Sashe 42
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana sauk'owa taci karo da Hayatuddeen a tsakiyar parlour yanata kiciniyar kwance bel d'in k'ugunshi,
ido ta zura mishi ba tare da ta k'arisa sauk'owanba hakama Raliya ido ta zura mishi,
shi kuwa baima san sunayi ba yana zare bel d'in yayi k'asa da dogon wondon Blue Jeans dake jikinshi ya rage dagashi sai d'an gajeren wondo dake jikinshi, sawunshi ya zare kana ya tsallake wondon inda ya sab'uleshi ya nufi hanyar d'akinshi tare da cilla bel d'in a tsakiyar parlour,
sai kuma ya fara kiciniyar cire rigarshi tare da cewa.
"Nima bari inje inyi wonka dan yau a masallacin fad'ar jiha zamuyi salla dasu Imran dasu Sulaiman Zakariyya shi yace yama je tun d'azu."
tsayawa yayi tare da juyawa da sauri jin Raliya na mishi mgna cikin tsawa take ce mishi.
"Wai kai kam Hayatuddeen wanne irin yarone mara kan gado,
kalli yadda ka watsa mana parlour dan tsabar sakarci da sakalci inda ka cire wondonka nan kake bar mana shi wato kai gaka auta mai buhun sakalci uwar wa zata tattara maka kwamutsan naka to da ka barshi?."
wani dogon tsaki yaja tare da cewa.
"Uwata mana ce miki akayi bani da gatane banza kawai uwar sa ido."
yana fad'in haka yayi shigewarsa d'an k'aramin side inshi,
ita kuwa Raliya taita zumbura baki dan Ummi ta sata tattaramishi kayanshi daya watsar.
Saifuddeen kuwa yana fita yaci karo da Salisu wanda shine ya d'aukeshi suka nufi hanyarsu da zata sadasu da titin tutun wada,
mik'ewa sukayi direct har kusa da mashigar G.S.U cikin nitsuwa Salisu ke draving suna gab da shiga gate d'in.
Jonapwd k'ungiyar nakasassu ta jihar kenan Salisu ya juyo cikin nitsuwa da kula ya kalli Saifuddeen tare da cewa.
"Motocin nan da mukayi mgnarsu last week sun iso jiya,
shiyasa nazo da nufin muje ka gansu ka zab'i kalan da kakeso a ciki,
dan gsky zamanka ba mota baiyiba,
tunda ko bazaka yi tuk'iba zamu iya samar maka amintaccen direba da zai rink'a kaika duk inda kakeso da kai da Ummi kafin Hayatuddeen ya k'ara girma."
murmushi Saifuddeen yayi tare da gyara zamanshi duk da yaga Salisun yayi parking kai ya jinjina tare da rubuta mishi.
"Bank'i shawararku bafa sai dai kuda kanku kunsan cewa yanzu bani da kud'in a k'asa dan na yashe duk asusuna nayi hidimar k'aurannan to kuma bani son abu da bashi."
a take fuskar Salisu ta sauya yanayi,
cikin sanyin sauti yace.
"Bashi kuma! Saifuddeen yanzu ashe dama kayana ba naka bane,
ashe dan ka d'auki mota d'aya rak cikin jerin motoci kusan takwas wanda kaine silar samar min jarinsu sai ya zama wani abu?."
Kai ya rink'a jujjuyawa cikin nuna alamun ba haka bane,
ganin haka yasa Salisu cewa.
"To kada ka sake kiramin kalmar bashi a tsakaninmu kuma ko bakaje ka zab'i kalar da kake soba ni zan zab'a maka da kaina gobe zan kawo maka ita har gida,
kuma in ba matsala a cikin yaran da suke wonke mana motocin akwai wani yaro Sule yanada nitsuwa ya kuma iya tuk'i na mutunci sai ya dawo nan ya rink'a kaiku duk inda kuke buk'ata zai kuma iya kula da shuke-shuken gidan in yaso duk wata ka rink'a biyanshi abinda nake biyanshi,
to dama kullum ina bashi kud'in abinci,
to kaga kai ba sai kayi ta bashi kud'in abinciba sai Ummi ta rink'a zuba mishi shida baba maigadi ko?." ya k'arishe mgnar cikin yanayin tambaya.
kai ya jinjina mishi tare da rubuta mishi.
"To ba matsala kayi yadda kaga ya dace."
cikin jin dad'in amincewar Saifuddeen d'in yace.
"To ba matsala."
Daga nan suka fito suka shiga cikin harabar wurin,
kai tsaye office d'in Ishaq suka nufa,
jin motsin bud'e k'ofarne yasa Ishaq juyawa da sauri sai ya kuma mik'e da sauri jin muryar Salisu,
numfashi ya shak'a tare da cewa.
"Lalle marhabin da manyan bak'i."
jin Saifuddeen ya rik'e hannunshi ya sashi juyawa gareshi tare da cewa.
"Kai amman naji haushi wlh kaga da kazo awa uku da suka wuce da ka had'u da Zaleeha sabuwar ma'akaciyar gidan radio vision FM gombe wacce take gabatar da shirin *Babu nakasasshe sai rago* yau dani mukayi hira na d'an bata tarihin rayuwata ka ko san dole zaka shiga ciki."
shiru yayi jin Saifuddeen ya rufe mishi baki da hannu tare da zaro wayarshi da hannunshi d'aya kana ya rubuta mishi text.
"Kai dan Allah ka huta mana wai bakinka bai gajiya da surutune? to ni ka bani ruwan sha tukun."
da sauri ya zaro wayarshi jin shigowar sak'o yasan Saifuddeen ne ya mishi mgn,
dariya yayi sanda ya karanta kana yace.
"To sarkin k'warafi ga wuri ku zauna."
sai kuma ya d'anyi taku biyu zuwa uku ya isa gaban firiji ruwan sanyi ya d'auko musu sannan yazo kusa dasu,
Salisu kam har yau bai dena mamakin yadda abota ta kasance tsakanin makaho da kurmaba suna kuma fahimtar juna over,
amsar ruwan sukayi saida suka d'an sha sannan suka ci gaba da hira amman banda Saifuddeen dan TV yake kallon tashar Farin wata wanda duk had'e suke da vision sosai ya zubawa TV idanu yana karanta rubutun daya bayyana a fuskar tv inda aka rubuta Babu nakasasshe sai rago, sosai Saifuddeen ya maida hankalin shi kan tv ganin sun hasko fuskar wata kekyawar budurwa mai cikar haiba,
lips d'inta ya zubawa idanu dan yana son gane abinda zata fad'a da kyau,
wani irin sassanyan ajiyan zuciya yayi jin wani abu na yana zirta cikin zuciyarshi har zuwa kwanyar kanshi ganin yadda take motso labb'anta wani sassanyar ajiyan zuciya ya kuma yaja a hankali ya sauk'e jin zuciyarshi na bugawa da sauri-sauri,
wani irin shauk'i ne mai cike da farin ciki ya ziyarci zuciyarshi da gangar jikinshi,
ina ya kasa kauda idanunshi a kanta,
da kyar ya juyo a fizge ya kalli Ishaq da yake tab'ashi yana ce mishi.
"Yauwa Saifuddeen juya ka kalli tv kaga sun fara haska hirar da tayi damu yau da safen,
kaga wannan itace Zaleeha sabuwar mai gabatar da shirin babu nakasashe sai ragon."
da sauri ya maida kanshi ga tv ganin an d'auke fuskarta an haska fuskar Ishaq ya sashi jan dogon tsaki tare da yin mgnar zuci.
"Yauwa kaga wannan surutaccen ya janye min hankali da d'an banzai surutunshi kafin in juyo sukuma sarakan azarbab'i sun cire fuskarta sun hasko min sufkar wannan gardin,
sai ya kuma ja tsaki tare da buge k'eyar Ishaq da yaketa murmushin jin dad'in shirin.
sai kusan 4to5 minutes kafin suka sake nuno fuskarta inda take cewa.
"Eh lallai kam na yarda Nakasa ba kasawa bace, tunda gashi kunayin komai kamar sauran masu cikekkiyar halitta."
tsaki ya kuma ja ganin an kuma nuno fuskar Ishaq,
Salisu kuwa gaba d'aya hankalin shi na kan Saifuddeen d'in dan ya fahimci ya bawa kallon tv mahimmanci a ranshi yace.
"Kamar yana jin me suke fad'i."
sai ya kuma yi murmushi ganin yadda Saifuddeen keta lumshe idanu da sauk'e sassanyar ajiyan zuciya."
a haka dai har aka gama shirin,
sannan suka salami Ishaq suka tafi.
Washe gari kuwa kamar yadda Salisu ya fad'in haka yayi ya kawowa Saifuddeen motar da tayi matuk'ar bawa kowa mamki dan motace ta kud'i kimanin million uku da rabi,
ga kuma Sule direba.
Sosai darajar Salisu ta kuma k'aruwa a idanun makusanta Saifuddeen.
Daga ranar Ahmad kuwa ya kasa ya tsare akan ala dole Saifuddeen ya daina tallan leda,
ruwa da omo kuwa maiso yazo shagonsu ya saya,
haka tasa dole Saifuddeen ya dena yawo a kasuwa yana gararamba,
sai dai ya ajiye yaro d'aya mai wul baro,
wanda yake cika baronshi da leda ya rink'a kaiwa duk costumes d'in Saifuddeen shago-shago suna bashi kud'in ya kawowa Saifuddeen inda shi kuwa yake sallaman yaron da dubu biyu kullum,
haka yayiwa Ado dad'i sosai dan cikin awa uku yake gama raba ledan sannan ya dawo yaci gaba da dakon kayan mutane.
A kwana a tashi asarar mai rai.
Lokacin yaci gaba da tafiya,
tuni Saifuddeen harkalla taci gaba ya gama biyan bashin daya amsa a shagonsu wanda ya cikata ya sayi gidanshi,
ya kuma k'ara sayan wata dalleliyar mota mai d'an karen kyau da tsada.
Ya kuma jonawa Hayatuddeen da Faruq makarantar da suke son,
ya sayawa Hayatuddeen mashin d'in U.D sabuwa dal a leda.
Hayatuddeen kuwa rawan kai sai abinda ya k'aru ya k'ara sabawa da abokanshi su Zakariyya sosai tunda yanzu makarantarsu d'aya kuma duk su hud'u sunada U.D
Sosai Sule direba ya saba da Saifuddeen yana gane body language d'inshi sosai,
duk inda zaije Sule ke kaishi a sabuwar motarshi,
inda ya b'ar d'ayar kuma wa Ummi.
Salisu da Warisu duk sunyi aure,
Ahmad ma an aura mishi Raliya,
kuma suna nan cikin gidan da yake Ahmad bai k'arisa ginin gidanshi ba shiyasa,
Saifuddeen yace to yazo ya zauna a cikin d'aya daga cikin part d'in nan dake sashin daman gidan suna zamansu lami lafiya sai tsananin son haihuwa da Ahmad keyi musamman d'iya mace shiyasa yasa Raliya dole ta rink'a kiranshi Abban Farida kamar da wasa sai sunanshi ya koma haka dan sai ya zama su Ummi dasu Rahma duk haka suke kiranshi.
Salisu kuwa tuni ya d'auko kakarshi Iya shatu ta bar Dukku.
Mudassir kuwa bunsurune na Mamajo fir yak'i maida hankali kan batun aure sai tara buhun 'yan mata.
Ishaq kuwa shima har yau baiyi aureba da zaran an mishi mgnar aure sai yace wai baiga matar data mishi bane,
duk sanda ya fad'i haka Saifuddeen kan ce mishi to wai da wanne idon zaiga matar da zata mishin,
yakanyi dariya yace da idon zuciya zai ganta.
To uban gayya Saifuddeen kuwa tun randa ya fara ganin fuskar Zaleeha a tv Allah ya jarabci zuciyarshi da wata zazzafar k'aunarta mai kashe zuciya da jiki,
Allah da ikonshi kuwa bai tab'a ganinta eyes to eyes ba duk da yanzu yana yawan zuwa k'ungiyar tasu wai ko Allah zaisa su had'u amman ina,
ko dan yawanci Zaleeha k'auyuka takebi tana hira da nakasassunne shiyasa basu fiye had'uwa ba,
amman fa duk ran jumma'a shabiyu da rabi nayi zai kunna tv tashar Farin wata ya kalli program d'inta da take gabatarwa.
ido ta zura mishi ba tare da ta k'arisa sauk'owanba hakama Raliya ido ta zura mishi,
shi kuwa baima san sunayi ba yana zare bel d'in yayi k'asa da dogon wondon Blue Jeans dake jikinshi ya rage dagashi sai d'an gajeren wondo dake jikinshi, sawunshi ya zare kana ya tsallake wondon inda ya sab'uleshi ya nufi hanyar d'akinshi tare da cilla bel d'in a tsakiyar parlour,
sai kuma ya fara kiciniyar cire rigarshi tare da cewa.
"Nima bari inje inyi wonka dan yau a masallacin fad'ar jiha zamuyi salla dasu Imran dasu Sulaiman Zakariyya shi yace yama je tun d'azu."
tsayawa yayi tare da juyawa da sauri jin Raliya na mishi mgna cikin tsawa take ce mishi.
"Wai kai kam Hayatuddeen wanne irin yarone mara kan gado,
kalli yadda ka watsa mana parlour dan tsabar sakarci da sakalci inda ka cire wondonka nan kake bar mana shi wato kai gaka auta mai buhun sakalci uwar wa zata tattara maka kwamutsan naka to da ka barshi?."
wani dogon tsaki yaja tare da cewa.
"Uwata mana ce miki akayi bani da gatane banza kawai uwar sa ido."
yana fad'in haka yayi shigewarsa d'an k'aramin side inshi,
ita kuwa Raliya taita zumbura baki dan Ummi ta sata tattaramishi kayanshi daya watsar.
Saifuddeen kuwa yana fita yaci karo da Salisu wanda shine ya d'aukeshi suka nufi hanyarsu da zata sadasu da titin tutun wada,
mik'ewa sukayi direct har kusa da mashigar G.S.U cikin nitsuwa Salisu ke draving suna gab da shiga gate d'in.
Jonapwd k'ungiyar nakasassu ta jihar kenan Salisu ya juyo cikin nitsuwa da kula ya kalli Saifuddeen tare da cewa.
"Motocin nan da mukayi mgnarsu last week sun iso jiya,
shiyasa nazo da nufin muje ka gansu ka zab'i kalan da kakeso a ciki,
dan gsky zamanka ba mota baiyiba,
tunda ko bazaka yi tuk'iba zamu iya samar maka amintaccen direba da zai rink'a kaika duk inda kakeso da kai da Ummi kafin Hayatuddeen ya k'ara girma."
murmushi Saifuddeen yayi tare da gyara zamanshi duk da yaga Salisun yayi parking kai ya jinjina tare da rubuta mishi.
"Bank'i shawararku bafa sai dai kuda kanku kunsan cewa yanzu bani da kud'in a k'asa dan na yashe duk asusuna nayi hidimar k'aurannan to kuma bani son abu da bashi."
a take fuskar Salisu ta sauya yanayi,
cikin sanyin sauti yace.
"Bashi kuma! Saifuddeen yanzu ashe dama kayana ba naka bane,
ashe dan ka d'auki mota d'aya rak cikin jerin motoci kusan takwas wanda kaine silar samar min jarinsu sai ya zama wani abu?."
Kai ya rink'a jujjuyawa cikin nuna alamun ba haka bane,
ganin haka yasa Salisu cewa.
"To kada ka sake kiramin kalmar bashi a tsakaninmu kuma ko bakaje ka zab'i kalar da kake soba ni zan zab'a maka da kaina gobe zan kawo maka ita har gida,
kuma in ba matsala a cikin yaran da suke wonke mana motocin akwai wani yaro Sule yanada nitsuwa ya kuma iya tuk'i na mutunci sai ya dawo nan ya rink'a kaiku duk inda kuke buk'ata zai kuma iya kula da shuke-shuken gidan in yaso duk wata ka rink'a biyanshi abinda nake biyanshi,
to dama kullum ina bashi kud'in abinci,
to kaga kai ba sai kayi ta bashi kud'in abinciba sai Ummi ta rink'a zuba mishi shida baba maigadi ko?." ya k'arishe mgnar cikin yanayin tambaya.
kai ya jinjina mishi tare da rubuta mishi.
"To ba matsala kayi yadda kaga ya dace."
cikin jin dad'in amincewar Saifuddeen d'in yace.
"To ba matsala."
Daga nan suka fito suka shiga cikin harabar wurin,
kai tsaye office d'in Ishaq suka nufa,
jin motsin bud'e k'ofarne yasa Ishaq juyawa da sauri sai ya kuma mik'e da sauri jin muryar Salisu,
numfashi ya shak'a tare da cewa.
"Lalle marhabin da manyan bak'i."
jin Saifuddeen ya rik'e hannunshi ya sashi juyawa gareshi tare da cewa.
"Kai amman naji haushi wlh kaga da kazo awa uku da suka wuce da ka had'u da Zaleeha sabuwar ma'akaciyar gidan radio vision FM gombe wacce take gabatar da shirin *Babu nakasasshe sai rago* yau dani mukayi hira na d'an bata tarihin rayuwata ka ko san dole zaka shiga ciki."
shiru yayi jin Saifuddeen ya rufe mishi baki da hannu tare da zaro wayarshi da hannunshi d'aya kana ya rubuta mishi text.
"Kai dan Allah ka huta mana wai bakinka bai gajiya da surutune? to ni ka bani ruwan sha tukun."
da sauri ya zaro wayarshi jin shigowar sak'o yasan Saifuddeen ne ya mishi mgn,
dariya yayi sanda ya karanta kana yace.
"To sarkin k'warafi ga wuri ku zauna."
sai kuma ya d'anyi taku biyu zuwa uku ya isa gaban firiji ruwan sanyi ya d'auko musu sannan yazo kusa dasu,
Salisu kam har yau bai dena mamakin yadda abota ta kasance tsakanin makaho da kurmaba suna kuma fahimtar juna over,
amsar ruwan sukayi saida suka d'an sha sannan suka ci gaba da hira amman banda Saifuddeen dan TV yake kallon tashar Farin wata wanda duk had'e suke da vision sosai ya zubawa TV idanu yana karanta rubutun daya bayyana a fuskar tv inda aka rubuta Babu nakasasshe sai rago, sosai Saifuddeen ya maida hankalin shi kan tv ganin sun hasko fuskar wata kekyawar budurwa mai cikar haiba,
lips d'inta ya zubawa idanu dan yana son gane abinda zata fad'a da kyau,
wani irin sassanyan ajiyan zuciya yayi jin wani abu na yana zirta cikin zuciyarshi har zuwa kwanyar kanshi ganin yadda take motso labb'anta wani sassanyar ajiyan zuciya ya kuma yaja a hankali ya sauk'e jin zuciyarshi na bugawa da sauri-sauri,
wani irin shauk'i ne mai cike da farin ciki ya ziyarci zuciyarshi da gangar jikinshi,
ina ya kasa kauda idanunshi a kanta,
da kyar ya juyo a fizge ya kalli Ishaq da yake tab'ashi yana ce mishi.
"Yauwa Saifuddeen juya ka kalli tv kaga sun fara haska hirar da tayi damu yau da safen,
kaga wannan itace Zaleeha sabuwar mai gabatar da shirin babu nakasashe sai ragon."
da sauri ya maida kanshi ga tv ganin an d'auke fuskarta an haska fuskar Ishaq ya sashi jan dogon tsaki tare da yin mgnar zuci.
"Yauwa kaga wannan surutaccen ya janye min hankali da d'an banzai surutunshi kafin in juyo sukuma sarakan azarbab'i sun cire fuskarta sun hasko min sufkar wannan gardin,
sai ya kuma ja tsaki tare da buge k'eyar Ishaq da yaketa murmushin jin dad'in shirin.
sai kusan 4to5 minutes kafin suka sake nuno fuskarta inda take cewa.
"Eh lallai kam na yarda Nakasa ba kasawa bace, tunda gashi kunayin komai kamar sauran masu cikekkiyar halitta."
tsaki ya kuma ja ganin an kuma nuno fuskar Ishaq,
Salisu kuwa gaba d'aya hankalin shi na kan Saifuddeen d'in dan ya fahimci ya bawa kallon tv mahimmanci a ranshi yace.
"Kamar yana jin me suke fad'i."
sai ya kuma yi murmushi ganin yadda Saifuddeen keta lumshe idanu da sauk'e sassanyar ajiyan zuciya."
a haka dai har aka gama shirin,
sannan suka salami Ishaq suka tafi.
Washe gari kuwa kamar yadda Salisu ya fad'in haka yayi ya kawowa Saifuddeen motar da tayi matuk'ar bawa kowa mamki dan motace ta kud'i kimanin million uku da rabi,
ga kuma Sule direba.
Sosai darajar Salisu ta kuma k'aruwa a idanun makusanta Saifuddeen.
Daga ranar Ahmad kuwa ya kasa ya tsare akan ala dole Saifuddeen ya daina tallan leda,
ruwa da omo kuwa maiso yazo shagonsu ya saya,
haka tasa dole Saifuddeen ya dena yawo a kasuwa yana gararamba,
sai dai ya ajiye yaro d'aya mai wul baro,
wanda yake cika baronshi da leda ya rink'a kaiwa duk costumes d'in Saifuddeen shago-shago suna bashi kud'in ya kawowa Saifuddeen inda shi kuwa yake sallaman yaron da dubu biyu kullum,
haka yayiwa Ado dad'i sosai dan cikin awa uku yake gama raba ledan sannan ya dawo yaci gaba da dakon kayan mutane.
A kwana a tashi asarar mai rai.
Lokacin yaci gaba da tafiya,
tuni Saifuddeen harkalla taci gaba ya gama biyan bashin daya amsa a shagonsu wanda ya cikata ya sayi gidanshi,
ya kuma k'ara sayan wata dalleliyar mota mai d'an karen kyau da tsada.
Ya kuma jonawa Hayatuddeen da Faruq makarantar da suke son,
ya sayawa Hayatuddeen mashin d'in U.D sabuwa dal a leda.
Hayatuddeen kuwa rawan kai sai abinda ya k'aru ya k'ara sabawa da abokanshi su Zakariyya sosai tunda yanzu makarantarsu d'aya kuma duk su hud'u sunada U.D
Sosai Sule direba ya saba da Saifuddeen yana gane body language d'inshi sosai,
duk inda zaije Sule ke kaishi a sabuwar motarshi,
inda ya b'ar d'ayar kuma wa Ummi.
Salisu da Warisu duk sunyi aure,
Ahmad ma an aura mishi Raliya,
kuma suna nan cikin gidan da yake Ahmad bai k'arisa ginin gidanshi ba shiyasa,
Saifuddeen yace to yazo ya zauna a cikin d'aya daga cikin part d'in nan dake sashin daman gidan suna zamansu lami lafiya sai tsananin son haihuwa da Ahmad keyi musamman d'iya mace shiyasa yasa Raliya dole ta rink'a kiranshi Abban Farida kamar da wasa sai sunanshi ya koma haka dan sai ya zama su Ummi dasu Rahma duk haka suke kiranshi.
Salisu kuwa tuni ya d'auko kakarshi Iya shatu ta bar Dukku.
Mudassir kuwa bunsurune na Mamajo fir yak'i maida hankali kan batun aure sai tara buhun 'yan mata.
Ishaq kuwa shima har yau baiyi aureba da zaran an mishi mgnar aure sai yace wai baiga matar data mishi bane,
duk sanda ya fad'i haka Saifuddeen kan ce mishi to wai da wanne idon zaiga matar da zata mishin,
yakanyi dariya yace da idon zuciya zai ganta.
To uban gayya Saifuddeen kuwa tun randa ya fara ganin fuskar Zaleeha a tv Allah ya jarabci zuciyarshi da wata zazzafar k'aunarta mai kashe zuciya da jiki,
Allah da ikonshi kuwa bai tab'a ganinta eyes to eyes ba duk da yanzu yana yawan zuwa k'ungiyar tasu wai ko Allah zaisa su had'u amman ina,
ko dan yawanci Zaleeha k'auyuka takebi tana hira da nakasassunne shiyasa basu fiye had'uwa ba,
amman fa duk ran jumma'a shabiyu da rabi nayi zai kunna tv tashar Farin wata ya kalli program d'inta da take gabatarwa.