Sashe 106
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zaleeha kuwa daga ma'aikatan nasu gidan kakar tasu ta koma,
don dama kwana uku ta roƙi Baba Malam daya barta tayi, kuma da yake gidan mahaifiyarshi ce sai bai hanata ba.
Kafin ma ta dawo tuni Ziyada ta gama haɗa musu komai na girki,
tuwon ɗanyar shinkafa da miyar kase,
tana ganin haka tace.
"Ziyada ina Zakariyya kuma da tsohuwar nan sukaje, suka barki ke ɗaya a gida?."
Cikin yanayin nutsuwarta irin na Maryam sak tace.
"Sun tafi gidansu abokinshi Hayatuddeen."
Tana warware naɗin gyalen hijabin dake jikinta tace.
"Sun daɗe da tafiya ne?."
Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.
"Eh tun da akayi sallan la'asar suka tafi."
kai ta jinjina kana ta zaro wayarta ta danna ƙiran number'n Zakariyya.
Shi kuwa Zakariyya lokacin suna parlour'n Ummi shida Hayatuddeen da Raliya, sunata tsiya wa Hajja Inna, ita kuwa Hajja inna
sai surfa musu boris takeyi,
Ummi kuwa sai nan-nan takeyi da hajja Inna dan taji dad'in zuwan kakar abokin autan nata, sosai takejin son tsohuwar a ranta, musamman yadda ta nuna tana masifar son Saifuddeen ɗinta.
Ta tasashi gaba tana yabo harda kukanta tana.
"Allah sarki bawan Allah, yaro kyakkyawa, Allah ya jarabceshi da nakasa,
ganshi kuwa kamar balarabe."
Sai kuma ta juyo ta kalli Ummy tare da cewa.
"Wannan yaron naki abin sone da tausayawa ga ko wanne mutum ɗan Adam me imani, ki godewa Allah daya azurtaki da samunsa a matsayin ɗa,
wasu suna can sun haifi lafi yayyun yara amman sai ki samu yaran munanane kamar kashin dare,
kinga ko gwara miki kyakkyawa fari ƙal nakasasshen."
Hayatuddeen ne yayi dariya sosai tare da cewa.
"Kai tsohuwar nan munana sun boni a wajenki."
Zakariyya ne ya zaro wayarshi dake suwa, wacce take cikin aljihun wondonshi yana cewa.
"Itafa sam bata son mummunan mutum, in taga kyakkyawan mutun kuma wai ji take kamar ta dawo dashi ɗanta."
Dariya sukayi baki ɗaya,
kana shiko Zakariyya ya amsa kiran Zaleeha tare da cewa.
"Hello Adda Zalees ya akayi ne?."
Sai ya kuma yafito Hayatuddeen tare da mishi alamun ga mutuniyarshi fa.
amsar wayar yayi ya kara a kunne tare da cewa.
"Adda Zalees nayi fushi dake muka dawo ko kizo ki duba kyakkyawan hammana da jiki ko."
Murmushi tayi tare da cewa.
"Afwan autan gidansu."
da sauri yace.
"No autan Ummi dai zakice, gidanmu kam ai kwanannan ma Hamma na zai fara ƙenƙesa mana yara sabbin zubi, ƴan yayi kuma kyawawa, irin yaran da Hajja inna ke masifar so."
Ƴar dariya tayi tare da cewa.
"To aku sarkin zance, please ka cewa Zakariyya su biya Abba bakery ya saya min pizza dan Allah."
Da sauri yace.
"To ba matsala karki damu zan bashi abin daɗi ma ya kawo miki, cikin na Hamma na zan ɗiba miki."
Da sauri tace.
"A a ni dai pizza kawai nake so."
Bai kulataba ya katse ƙiran.
sannan ya amshi kular da Raliya ta haɗa musu tsarabar Kai kayan lefen jiya."
Daga nan suka miƙe zasu tafi, har sun kusa fita daga parlour Hajja Inna ta juyo ta kalli Saifuddeen murmushi ya mata, haka itama murmushin tayi mishi sannan ta kalli Ummi cikin halin tsufa tace.
"Kin ga ƴata kada ki yarda ki bari wannan kyakkyawan ɗan naki ya auro miki mummunar surka,
in kuwa kika bari ya auro miki mummunar surka, to shike nan ya ɓata miki wannan kyakkyawar zuriyar taki, dan tabbas dole wata rana sai ta haifo muku mai kama da ita,
dan ni dai anmin na gani, yanzu in kika kalli Zahira zakice ba jinin ahlina bane dan ita kamannin dangin uwarsu tayi yo."
Zakariyya ne ya tura baki tare da cewa.
"Kefa kince baki da goni a duniya sai mai kyau, to sam gigin tsufarki baya gaya miki gsk, ya zaki rinƙa sarata ina ji, aikin kawai."
Dariya sukayi dukansu ganin yadda ta kamo hannun Zakariyya tana cewa.
"A a kada kaji haushi shalelena, ai kai sak da kakanka baban babanka kakeyi, shiyasa kai da Ahmad kuke tsananin kama,
Zaleeha da Ziyada kuwa dani suke kama, bakaga Zaleeha ko gashi irin nawa ta gado ba?."
Janye hannunshi yayi tare da kunna machine ɗinsa, kana ya amshi kular da Hayatuddeen ke miƙo mishi ya saka a cikin ɗan kondon dake gaban machine ɗin.
Sai ya kuma kallon Hayatuddeen dake miƙo mishi 10k kana yace.
"Ga tukuicinmu na jiya."
Dariya Zakariyya yayi tare da cewa.
"Kace abin namu ne babu ƙaranci, ashe ko zamuyi casu a bikinga."
Sosai Ummi ke murmushi dan Zakariyya sak autan tane da shirmensa.
Sosai hajja Inna ta ɗale saman machine ɗin na Zakariyya, kamar ba tsohuwa ba,
da sauri Ummi ta riƙe kai ganin yadda Zakariyya ya figi machine ɗin ya fita a guje.
Hayatuddeen ne ya kece da dariya tare da cewa.
"Hege Zakary namu, wata rana zai ɓarar da hagwaran tsohuwar nan a titi yaseen."
Dariya Raliya tayi tare da cewa.
"Ai harda karya mata ƙafa."
Daƙuwa Ummi tayi musu tare da juyawa tayi cikin gida sannan suma sukabita a baya.
Su kuwa Zakariyya na isa ya miƙawa Zaleeha kular da Hayatuddeen yabasa yayi, dan tuni shi yaci a can yayi haniƙan,
ita kuwa Zaleeha kamar bazata buɗe kularba sai ta kuma buɗe, ganin abinda ke cikine ya sata yin murmushi sannan ta miƙe tsaye, lemon exotic ta ɗauko acikin fridge kana ta dawo ta zauna, haka ta fara cin pepper chicken ɗin dayaji onion, tanaci tana latsa wayarta,
Ziyada kuwa tuni tabi bayan Hajja inna da ta kirata wai tazo ta cire mata sarkan da ta sanya awuyanta, kasancewar idanun tsufa gareta bazata iya cirewa kanta ba.
Ƙarfe tara dai-dai Zaliha Ziyada da Zakariyya dukansu suna zaune parlour'n Hajja ina sunata hirarsu irin ta ƴan uwan juna,
yayinda kakarsu ke tsakiyarsu,
tana kallon kyawawan jikokinta da take matuƙar so arayuwa, dan
duk cikin jikokinta tafi son Ahmad da kuma Zakariyya.
Sam bata shiri da Habu a cewarta wai shi baya dariya.
A can New G.R.A kuwa kasan cewar yau girkin Mamane dan Mamy yau ta ƙare kwana biyunta.
Suna dawowa sallan isha Ahmad da Habu sukayi cikin gida.
Da sauri Habu ya tsaya, cikin mamaki yace.
"Ya Ahmad kalli can."
Da sauri Ahmad ya isa wurin da Habu ke nuna mishi, ganin
kayan lefen Zaleeha ne da aka kawo jiya watse aƙasa, setin gaba ɗaya akwatuna 30 dasu tarkacen gishiri da goro duk an watsosu waje,
cikin tsananin Al'ajabin halin Mama da tsaurin ido irin nata yace.
"Innalillahi! Habu tayani mu kwashesu, tunkan Baba Malam yazo yagani, nasan bazaiji daɗi ba aransa ba."
Da sauri suka fara tattara kayan, sai kuma duk suka tsaya tare dayin shiru, sakamakon jin muryar mahaifinsu ta window parlour'n shi.
"Ku barsu a wurin ko tsinke kada ku ɗaga, ku wuce ku bar wurin."
Shiru sukayi cikin tsananin tarin damuwa dan dagajin muryar Baba malam yana cikin tsananin baƙin ciki, muryarshin ce ta katse musu tunanin da sukeyi.
"Ku bar wurin ko nace!." ya ƙarishe maganar cikin bada umarni irin na fusata.
Da sauri sukace.
"Toh".
sannan suka juya, kowa ya nufi ɗakin mahaifiyarshi.
Gefen Mamy Ahmad ya zauna cikin ƙunan rai yace.
"Please Mamy kije ki bawa Baba malam haƙuri, naga ranshi ya matuƙar ɓaci, kice yayi haƙuri ya barmu mu kwashi kayan, in yaso mushigo dashi nan ɗakinki."
Murmushi Mamy tayi tare da cewa.
"Hmmm Ahmad ai wannan ba hurumi na bane,
ku bar kayan kamar yadda ya umarceku,
Mamanku ta zauna da Malam kusan tsawon shekaru 30 kenan yau, amman har yau bata san waye Malam ba, bata taɓa ƙureshi ba,
amman da dukkan alama yau zata san kaɗan daga cikin halaiyarsa, idan ransa ya ɓaci,
shi acikin ruwan sanyi zai dafata."
Jin haka yasanya Ahmad cewa.
"Hmmm kai Mama tanada matsala Wallahi, mutum duk haƙurinshi sai ta ƙureshi."
"Kaje kaci abinci ka dena zama da yunwa."
Mamy ta umarceshi cikin son kauda zancen, kasancewar bata son tayi mgnar kishiyarta, dan wannan shi ke ɓata alaƙar zuciyar yaro da matar ubanshi.
Ƙarfe tara dai-dai Mama ta shiga parlour'n Baba Malam, tare da yin sallama can ƙasan maƙoshi, ta yadda shi baima jitaba.
A kan kujera ta sameshi zaune ya zubawa TV idanu yana kallon BBC News.
Kan dinning table ta kai dubanta, gani tayi yanda ta ajiye abinci, yana nan ayanda yake, da alama babu wanda ya taɓa ko food flask ɗin bare akai ga ci,
juyowa tayi ta maida kallonta kan fuskarshi da ta ɓoye ɓacin ransa,
ta sani koda bazaici abinciba to tabbas zaisha tea,
dan haka taku uku zuwa biyar ne yakaita gaban dinning area,
cup ta ɗauka sannan ta haɗa mishi tea kamar yadda ta saba,
a hankali tazo ta ajiye mishi cup ɗin a kan table ɗin dake gabanshi, wanda yawanci nan yake miƙe sawunshi idan yana zaune akan kujera.
danne ɓacin ranta tayi dan yanzu so take ta gwada kirsa tunda taga hayagagar bata kamashi,
gefenshi ta zauna tare da cewa.
"Ga tea ɗinka nan nahaɗa ma kada yayi sanyi."
shiru yayi baice ƙala ba, ganin yadda yayi kamar babu wani mahaluƙin dake kusa dashi, yasanya
cikin tsareshi da ido taƙira sunanshi.
"Malam!."
Baima juyo ya kalleta ba bare tayi zaton ko zai amsa mata,
saima kaɗa ƙafafunshi da ya farayi a hankali.
shi kuwa wani irin tafarfasa zuciyarsa keyi,
yadda tazo tayi ta mishi ihu da haushi a kanshi gaban yaranshi da uwar gidanshi, shine ke ƙara ɓata masa rai, sam bata sa hankali da nutsuwa cikin lamuranta.
Kusa dashi ta kuma matsowa tare da cewa.
"Malam magana nake so muyi da kai fa."
Bai bi ta kantaba bare ya saurareta saima ƙara volume ɗin TV da yayi.
Cikin takaicin abin tace.
"Ya kamata muyi magana ta fahimtar juna,
a bani matsayina da damata a matsayina na uwar yarinya,
ni nasan Zaleeha bata son wannan nakasasshen, ta tsaida gwaninta, harma ta bashi daman ya turo komai na aure, tunda dama iyayenshi kam sun zo kuma ka sansu ba baƙin fuska bane,
d'an manya ne gaba da bayansa."
don dama kwana uku ta roƙi Baba Malam daya barta tayi, kuma da yake gidan mahaifiyarshi ce sai bai hanata ba.
Kafin ma ta dawo tuni Ziyada ta gama haɗa musu komai na girki,
tuwon ɗanyar shinkafa da miyar kase,
tana ganin haka tace.
"Ziyada ina Zakariyya kuma da tsohuwar nan sukaje, suka barki ke ɗaya a gida?."
Cikin yanayin nutsuwarta irin na Maryam sak tace.
"Sun tafi gidansu abokinshi Hayatuddeen."
Tana warware naɗin gyalen hijabin dake jikinta tace.
"Sun daɗe da tafiya ne?."
Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.
"Eh tun da akayi sallan la'asar suka tafi."
kai ta jinjina kana ta zaro wayarta ta danna ƙiran number'n Zakariyya.
Shi kuwa Zakariyya lokacin suna parlour'n Ummi shida Hayatuddeen da Raliya, sunata tsiya wa Hajja Inna, ita kuwa Hajja inna
sai surfa musu boris takeyi,
Ummi kuwa sai nan-nan takeyi da hajja Inna dan taji dad'in zuwan kakar abokin autan nata, sosai takejin son tsohuwar a ranta, musamman yadda ta nuna tana masifar son Saifuddeen ɗinta.
Ta tasashi gaba tana yabo harda kukanta tana.
"Allah sarki bawan Allah, yaro kyakkyawa, Allah ya jarabceshi da nakasa,
ganshi kuwa kamar balarabe."
Sai kuma ta juyo ta kalli Ummy tare da cewa.
"Wannan yaron naki abin sone da tausayawa ga ko wanne mutum ɗan Adam me imani, ki godewa Allah daya azurtaki da samunsa a matsayin ɗa,
wasu suna can sun haifi lafi yayyun yara amman sai ki samu yaran munanane kamar kashin dare,
kinga ko gwara miki kyakkyawa fari ƙal nakasasshen."
Hayatuddeen ne yayi dariya sosai tare da cewa.
"Kai tsohuwar nan munana sun boni a wajenki."
Zakariyya ne ya zaro wayarshi dake suwa, wacce take cikin aljihun wondonshi yana cewa.
"Itafa sam bata son mummunan mutum, in taga kyakkyawan mutun kuma wai ji take kamar ta dawo dashi ɗanta."
Dariya sukayi baki ɗaya,
kana shiko Zakariyya ya amsa kiran Zaleeha tare da cewa.
"Hello Adda Zalees ya akayi ne?."
Sai ya kuma yafito Hayatuddeen tare da mishi alamun ga mutuniyarshi fa.
amsar wayar yayi ya kara a kunne tare da cewa.
"Adda Zalees nayi fushi dake muka dawo ko kizo ki duba kyakkyawan hammana da jiki ko."
Murmushi tayi tare da cewa.
"Afwan autan gidansu."
da sauri yace.
"No autan Ummi dai zakice, gidanmu kam ai kwanannan ma Hamma na zai fara ƙenƙesa mana yara sabbin zubi, ƴan yayi kuma kyawawa, irin yaran da Hajja inna ke masifar so."
Ƴar dariya tayi tare da cewa.
"To aku sarkin zance, please ka cewa Zakariyya su biya Abba bakery ya saya min pizza dan Allah."
Da sauri yace.
"To ba matsala karki damu zan bashi abin daɗi ma ya kawo miki, cikin na Hamma na zan ɗiba miki."
Da sauri tace.
"A a ni dai pizza kawai nake so."
Bai kulataba ya katse ƙiran.
sannan ya amshi kular da Raliya ta haɗa musu tsarabar Kai kayan lefen jiya."
Daga nan suka miƙe zasu tafi, har sun kusa fita daga parlour Hajja Inna ta juyo ta kalli Saifuddeen murmushi ya mata, haka itama murmushin tayi mishi sannan ta kalli Ummi cikin halin tsufa tace.
"Kin ga ƴata kada ki yarda ki bari wannan kyakkyawan ɗan naki ya auro miki mummunar surka,
in kuwa kika bari ya auro miki mummunar surka, to shike nan ya ɓata miki wannan kyakkyawar zuriyar taki, dan tabbas dole wata rana sai ta haifo muku mai kama da ita,
dan ni dai anmin na gani, yanzu in kika kalli Zahira zakice ba jinin ahlina bane dan ita kamannin dangin uwarsu tayi yo."
Zakariyya ne ya tura baki tare da cewa.
"Kefa kince baki da goni a duniya sai mai kyau, to sam gigin tsufarki baya gaya miki gsk, ya zaki rinƙa sarata ina ji, aikin kawai."
Dariya sukayi dukansu ganin yadda ta kamo hannun Zakariyya tana cewa.
"A a kada kaji haushi shalelena, ai kai sak da kakanka baban babanka kakeyi, shiyasa kai da Ahmad kuke tsananin kama,
Zaleeha da Ziyada kuwa dani suke kama, bakaga Zaleeha ko gashi irin nawa ta gado ba?."
Janye hannunshi yayi tare da kunna machine ɗinsa, kana ya amshi kular da Hayatuddeen ke miƙo mishi ya saka a cikin ɗan kondon dake gaban machine ɗin.
Sai ya kuma kallon Hayatuddeen dake miƙo mishi 10k kana yace.
"Ga tukuicinmu na jiya."
Dariya Zakariyya yayi tare da cewa.
"Kace abin namu ne babu ƙaranci, ashe ko zamuyi casu a bikinga."
Sosai Ummi ke murmushi dan Zakariyya sak autan tane da shirmensa.
Sosai hajja Inna ta ɗale saman machine ɗin na Zakariyya, kamar ba tsohuwa ba,
da sauri Ummi ta riƙe kai ganin yadda Zakariyya ya figi machine ɗin ya fita a guje.
Hayatuddeen ne ya kece da dariya tare da cewa.
"Hege Zakary namu, wata rana zai ɓarar da hagwaran tsohuwar nan a titi yaseen."
Dariya Raliya tayi tare da cewa.
"Ai harda karya mata ƙafa."
Daƙuwa Ummi tayi musu tare da juyawa tayi cikin gida sannan suma sukabita a baya.
Su kuwa Zakariyya na isa ya miƙawa Zaleeha kular da Hayatuddeen yabasa yayi, dan tuni shi yaci a can yayi haniƙan,
ita kuwa Zaleeha kamar bazata buɗe kularba sai ta kuma buɗe, ganin abinda ke cikine ya sata yin murmushi sannan ta miƙe tsaye, lemon exotic ta ɗauko acikin fridge kana ta dawo ta zauna, haka ta fara cin pepper chicken ɗin dayaji onion, tanaci tana latsa wayarta,
Ziyada kuwa tuni tabi bayan Hajja inna da ta kirata wai tazo ta cire mata sarkan da ta sanya awuyanta, kasancewar idanun tsufa gareta bazata iya cirewa kanta ba.
Ƙarfe tara dai-dai Zaliha Ziyada da Zakariyya dukansu suna zaune parlour'n Hajja ina sunata hirarsu irin ta ƴan uwan juna,
yayinda kakarsu ke tsakiyarsu,
tana kallon kyawawan jikokinta da take matuƙar so arayuwa, dan
duk cikin jikokinta tafi son Ahmad da kuma Zakariyya.
Sam bata shiri da Habu a cewarta wai shi baya dariya.
A can New G.R.A kuwa kasan cewar yau girkin Mamane dan Mamy yau ta ƙare kwana biyunta.
Suna dawowa sallan isha Ahmad da Habu sukayi cikin gida.
Da sauri Habu ya tsaya, cikin mamaki yace.
"Ya Ahmad kalli can."
Da sauri Ahmad ya isa wurin da Habu ke nuna mishi, ganin
kayan lefen Zaleeha ne da aka kawo jiya watse aƙasa, setin gaba ɗaya akwatuna 30 dasu tarkacen gishiri da goro duk an watsosu waje,
cikin tsananin Al'ajabin halin Mama da tsaurin ido irin nata yace.
"Innalillahi! Habu tayani mu kwashesu, tunkan Baba Malam yazo yagani, nasan bazaiji daɗi ba aransa ba."
Da sauri suka fara tattara kayan, sai kuma duk suka tsaya tare dayin shiru, sakamakon jin muryar mahaifinsu ta window parlour'n shi.
"Ku barsu a wurin ko tsinke kada ku ɗaga, ku wuce ku bar wurin."
Shiru sukayi cikin tsananin tarin damuwa dan dagajin muryar Baba malam yana cikin tsananin baƙin ciki, muryarshin ce ta katse musu tunanin da sukeyi.
"Ku bar wurin ko nace!." ya ƙarishe maganar cikin bada umarni irin na fusata.
Da sauri sukace.
"Toh".
sannan suka juya, kowa ya nufi ɗakin mahaifiyarshi.
Gefen Mamy Ahmad ya zauna cikin ƙunan rai yace.
"Please Mamy kije ki bawa Baba malam haƙuri, naga ranshi ya matuƙar ɓaci, kice yayi haƙuri ya barmu mu kwashi kayan, in yaso mushigo dashi nan ɗakinki."
Murmushi Mamy tayi tare da cewa.
"Hmmm Ahmad ai wannan ba hurumi na bane,
ku bar kayan kamar yadda ya umarceku,
Mamanku ta zauna da Malam kusan tsawon shekaru 30 kenan yau, amman har yau bata san waye Malam ba, bata taɓa ƙureshi ba,
amman da dukkan alama yau zata san kaɗan daga cikin halaiyarsa, idan ransa ya ɓaci,
shi acikin ruwan sanyi zai dafata."
Jin haka yasanya Ahmad cewa.
"Hmmm kai Mama tanada matsala Wallahi, mutum duk haƙurinshi sai ta ƙureshi."
"Kaje kaci abinci ka dena zama da yunwa."
Mamy ta umarceshi cikin son kauda zancen, kasancewar bata son tayi mgnar kishiyarta, dan wannan shi ke ɓata alaƙar zuciyar yaro da matar ubanshi.
Ƙarfe tara dai-dai Mama ta shiga parlour'n Baba Malam, tare da yin sallama can ƙasan maƙoshi, ta yadda shi baima jitaba.
A kan kujera ta sameshi zaune ya zubawa TV idanu yana kallon BBC News.
Kan dinning table ta kai dubanta, gani tayi yanda ta ajiye abinci, yana nan ayanda yake, da alama babu wanda ya taɓa ko food flask ɗin bare akai ga ci,
juyowa tayi ta maida kallonta kan fuskarshi da ta ɓoye ɓacin ransa,
ta sani koda bazaici abinciba to tabbas zaisha tea,
dan haka taku uku zuwa biyar ne yakaita gaban dinning area,
cup ta ɗauka sannan ta haɗa mishi tea kamar yadda ta saba,
a hankali tazo ta ajiye mishi cup ɗin a kan table ɗin dake gabanshi, wanda yawanci nan yake miƙe sawunshi idan yana zaune akan kujera.
danne ɓacin ranta tayi dan yanzu so take ta gwada kirsa tunda taga hayagagar bata kamashi,
gefenshi ta zauna tare da cewa.
"Ga tea ɗinka nan nahaɗa ma kada yayi sanyi."
shiru yayi baice ƙala ba, ganin yadda yayi kamar babu wani mahaluƙin dake kusa dashi, yasanya
cikin tsareshi da ido taƙira sunanshi.
"Malam!."
Baima juyo ya kalleta ba bare tayi zaton ko zai amsa mata,
saima kaɗa ƙafafunshi da ya farayi a hankali.
shi kuwa wani irin tafarfasa zuciyarsa keyi,
yadda tazo tayi ta mishi ihu da haushi a kanshi gaban yaranshi da uwar gidanshi, shine ke ƙara ɓata masa rai, sam bata sa hankali da nutsuwa cikin lamuranta.
Kusa dashi ta kuma matsowa tare da cewa.
"Malam magana nake so muyi da kai fa."
Bai bi ta kantaba bare ya saurareta saima ƙara volume ɗin TV da yayi.
Cikin takaicin abin tace.
"Ya kamata muyi magana ta fahimtar juna,
a bani matsayina da damata a matsayina na uwar yarinya,
ni nasan Zaleeha bata son wannan nakasasshen, ta tsaida gwaninta, harma ta bashi daman ya turo komai na aure, tunda dama iyayenshi kam sun zo kuma ka sansu ba baƙin fuska bane,
d'an manya ne gaba da bayansa."