k da nufin zai yiwa Baba bello ihsanin yayi hidiman salla,
to kuma gashi ya rasa wanda yasan gidan,
dole haka ya hak'ura sannan ya bawa malam Habu ajiyan wannan 10k d'in dan ya rigada yayi niyar wannan kud'in Dottijon zai bamawa.
K'arfe biyar nayi Salisu yazo suka tafi Dukku.
"Ka bari haka ya isa, Ummi ya za'ayi ki barshi yaja ruwa kinsan yanzu hannunshi zai d'uri ruwa."
cikin kula Ummi tace.
"Yak'i ya barni inja kin san ba yarda zaiba, kuma bazai bari mu zauna ba ruwa ba."
fuska ta kwabe ganin ya amshi gugar yaci gaba da jan ruwan,
cikin sanyi tace.
"To ka rink'a ja nida Hayatuddeen zamu rink'a jida,
ni da ka bari ma dan na aika Mudassir yazo kuma nasan in yazo in na sashi ba k'i zaiyiba."
cikin k'arfin hali ya nuna mata alamun karta damu,
daga nan sukaci gaba da jan ruwan.
Suna gamawa ya cika botikin ya shiga wonka,
tuni Ummi kuma ta gama dama kunun,
inda Raihana da cikinta ya d'an lafa ta tashi zaune ta jingina da bishiyar dimurin dake tsakiyar gidan nasu kusan nanne wurin zamansu,
Rahma kuma duk ta had'a komai na bud'a baki har miyar asuba tayi musu tunda Raihana maiyin bata da lfy,
Hayatuddeen kuwa tuni Ummi ta d'ora mishi kulan masa ya kai ya dawo kana ta d'ora mishi na k'osan tare da bashi robar dake cike da dabino a hannu bayan ya dawone ta kuma aza mishi kulan kunun tare da cewa.
"Zaka iya ko autana?."
cikin dakiya da jarumtar da yake koya a wurin Hamma Safuddeen d'inshi yace.
"Eh Ummi zan iya."
kai ta gyad'a sannan tace.
"To in kaje kace a sauk'eka kada kace zaka sauk'e da kanka dan bazaka iyaba."
juyawa yayi yana fita tare da cewa.
"To, duk da yaso yayi irin na Hamma shi duk abinda ake tunanin bazai iyaba sai ya yin, to amman ina ai shi Autan Ummi akwai ragwanci over.
Shi kuwa Saifuddeen bayan yayi wonka yana fitowa ana kiran salla.
Ummi da kanta yau ta zuba mishi madara da sugar bisa kankanan ta kuma wonke mishi dabinon,
yana isa inda suke ya zauna gefe bisa wani dutse wanda nan suke zama suyi al'wala, Faruq ne ya mik'a mishi buta yayinda Ummi kuma ta mik'o mishi dabinon,
Ummi da Rahma da Raihana duk tafin hannunshi suka zubawa ido ganin sunyi jazir tamkar ka tab'a jini ya tsallo,
kan yatsunshi kuma sunfi ko ina yin ja,
cikin muryar ciwo Raihana tace.
"Dan Allah Hamma kada ka sake jan ruwa kalli yadda tafin hannunka sukayi fa."
yi yayi kamar bai gane me take cewaba.
Ummi kuwa kamar tasa kuka takeji dan tausayinshi,
Rahma kuwa hannunta tasa ta shafi tafin hannun nashi ganin duk inda ta shafa sai jinin wurin ya gudu wurin yayi fari sai kuma a take wurin yayi ja kamar da,
sai kuma duk suka juyo kan Raihana dan ganin ta kamo hannun Umminta ta rik'e gam alamun,
ciwon cikin nata ya murd'a,
gaba d'aya jikinta rawa yakeyi dan azaba,
kusan a tare suke ce mata sannu,
shi kuwa Saifuddeen nuni yayiwa Ummi da ta,
had'awa Raihana zuma da ruwan zafi ta bata tasha."
cikin gane abinda yake nufi tace.
"Na bata ta sha tunda da yamma nace tasha amman tak'i wai ita sai ta kai azuminta, to sai yanzu da auta ya kai dabino masallaci yace ansha ruwa to shine ta amshi ruwan zafin da zuman tasha yanzu kuma inaga cikin ya kuma murd'awane."
sai kuma suka bita da idanu ganin ta mik'e da sauri ta zari butan dake gaban Saifuddeen d'in ta nufi band'akinsu,
tuni kuma Al'adar tata ta iso har ya d'an b'ata mata zani,
ai da sauri Saifuddeen ya rumtse idanunshi dan yanada tsananin k'yank'yani yanzu haka bazai sake cin abin hannun Raihana ba har sai yaga ta samu tsarki tana salla,
Rahma kuwa dariya tayi tare da cewa.
"Hmmmm Deeen kenan tunda kai na mijine ai da sauk'i,
sai dai kuma tunda zakayi aure ba mmki wata ran kayiwa matarka wonki."
kame jikinshi yayi alamun tsikar jikinshi ya tashi da batun wai shi dai yayiwa matarshi wonkin wannan k'azantar,
Ummi kam tuni ta bar wurin shi kuwa yawu ya tofar kana ya d'auki pillet d'in kankana ya mik'e tare da yiwa Adda Rahman tashi alamun Allah ya kiyasheshi da sharrin bakinta, dariya tayi tare da bin bayanshi da ido,
tabbas tasan su duka zuriyarsu kyawawane amman babu wanda ya kai Saifuddeen ita kanta wani lokaci ganinshi take tamkar balarabe ko ba indiye,
gashi komai nashi da nitsuwa da tausayawa,
gashin k'eyanshi ta zubawa idanu har saida ya b'acewa ganinta.
Shiko yana fitowa woje yayi gefen su Warisu nan suka shanye kankanan a tare amman time to time yakan rumtse ido in ya tuno jinin da ya gani sai ya kuma tofar da minyau.
Ana idar da salla suka shiga gida inda suka samu,
yau kuma awaran couscous Adda Rahma tayi musu sai masan da ta d'iba musu cikin na masallaci sannan tayi musu miyan alaiyahu da tontok'oshi wanda da miyar zasuci masan,
sai kuma tea da ta kawo musu amman ba madara, dan azumi yazo k'arshe mafi yawanci cefenensu yayi k'asa
sai kuma kunun gyad'a,
nan sukaci sukasha kamar kullum,
sannan suka tafi jin tabsir wanda yau zasu rufe 27 ga watan Ramadan d'in kenan.
Suna dawowa ta kawo musu tuk'ek'k'en tuwon shinkafa da miyar ganye wanda miyar asubane to da yake miyar da d'an yawa shiyasa ta tuk'a musu tuwo,
a zatonta bazasu wani ciba amman kuma sai gashi sun cinye tas yau harda Saifuddeen da yake abinda yake sone Warisu ne ya d'anci kad'an.
Bayan sun gama cine Ahmad ya firfito musu da d'inku nansu baki d'aya,
sosai sukayi mmkin yadda ya gama d'inkunan cikin k'ank'anin lokaci kuma d'inkunan sunyi kyau sosai da salon tsarin d'inkunan wannan shekarun.
Nan Saifuddeen ya bawa kowa nashi,
duk sukayi godiya dama tuni Saminu ya kawo musu takalmansu da huluna Salisu kuma ya kawo musu ogogunansu.
Daga nan duk sukayi sallama suka tafi sai Ahmad da yace yau nan zai kwana,
to bayan su Mudassir sun tafine Bappa Ali da Aunty Nina ma sukazo yiwa Saifuddeen godiya nan sukaci gaba da hira,
a nanne Saifuddeen yace dasu,
Hayatuddeen zai rink'a zuwa wurin Ahmad ya rink'a koya mishi d'inki,
to kuma duk sunyi na'am da hakan daga nan suka d'an tab'a hira sannan duk sukayi saida safe suka watse.
Washe gari kamar kullum suna isa ya d'an shiga massalaci yayi baccin awa d'aya da rabi yana tashi yayi al'wala yayi walahanshi,
yana fitowa kai tsaye layin da zai sadashi da kantin kori ya shiga,
yana isa d'ab da kantin korin ya tsaya a bakin shagon Malam Habu mai saida mayukan shafa da turatuka powder da dai sauran kayan kolliya na mata,
Sadiq na ganinshi cikin fara'a yace.
"Barka da isowa Balarabe."
murmushi yayi tare da mishi alamun bafulatani dai daga nan suka d'an gaggaisa da mutanen layin sannan ya isa dilansu na ledan yana zuwa aka bashi kamar kullum sannan ya fara zazzagayawa ya rabawa kowa.
Koda ya gama sai ya d'auko omonshi nan yayi ta zagayawa sosai kuwa yau ya sayar koda ya gaji ya koma shagon Malam Habu ya zauna yana d'an hutawa dan yana son yaje gidansu Ishaq to ya kuma yanaga kada yaje ya samu basu isoba da wannan tunanin ya bari sai gobe yaje,
cikin body language ya tambayi Malam Habu ko yasa inda gidan Baba Bella yake?."
kai ya jujjuya alamun gsky bai saniba to amman sai ya bashi shawaran yaje ya tambayi Alhaji Aliyu dilansu na ledodin kenan dan yana kyautata zaton shi zai san unguwar da Dottijon yake,
nan yake cewa Malam Habu ya mantane Alhaji Aliyu baya k'asar ya tafi umrah,
to nan yace ya tambayi yan shagonshi wata k'il zasu sani,
toh fa abu kamar da wasa ya tambayi duk mutanen da yake zaton zasu san gidan Dottijon nan baba Bello amman duk sai kowa yace ko unguwar da yakema basu saniba yayinda wasuma sai suke mmki da ce mishi ba yace kai jikanshi bane to ya za'ayi kai jikanshi baka san gidanshi ba sai mu.
Shi kuwa Saifuddeen ribarshi na yau na omo dana leda harda riban omon jiya ya had'an kud'in 10k da nufin zai yiwa Baba bello ihsanin yayi hidiman salla,
to kuma gashi ya rasa wanda yasan gidan,
dole haka ya hak'ura sannan ya bawa malam Habu ajiyan wannan 10k d'in dan ya rigada yayi niyar wannan kud'in Dottijon zai bamawa.
K'arfe biyar nayi Salisu yazo suka tafi Dukku.