Sashe 20
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Biyar na cika Salisu yazo nan suka kama hanyar Dukku, cikin sa'a suka isa da sauran rana.
Yauma kamar jiya tare da abokanshi sukayi bud'a baki.
ana idar da sallan asham suka tafi tabsir.
koda suka dawo suka ci abinci sannan suka raka Ahmad.
Yana dawowa ya sumu Ummi a tsakar gida,
bisa taburma Rahma na gefenta tana bacci yayinda take ruggume da Adam.
gefenta ya zauna ita kuwa Ummi tea ta had'a mishi sannan ta bashi,
yana sha ne taje ta d'auko asusun duka biyu yana ganinta da asusun ya d'an kaikaice tare da cusa hannunshi a aljihun wondon Jeans d'in jikinshi zaro kud'in yayi tare da mik'a mata,
cikin kula ta amsa kana ta irgasu ganin dubu biyar ne sai ta fuskanci da kyau cikin maganar kurame tace mishi.
"Kud'in waye ne."
kurb'an tea d'in ya d'anyi bayan ya had'iye ne sai ya nuna mata kanta.
fidda numfashi tayi tare da gyara zama dan tasan in abu nashine in ta tambayeshi na waye ne sai yace mata natane haka yasa ta gane kud'in nashine cikin tsoro da tuhuna da gudun masifun zamani wanda dole in kaga d'anka da kud'i ka bincikeshi ina ya samesu a hankali tace mishi.
"Ina ka samesu? Me kayi aka baka su? Ya jiya ka samu da yawa yauma kuma gasu da yawa gashi harda su gero naga ka seyo Babana ina tsoro duk da tabbas nasan halinka amman kud'in sunyi yawa."
Allah sarki Saifuddeen ganin firgici a fuskarta ya sashi ajiye kofin tea d'in kana ya juyo suka fuskanci juna da kyau,
a hankali yasa hannu ya kamo nata hannun cikin sama mata nitsuwa ya mata bayanin komai yadda ya samu kud'in duk da body language yakeyi so Ummi tana bala'i gane body language shiyasa wasu lokutan takanyi mgna dashi cikin mutane ba mai ganewa sai Rahma,
sai kuma yanzu sun lura Hayatuddeen ma yana ganewa kad'an-kad'an ajiyan zuciya ta sauk'e lokacin daya gama yi mata bayi,
sai tayi murmushi tare da hamdala kana ta godewa Allah,
sai kuma ya fara rubutu a gefensu kamar haka.
"Yauwa my Ummi ko kefa kada kiji tsoro Saif d'inki da halal zai cigar daku ya shayar daku ya tufatar daku da guminshi."
kanshi ta shafa tare da samishi al'barka shi kuwa rubutun ya kumayi.
"Amin Amin ya rabbil izzati.
Yauwa Ummi batun gero da wake da sugar kuma,
a jik'a geron sai a markad'a ayi kamu a rink'a dama kunu kullum da yamma sannan d'auki wake mudu d'aya kullum a surfa ayi k'osai da yamma sai asa a manyan kwanuka a rink'a kaiwa bakin masallaci sadaka,
gobe zan sayi dabino a rink'a had'awa da dabinon."
Allah sarki Ummi ji tayi tamkar ta ruggumeshi sai kuma taji wasu zafafan hawayen farin ciki,
cikin raman murya tace.
"Ya Allah ya yimaka al'barka babana Allah ya k'ara maka imani da tausayi ya Allah ya bud'a maka k'ofofin samu mai al'barka in sha Allahu nida kaina zan rink'a wannan aikin har zuwa k'arshen Ramadan su Rahma da Raihana kuma suyi na gida."
Wani irin farin ciki yaji yana ratsashi sabida ganin yasa mahaifiyarshi farin ciki.
ita kuma cikin bada shawara ko ince neman izininshi a matsayinshi namiji kuma babba tace.
"Goggonku Dada ta aiko Ahmad d'azu yake cemin wai dan Allah a bata Raliyya mana taje suyi azumi acan zata d'an taimaka mata da aiki."
cikin sanin makamar girma ya rubuta mata.
"Ummi in dai kin yarda ba matsala dan na yarda da tarbiyar Goggo Dada, amman ki gayawa Bappa Ali in ya amince ai sai taje."
kai ta jinjina kana tace.
"Shi na fara gayawa kasan ai bazai hanaba yace taje ba matsala."
gyara zamanshi yayi ya kalli Rahma data zuba musu ido,
sai kuma tayi maza ta rufe ido wai ita bacci takeyi.
Jin sautin murmushin sane ya sata tashi zaune kana tace.
"Yoh tun d'azu na farka sai naga kamar hirran sirri uwa da d'an lelenta sukeyi shine nayi likimo ai, kai kuma da yake ka shahara da body language ko kallonka akeyi jikinka ke gaya maka kawai sai naga ka zuba min wannan fararen idanun naka."
dariya suka d'anyi baki d'aya kana ta zauna sukaci gaba da hira,
inda itace ta amshi kud'in ta cusasu a asusun babban goggonin milo.
Daga nan sukaci gaba da hirarsu tasu ta rayuwarsu sai shad'aya suka shiga.
Shi kam Saifuddeen saida yayi wonka sannan ya yayi al'wala kana yazo ya shafa mai tare da fesa turare wanda wannan al'adar rayuwarsa ce domin Saifuddeen mutunne mai tsananin tsabta sam baya son k'azanta ko kad'a shiyasa yakeda kenkeyani over.
Washe gari kamar kullum yayi suka tafi gombe da kafin bakwai na safema sun isa,
baccinshi ya d'anyi na awa d'aya da rabi kana daya tashi yayi walahan shi kamar yadda ya saba,
sannan ya shiga cikin kasuwa ya fara rarraba ledodinshi ana bashi kud'in na jiya yana bada wani, cikin awa hud'u da kad'an ya gama rabawa ya had'a kud'insu 60k sannan ya ware ribanshi dubu bakwai da d'ari biyu,
yaso yayi ragin d'ari bibbiyun saman to kuma sai ya shawarci Jabeer sai yake ce mishi kada ya rage dan kar ya zama yayi azarb'ab'i a kasuwar ledan tunda du du du a wata d'aya ne zaiyi sana'ar kar yayiwa baba Bella shisshigi to da wannan
shawarar ya hak'ura.
Daga shagonsu Jabeer wucewa yayi yaje ya amso omo aifa nan ya samu sa'an shiga layin masu wonki da guga sukayi ta kwasan sabulun kamaru da omon ranar ribar 2k ya samu a omon ma,
da zai koma ya saya musu naman miya da kuma fruits.
********
Rayuwa ta ja yau da gobe asarar mai rai,
kwanaki sun tafi tuni azumi ya shigi jikin al'ummar annabi
anyi dibi-dibin goma na marmari gashi har an shiga goma na wuya inji hausawa da fad'i.
Cikin izinin Allah an gama na wuyan ma yau, gobe dai na d'okin sallah za'a fara.
Iyaye da yan uwa da masu wadata dama talaka kowa na hidimar d'inkunan sallah.
Saifuddeen ya k'ara sabawa da mutane sosai ko ta ina an sanshi a kasuwar sabida dalilai uku sana'arsa ta yawoce dole yana ratsa ko wanne lungu,
sannan shi kurmane da hakane duk wanda ya had'u dashi baya manceshi kana shi mai gsky da amanane da yawan ibada to sai Allah ya sanya soyayyarsa a zuk'atan bani adam.
Uwa uba Allah ya yalwata mishi surarshi da kyau mai d'aukar hankali yana da muhibba, kima, daraja, kamala, haiba, da cikar zati,
so wadannan abubuwan sukasa ya sanu tako ina.
Alhamdulillahi kasuwarshi kuwa sai son barka dashi dama Ummi da Rahma sai godewa Allah suke suna k'arawa sabida sune kad'ai suka san kullum sai yasa dubu buyer a asusunshi, sauran na saman kuma da balance d'in machine dasu sukeyi buk'atun yau da kullum,
ribar omo kuma yaci gaba da zurawa a asusun ribar pure water.
Abota tsakanin shi da Jabeer da Hisham da Kabir kuwa sai gaba-gaba sun shak'u sosai yanzu ya saba da wani yaron shagon Alhaji ishaq Ibrahim shima yaron yana sonshi, sosai hakama wani shagon ba miskila Bello sun saba over amman shi ya girmi Saifuddeen sosai so da yake Saifuddeen ya gaya mishi sunan Abbanshi gareshi shiyasa yana kiran Saifuddeen da Bingel am d'ana kenan.
Rayuwa ta mik'a d'aura kwalin ledodi a kafad'a da Saifuddeen yake yawan yi sai ya d'an canza mishi salon tafiya
sai ya d'an karkace ka d'an mu samman ta samanshi karkacewar da bafa zaka ganeba sai in ka zuba mishi ido sosai baranma in ka sanshi kafin ya fara tallan ledan ne zaka gane hakan sosai,
wannan 'yar karkacewar sai ta zama wani abu da yake jan hankalin mutane a gareshi domin daga saman wuyanshi zakaga time to time yana tonk'oshe wuyarshi irin yadda manyan sara kuna keyi sabida nauyin rawani da k'asaita,
da yawa kuma cewa sukeyi kyanshi ne yasa yake hakan wai a zatonsu rigimace da izza,
sabida in dai ka kalli yadda yake tafiya to sai kayi zaton d'an sarkine ko matashin d'awisu domin dama a nitse yake sai tafiyarshi da tsarinshi suka koma tamkar na jarumI R.K na seris film d'in Madubalah wanda aka tab'a nunawa a Bollywood
in ka ganshi sai kayi zaton tsantsar izzace da gadara da tak'ama kasan cewarsa karma ba ko yaushe yake mgna ba sai wasu suke zaton miskilanci ne.
Yakan je gidansu Is'haq time to time musamman in yaji zafi ya matsa mishi sai ya ajiye omonshi yaje yayi wonka ya canza kayan inda zaisa na is'haq sabida bashi da shamaki a gidansu is'haq so yawan tsabtarshi yasa kawai wasu ke masa kallon tabbas rigimace tunda gashi a wuni d'aya a kasuwa sai a ganshi da kaya kala biyu,
in yaje gidansu is'haq yakan amshi wayar step mother in is'haq din su gaisa ta hanyar rubutawa juna text.
Kullum duk bayan kwana uku zai sayi wakenshi mudu shida geroma haka sannan sugar mudu d'aya da rabi sai mai k'aramin galam da dabino mudu d'aya.
Umminshi ta dama koko ta toya kosan a kai masallacin k'ofar gidansu.
Yauma kamar jiya tare da abokanshi sukayi bud'a baki.
ana idar da sallan asham suka tafi tabsir.
koda suka dawo suka ci abinci sannan suka raka Ahmad.
Yana dawowa ya sumu Ummi a tsakar gida,
bisa taburma Rahma na gefenta tana bacci yayinda take ruggume da Adam.
gefenta ya zauna ita kuwa Ummi tea ta had'a mishi sannan ta bashi,
yana sha ne taje ta d'auko asusun duka biyu yana ganinta da asusun ya d'an kaikaice tare da cusa hannunshi a aljihun wondon Jeans d'in jikinshi zaro kud'in yayi tare da mik'a mata,
cikin kula ta amsa kana ta irgasu ganin dubu biyar ne sai ta fuskanci da kyau cikin maganar kurame tace mishi.
"Kud'in waye ne."
kurb'an tea d'in ya d'anyi bayan ya had'iye ne sai ya nuna mata kanta.
fidda numfashi tayi tare da gyara zama dan tasan in abu nashine in ta tambayeshi na waye ne sai yace mata natane haka yasa ta gane kud'in nashine cikin tsoro da tuhuna da gudun masifun zamani wanda dole in kaga d'anka da kud'i ka bincikeshi ina ya samesu a hankali tace mishi.
"Ina ka samesu? Me kayi aka baka su? Ya jiya ka samu da yawa yauma kuma gasu da yawa gashi harda su gero naga ka seyo Babana ina tsoro duk da tabbas nasan halinka amman kud'in sunyi yawa."
Allah sarki Saifuddeen ganin firgici a fuskarta ya sashi ajiye kofin tea d'in kana ya juyo suka fuskanci juna da kyau,
a hankali yasa hannu ya kamo nata hannun cikin sama mata nitsuwa ya mata bayanin komai yadda ya samu kud'in duk da body language yakeyi so Ummi tana bala'i gane body language shiyasa wasu lokutan takanyi mgna dashi cikin mutane ba mai ganewa sai Rahma,
sai kuma yanzu sun lura Hayatuddeen ma yana ganewa kad'an-kad'an ajiyan zuciya ta sauk'e lokacin daya gama yi mata bayi,
sai tayi murmushi tare da hamdala kana ta godewa Allah,
sai kuma ya fara rubutu a gefensu kamar haka.
"Yauwa my Ummi ko kefa kada kiji tsoro Saif d'inki da halal zai cigar daku ya shayar daku ya tufatar daku da guminshi."
kanshi ta shafa tare da samishi al'barka shi kuwa rubutun ya kumayi.
"Amin Amin ya rabbil izzati.
Yauwa Ummi batun gero da wake da sugar kuma,
a jik'a geron sai a markad'a ayi kamu a rink'a dama kunu kullum da yamma sannan d'auki wake mudu d'aya kullum a surfa ayi k'osai da yamma sai asa a manyan kwanuka a rink'a kaiwa bakin masallaci sadaka,
gobe zan sayi dabino a rink'a had'awa da dabinon."
Allah sarki Ummi ji tayi tamkar ta ruggumeshi sai kuma taji wasu zafafan hawayen farin ciki,
cikin raman murya tace.
"Ya Allah ya yimaka al'barka babana Allah ya k'ara maka imani da tausayi ya Allah ya bud'a maka k'ofofin samu mai al'barka in sha Allahu nida kaina zan rink'a wannan aikin har zuwa k'arshen Ramadan su Rahma da Raihana kuma suyi na gida."
Wani irin farin ciki yaji yana ratsashi sabida ganin yasa mahaifiyarshi farin ciki.
ita kuma cikin bada shawara ko ince neman izininshi a matsayinshi namiji kuma babba tace.
"Goggonku Dada ta aiko Ahmad d'azu yake cemin wai dan Allah a bata Raliyya mana taje suyi azumi acan zata d'an taimaka mata da aiki."
cikin sanin makamar girma ya rubuta mata.
"Ummi in dai kin yarda ba matsala dan na yarda da tarbiyar Goggo Dada, amman ki gayawa Bappa Ali in ya amince ai sai taje."
kai ta jinjina kana tace.
"Shi na fara gayawa kasan ai bazai hanaba yace taje ba matsala."
gyara zamanshi yayi ya kalli Rahma data zuba musu ido,
sai kuma tayi maza ta rufe ido wai ita bacci takeyi.
Jin sautin murmushin sane ya sata tashi zaune kana tace.
"Yoh tun d'azu na farka sai naga kamar hirran sirri uwa da d'an lelenta sukeyi shine nayi likimo ai, kai kuma da yake ka shahara da body language ko kallonka akeyi jikinka ke gaya maka kawai sai naga ka zuba min wannan fararen idanun naka."
dariya suka d'anyi baki d'aya kana ta zauna sukaci gaba da hira,
inda itace ta amshi kud'in ta cusasu a asusun babban goggonin milo.
Daga nan sukaci gaba da hirarsu tasu ta rayuwarsu sai shad'aya suka shiga.
Shi kam Saifuddeen saida yayi wonka sannan ya yayi al'wala kana yazo ya shafa mai tare da fesa turare wanda wannan al'adar rayuwarsa ce domin Saifuddeen mutunne mai tsananin tsabta sam baya son k'azanta ko kad'a shiyasa yakeda kenkeyani over.
Washe gari kamar kullum yayi suka tafi gombe da kafin bakwai na safema sun isa,
baccinshi ya d'anyi na awa d'aya da rabi kana daya tashi yayi walahan shi kamar yadda ya saba,
sannan ya shiga cikin kasuwa ya fara rarraba ledodinshi ana bashi kud'in na jiya yana bada wani, cikin awa hud'u da kad'an ya gama rabawa ya had'a kud'insu 60k sannan ya ware ribanshi dubu bakwai da d'ari biyu,
yaso yayi ragin d'ari bibbiyun saman to kuma sai ya shawarci Jabeer sai yake ce mishi kada ya rage dan kar ya zama yayi azarb'ab'i a kasuwar ledan tunda du du du a wata d'aya ne zaiyi sana'ar kar yayiwa baba Bella shisshigi to da wannan
shawarar ya hak'ura.
Daga shagonsu Jabeer wucewa yayi yaje ya amso omo aifa nan ya samu sa'an shiga layin masu wonki da guga sukayi ta kwasan sabulun kamaru da omon ranar ribar 2k ya samu a omon ma,
da zai koma ya saya musu naman miya da kuma fruits.
********
Rayuwa ta ja yau da gobe asarar mai rai,
kwanaki sun tafi tuni azumi ya shigi jikin al'ummar annabi
anyi dibi-dibin goma na marmari gashi har an shiga goma na wuya inji hausawa da fad'i.
Cikin izinin Allah an gama na wuyan ma yau, gobe dai na d'okin sallah za'a fara.
Iyaye da yan uwa da masu wadata dama talaka kowa na hidimar d'inkunan sallah.
Saifuddeen ya k'ara sabawa da mutane sosai ko ta ina an sanshi a kasuwar sabida dalilai uku sana'arsa ta yawoce dole yana ratsa ko wanne lungu,
sannan shi kurmane da hakane duk wanda ya had'u dashi baya manceshi kana shi mai gsky da amanane da yawan ibada to sai Allah ya sanya soyayyarsa a zuk'atan bani adam.
Uwa uba Allah ya yalwata mishi surarshi da kyau mai d'aukar hankali yana da muhibba, kima, daraja, kamala, haiba, da cikar zati,
so wadannan abubuwan sukasa ya sanu tako ina.
Alhamdulillahi kasuwarshi kuwa sai son barka dashi dama Ummi da Rahma sai godewa Allah suke suna k'arawa sabida sune kad'ai suka san kullum sai yasa dubu buyer a asusunshi, sauran na saman kuma da balance d'in machine dasu sukeyi buk'atun yau da kullum,
ribar omo kuma yaci gaba da zurawa a asusun ribar pure water.
Abota tsakanin shi da Jabeer da Hisham da Kabir kuwa sai gaba-gaba sun shak'u sosai yanzu ya saba da wani yaron shagon Alhaji ishaq Ibrahim shima yaron yana sonshi, sosai hakama wani shagon ba miskila Bello sun saba over amman shi ya girmi Saifuddeen sosai so da yake Saifuddeen ya gaya mishi sunan Abbanshi gareshi shiyasa yana kiran Saifuddeen da Bingel am d'ana kenan.
Rayuwa ta mik'a d'aura kwalin ledodi a kafad'a da Saifuddeen yake yawan yi sai ya d'an canza mishi salon tafiya
sai ya d'an karkace ka d'an mu samman ta samanshi karkacewar da bafa zaka ganeba sai in ka zuba mishi ido sosai baranma in ka sanshi kafin ya fara tallan ledan ne zaka gane hakan sosai,
wannan 'yar karkacewar sai ta zama wani abu da yake jan hankalin mutane a gareshi domin daga saman wuyanshi zakaga time to time yana tonk'oshe wuyarshi irin yadda manyan sara kuna keyi sabida nauyin rawani da k'asaita,
da yawa kuma cewa sukeyi kyanshi ne yasa yake hakan wai a zatonsu rigimace da izza,
sabida in dai ka kalli yadda yake tafiya to sai kayi zaton d'an sarkine ko matashin d'awisu domin dama a nitse yake sai tafiyarshi da tsarinshi suka koma tamkar na jarumI R.K na seris film d'in Madubalah wanda aka tab'a nunawa a Bollywood
in ka ganshi sai kayi zaton tsantsar izzace da gadara da tak'ama kasan cewarsa karma ba ko yaushe yake mgna ba sai wasu suke zaton miskilanci ne.
Yakan je gidansu Is'haq time to time musamman in yaji zafi ya matsa mishi sai ya ajiye omonshi yaje yayi wonka ya canza kayan inda zaisa na is'haq sabida bashi da shamaki a gidansu is'haq so yawan tsabtarshi yasa kawai wasu ke masa kallon tabbas rigimace tunda gashi a wuni d'aya a kasuwa sai a ganshi da kaya kala biyu,
in yaje gidansu is'haq yakan amshi wayar step mother in is'haq din su gaisa ta hanyar rubutawa juna text.
Kullum duk bayan kwana uku zai sayi wakenshi mudu shida geroma haka sannan sugar mudu d'aya da rabi sai mai k'aramin galam da dabino mudu d'aya.
Umminshi ta dama koko ta toya kosan a kai masallacin k'ofar gidansu.