← Book details Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 110 OF 116

Sashe 110

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ita ko Rashida murmushi tayi tare da cewa.
"Ayyah Zaleeha zuk'ar zuciya da rud'in shaid'an na d'awainiya da ke sun hanaki ganin nagartan Saifuddeen.
Fatana Allah ya sanya al'khairi a aurenku."

Ishaq kuwa Zaleeha na fita ya biyo bayanta ranshi a matuk'ar b'ace,
parking lot ya nufa ganin haka Ado drivarnshi ya biyu bayanshi bud'e mishi marfin motar yayi.
Bayan ya shiga ya maida marfin ya rufe,
sannan ya shiga yaja motar suka fita,
suna hawa kan titin da kyau Ado ya juyo ya kalli uban gidan nashi cikin girmamawa yace.
"Ina zamu je?."
A takaice yace.
"Gidan Saufuddeen."

A parlour'n Ummi ya samu Saifuddeen shi kad'ai,
kamar babu kowa a gidan.
bayan sun gaisa ne da salon yadda suke mgna,
Ishaq ya rubutawa Saifuddeen duk yadda sukayi da Zaleeha yanzu,
yana gama karanta text d'in ya gyara zamanshi kana ya fuskanci abokin nashi cikin lumshe ido yayi wani tattausan murmushi tare da rubuta mishi.
"Cool down my friend.
kada ka damu da duk abinda zatayi."
cikin jin haushi Ishaq fuskaci abokin nashi da kyau kana yace.
"Saifuddeen ka hak'ura da Zaleeha mana tunda ba ita kad'ai bace d'iya mace,
ita mafa macece kamar kowa ya za'ayi wasu na binka kai kana binta tana ci maka zarafi, na gaji Ka rabu da yarinyar nan,
yarinyar da ikirari zata mutu in ka aureta kayi zuciya ka barta mana."
A hankali Ummi ta zame ta zauna a kujerar da Saifuddeen ya baiwa baya, ishaq kuma ba ganinta zaiba.
Gaba d'aya jikinta rawa yakeyi.
Tsoronto d'aya kada k'iyayya tasa Zaleeha ta cutar mata da d'anta, ya zatayi in wani abu ya kuma samun Saifuddeen d'inta d'a mafi soyuwa a zuciyarta d'an da yake k'arar da lokutanshi wurin sama mata farin ciki da kare martabarsu. tuni hawaye na zirya a kumatunta dan tana tausayawa zuciyar d'an nata da Allah ya jarbaceshi da son matar da bata sonshi.

Shi kuwa Saifuddeen kanshi ya jujjuya kana ya fara rubutawa ishaq mgna kamar haka.
"Uhmmm Ishaq ai duk cikekken masoyi zai jure karan tsana.
Zai jure kai kawo da zirga-zirga ako ina.
Kuma bazai nufi masoyinshi da hatsala ba.
Kuma ai ba'a son fushi a so sai dai hak'uri da juriya
domin yin fushi a so alamun rashin nasara ne, in sha Allah
dole ne fa sai Zaleeha ta shigo gidane dolen-dolenta sai taga aikin ginennen tab'on nan da tace sai na shayar da ita ruwan mmki, barni da ita zata gane kurenta!."
cikin mmki Ummi ta zuba musu ido ganin sun tafa kuma ishaq ya saki wani irin shak'iyin dariya.
"Saifuddeen kenan ya iya sarrafa harshe gashi daga fushi yasa ishaq dariya ko meye ya rubuta mishi sai Allah."
Ummi Ke fad'i a ranta lokacin data mik'e ta nufi bedroom nata dan bata son Saifuddeen ya gane taji zancensu.

Ita kuwa Zaleeha daga gidansu Rashida  gidan Hajja inna nufa,
tana shiga kawai ta tasa hajja inna a gaba ta bud'e wani sabon shafin kuka.
Zakariyya ne dake gugun kayanshi dana Ziyada ya ajiye dutsen gugan tare da cewa.
"To yau kuma me aka miki?."
cikin kuka take cewa hajja inna.
"Wallahi bana sonshi dan Allah ki cewa Baba malam yayi hak'uri kada ya min auren dole."
shiru tayi jin hajja Inna ta ja wani dogon tsaki,
kana ta b'alli tsallin goro ta afa a bakinta tare da taunashi,
kai ta karkace tare da cewa.
"To me ruwana a ciki, aure ne dai dole fa sai an aurar dake,
na gaji da zamanki a gidan d'ana."
Dariya sosai Zakariyya da Ziyada keyi sabida abin na hajja Inna ba mutunci.
suna cikin dariyar suka jiyo muryar Hayatuddeen da sauri Zakariyya ya tarbeshi cikin murna suka ruggume juna irin yar ruggumarnan ta gefe.
kana suka zauna bisa 2 sitter.
Bayan sun gaisa da Hajja Inna ne Ziyada ta gaida Hayatuddeen cikin mmki Hayatuddeen yake tambayar meyasa Zaleeha kuka,
Zakariyya ne yayi dariya tare da cewa.
"Wai kuka take dan za'a mata aure."
Dariyar shak'iyanci sukayi mata cikin dariyar Hayatuddeen yace.
"Ato yarinya da kin san kina tsoron auren mai yasa zakisa gaye ya turo iyayenshi."
Ziyada ce ta d'an kalleshi cikin yanayin d'an sabonta dashi tace.
"Ya Hayatuddeen ai bata son mijin ne shiyasa take kuka auren dole za'ayi mata."
da sauri ya matso kusa da Zaleeha wacce keta kuka hajja Inna kuwa nata aikin auna mata harara, cikin sanyi yace.
"Allah sarki Adda Zalee gsky ba'ayi miki adalciba a dai wannan zamanin mace kekyawa big girl kamarki ace an miki auren dole,
gsky dole kiyi kuka."
jin haka yasa Zaleeha fuskantarshi cikin kukan tace.
"Kuma ina da wanda nakeso sannan su had'ani da wani can banza ginennen tab'o."
kai ya jinjina mata tare da cewa.
"To meyasa bazakuyi mgna ta fahimtar junaba keda shi,
ki gaya mishi kinada wanda kikeso, kice mishi koda ya aureki bazai ji dad'in zama da keba,
in ya amince ya hak'ura shine nan kin huta in ya kafe ya nace kuma kiyi hak'uri kibi umarnin iyayenki."
Cikin kuka tace.
"Na tsaneshi bana sonshi ta yaya zan auri nakasasshe alhalin da lfyta."
shiru tayi ganin yadda a take fuskar Hayatuddeen ta canza launi da yanayi cikin had'e girar sama da k'asa mik'ewa yayi ya matsa gefenta tare da cewa.
"Zancen banza kenan, ashema baki da hujja, shi nakasasshe ba halittar Allah bane, ko a zatonki Nakasa kasawa ce,
aikin banza d'an adam da bai san k'arshenshiba yace yana kyaran larurar wani."
Gaba d'aya ran Hayatuddeen ya b'aci sosai sai yake tuno wata k'ilfa wata ran ayiwa Hamma Saifuddeen d'inshi irin wannan cin zarafin, haka kawai kalamanta sukayi masifar tayar mishi da hankali,
Hajja Inna ce tayi dariya tare da cewa.
"Ato ai duk mai bin bayan Zaleeha zai shak'i takaici, yo wani nakasasshen ma ai yafi mai cikar halitta haiba."
Ita kuwa Zaleeha cikin kuka tace.
"Bazaku gane bane. Gurgu nefa akan wheelchair yake rayuwa, kuma kurmane bayaji baya mgna."
Dam-dam zuciyar Hayatuddeen ya bada wasu tagwayen tarnaki mai cike da fargaba cikin zargin kai anya kuwa wannan bada Hammanshi take ba, cikin tsananin fargaba baki na rawa yace.
"Uhmmm me sunan shi ne!?."
cikin tarin tsanar tsuna taja wani dogon tsaki tare da mik'ewa kana tace.
"Wai Saifuddeen n!!!."
da sauri Zakariyya ya mik'e tsaye tare da cewa.
"Hamma Saifuddeen.
Shi kuwa Hayatuddeen cikin k'arfi ya fizgo hannunta tare da zaro idanunshi da sukayi jazir tuni hawaye na shatata a kumatunshi har kan gemunshi cikin rawan murya yace.
"K'arya ne wallahi Hamma na ba nakasasshe bane, domin nakasarsa bata zame mishi kasawa ba,
Ke da kike zagin nakasarsa kinada tabbacin naki lafiyar ne, da har kike inkarin ke da lafiyarki, to wlh yanzu kika fara kuka ko zaki mutu sai kin zama matar kurma kuma gurgun nan,
D'an uwane shine jigon rayuwar ahlinmu."
Sai kuma ya sake mata hannu ya koma ya zauna, Zakariyya ma tuni hawaye yake zubdawa, dan sai yanzu ya gane ashe Hamma Saifuddeen ne wanda yayarshi Zaleeha keta ƙi.
hakama Ziyada hawaye take zubdawa,
Hajja Inna kuwa cikin mmki tace.
"Hayatu, ashe ma Saifuddeen kyakkyawa ne ta samu har take rigima.
Wlh ni ban saniba."
Cikin zubda kwalla shima Hayatuddeen yace.
"Wlh Hajja Inna nima sai yanzu na gane data kira sunanshi da yanayin nakasarsa kuma,
na tuna ance min sunan matar da aka bashi Zaleeha ne."
ita kam Zaleeha juyawa tayi ta fita jin ƙaninta Zakariyya na cewa.
"Wlh nima ban san akan Hamma Saifuddeen bane take wannan haukan da ko inda take bazanma kallaba."

Hajja Inna ce ta katsesu da cewa.
"Ai kuwa ko mutuwa zatayi sai ta aureshi."
Sai ta kuma kalli Hayatuddeen cikin rarrashi tace.
"Kayi haƙuri kaji ko Hayatu, dan Allah kada ka gayawa Umminku da yayunka wannan batun in sha Allah Zaleeha zata tanƙwaru."
Kai ya gyaɗa mata alamar to,
sai ya kuma Kalli Zakariyya tare da cewa.
"Dama nazo nefa muje gidansu Imran muyi batun dinner ɗin da za'ayi a bikin ne, ina son mu tsara fita ta musamman a wurin," cikin bada ƙarfin guiwa Zakariyya yace.
"To muje, danko abu namune maganin a kwaɓemu."

Daga nan suka tafi gidansu Imran ƙanin ishaq.

Ita kuwa Zaleeha abu ya cakuɗe mata komai ya birkice mata,
Yanzu ba mai bin ta kanta ta lura Aunty Lubna da Zakariyya basu damu da dmuwar tata ba

Haka yasa dole ta ƙudurci son haɗuwa dashi ido da ido ayita ta ƙare.

A lissafi dai yau saura kwana biyar ne auren.
ganin har danginsu na Dukku sun fara zuwane ya ƙara tayar mata da hankalin.
Gashi haka nan take jin kamar ana ingzata da zugata kan tayi wani mummunan abu.
Shiyasa yau tunda safe taketa tura mishi text akan yazo gidansu zasuyi mgna mai mahimmanci ganin har yamma ba amsa ne yasa ta kira Ishaq bayan ta tuttura mishi saƙo dan Allah ya amsa kiranta,
Yana d'agawa cikin rawan murya alamun zata fara kuka tace.
"Dan Allah Malam Ishaq na rok'eka da manzon rahma kace yazo gidanmu inada mgna dashi."
cikin danne dariyarshi da sai yanzu kalamanta na wai sun ce mata irin larrarshi basa iya aure dariyar ya ɗan danne kana yace.
"Yaushe kike son yazo?."
Da sauri tace .
"Dan Allah yazo yau. Ban san in da zan sameshi ba da naje na sameshi."
wani munafukin murmushi ishaq yayi sannan yace.
"Ki duba hanyarshi zuwa bayan sallan isha."
Da sauri tace to kana ta katse kiran,
a take ta kira Bilkisu dan tasan itace zata tayata ci musu zarafi ta yadda sai sun tsani kawunansu ma, aiko Bilkisu najin shirin Zaleeha tace gata nan zuwa.
Chapter 110 · 0% Book details