← Book details Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 67 OF 116

Sashe 67

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hayatuddeen ne ya ciccibi 'yar ma dai-dai ciyar jakarsu,
sannan yabi bayan Ahmad da d'aya daka cikin workers nasu da zai nuna musu d'akin da yake can saman bene na hud'u kasan cewar lifta ne cikin k'ank'anin lokaci suka isa,
suna isa ya bud'e musu k'ofar tare da juyawa ya fita,
suna shiga,
Hayatuddeen ya ajiye jakar hannunshi tare da zuwa gaban TV,
kunna tibin yayi sannan ya dawo ya zauna bisa lumtsuma-lumtsuman kujerun da sukayiwa parlour k'awanya,
ido ya lumshe sannan ya bud'esu yabi bayan Ahmad da kallo,
shi ko Ahmad bedroom ya wuce kai tsaye cikin bathroom ya nufa,
wonka yayi mai rai da lfy sannan yayi al'wala kana ya d'aura towel d'in daya samu a ninke sabo dal cikin ledsnshi ys farkeshi, komai na wurin sabo.
yana fitowa ya koma parlour ya d'auko jakar kayan nasu yazo ya dawo bedroom d'in k'ananan kaya ya saka fitowa yayi ya koma parlour gefen Hayatuddeen ya zauna tare da cewa.
"Je kayi wonka kazo muje mu samu abinda zamu ci,
mu kuma sayi sim card na k'asar tasu."
da sauran Hayatuddeen ya mik'e tare da cewa.
"To." shi kuwa Ahmad ido ya zuba mishi ganin yadda yake cilla kayanshi tsakiyar parlour,
baki ya bud'e ganin ya tsallake wondenshi a inda ya cireshi,
kuma ko a jikinshi ya nufi bedroom,
kai tsaye bathroom ya shiga bayan yayi wonka yayi al'wala sannan ya fito,
gaba d'aya kayan cikin jakar saida ya fiddasu ya zubesu bisa gado sannan ya saka wani wondo 3 quarter pink color sai rigarshi mai yankekken hannu white Color,
sosai kayan sukayi mishi kyau.

Shi kuwa Ahmad a fili yace.
"Wato haka Raliya ke fama da rigimar Autan Ummi."
dai-dai lokacin kuma ya fito tare da cewa.
"Na fito ya Ahmad muyi sallan muje muci abinci yunwa nakeyi."
cikin had'e fuska Ahmad yace.
"To wa zai tattara maka kayan daka watsar d'in?."
kai ya d'an longob'ar tare da cewa.
"Ni ban iya tattarewa ba ya Ahmad."
tsaki Ahmad yaja tare da cewa.
"Zaka ma koya ai, dan nima ban iyaba."
sai ya kuma fuskanci al'k'ibila ya tada kabbara ganin haka shima Hayatuddeen yabi bayanshi,
bayan sun idar da sallolin nasu ne suka sauk'a reception sukayi tambayar ta ina Restaurant yake nan aka kwatanta musu sannan,
suka nufi wurin suna isa sashin. Restaurant ɗin.
Mathuramakrishna viswanathun.
Hayatuddeen ya isa gaban teburin da yaga an rubuta Africa food, gefe d'aya ya juya inda yaga ansa Nigerians food is ready,
sai kuma ya juyo jin Ahmad yana ce mishi,
"Ni ka amso min feesh roll,."
to yace sannan ya saya musu duk abinda suke buk'ata sannan suka juyo,
suna dawowa reception d'in suka gayawa ma'aikatan wurin cewa suna son sayan SIM card,
kud'in sukace su kawo zasu sayar musu dan suma suna saidawa,
nan suka basu kud'in layukan da kuma kati sannan suka musu register tare da karb'an woyoyin suka saka musu layukan sannan suka saka musu katin,
ganin tuni lokaci d'aya layin ya hau yasa suka haura d'akinsu.

Suna isa suka zauna a parlour sukaci suka sha,
ganin ko kad'an Hayatuddeen bai damu da kanshi dake watseba yasa Ahmad mik'ewa ya tattarusu ya shiga bedroom dasu,
nan kuma yayi arba da kayansu daya wancakalar
hannunshi d'aya yasa ya tokare k'ugunshi kana yasa d'aya ya dafe goshinsa tare da cewa.
"Wayyo ni Ahmad jikan Ahmad naga ta kaina da aka had'ani da wannan sangartaccen Ummin."
dole ya kimtsa komai.

Shi kuwa Hayatuddeen a parlour ana ya konta tuni bacci ya fara d'ibanshi.
Ahmad da ya gama tattara abinda ya watsanne ya dawo parlour ya tada Hayatuddeen tare da cewa.
"Ka tashi mu koma asibitin mana."
cikin gengyad'i yace.
"Ya Ahmad dare yayi sosai fa ka bari da asuba muje."
da wannan shawarar ya koma bedroom ya konta.
Dan akwai gajiyar tafiya tare dasu.

Washe gari suna idar da sallan asuba,
suka fito suka kama hanyar da zata sadasu da asibitin,
tafiya kad'an suka shiga cikin asibitin.

Daga bakin harabar wurin,
suka fara tambaya da tambayar suka samu suka isa har office d'in Dr Acash prasat dan dashi suke tambaya,
suna shiga cikin wurin suka hango Adnan zaune bakin mashigar inda suka kwana,
da sauri suka iso gunshi,
Ahmad ne ya fara bashi hannu,
bayan sun gaisa ne,
yace musu ana mishi wonka ne,
jin haka yasa Ahmad ya bashi SIM card d'in da suka saya mishi da key d'in d'akinsu ya kwatanta mishi yace.
"Kaje kayi wonka ka samu ka canza kaya ka kuma d'an ci abinci kafin ka dawo, wata k'il Dr yazo."
haka kuwa akayi ya amsa ya tafi,
su kuma suka zauna koda aka gama kimtsashi.
Hayatuddeen ne yaje ya samo mishi abinda zaici,
daga nan sukayi ta hira dashi har zuwa lokacin da Ya Adnan ya dawo,
nan sukayi ta zaman jira sai bayan azahar Dr Acash yazo,
haka sukayi ta bin layin ranar amman ina ranar basu samu damar ganinshi ba,

the next day ma haka sukayi ta bin layi, har kusa k'arfe biyar na yammansu sannan suka samu damar shiga.

Suna shigar da Saifuddeen Dr Adnan yabi bayansu,
d'aya daga cikin nurses da suka shigar da Saifuddeen d'inne ya nunawa Dr Adnan wurin zama,
bisa wasu kujeru guda biyu dake gaban wani babban table,
wanda d'aya sashin shi kuma kujera d'aya ce,
wacce Doctor Acash prasat ke zaune,
kekyawan ba indiye ne,
fayel d'in da Saifuddeen da nurse ta bashi ne ya fara bubbud'ewa yana duddubawa,
yayinda Dr Adnan kuwa ya zauna gabanshi,
sauran nurses d'in kuwa suke ta kiciniyar kontar da Saifuddeen bisa wani d'an gado dake gefen doctor.

Suna gamawa suka koma gefe suka zauna,

Da sauri Dr Adnan ya d'ago kanshi cikin mmki yake kallon Dr Acash da yake mishi mgna cikin yaren hausa.
"Tun shekaran jiya Dr Aliyu yace min kun iso,
kuyi hak'uri abin ne da yawa."
cikin nitsuwa Dr Adnan yace.
"Ba matsala, d'azu mukayi mgna da Dr Aliyu ma."
juyawa yayi ya kalli Saifuddeen dake konce a rigingine,
sai ya kuma meda dubanshi ga fayel d'in,
kana ya bud'e poldernsu ya fara 'yan wasu rubuce-rubuce kusan tsawon 4 minutes sai ya kuma ture takardun sannan ya jawo system dake gabanshi still rubuce-rubucen yayi, sannan ya d'ago kanshi ya kalli Dr Adnan cikin bagwariyar hausarsa da zamanshi da Dr Aliyu ne yasa ya iya yace.
"Forko dai yanzu za'ayi mishi gwajin, X-ray CT scan MRI scanning wanda ko wanne d'aya N95,000. ne
sai kuma Surgery da ya kamata ayishi kan lokaci d'an yanzuma lokaci ya d'an fara ja,."
cikin gamsuwa da bayaninshi Dr Adnan yace.
"Surgery d'in kuwa zai kai nawane?."
kai ya d'an rusunar sannan ya d'anyi dube-dube a system d'in sannan ya d'ago kanshi ya kalleshi kana yace.
"N2.5 million."
A hankali Dr Adnan yace.
"Ba matsala a fara aiki."
mik'ewa yayi ya nufi gaban gadon da Saifuddeen yake a hankali yasa hannunshi ya fara jan 'yan yatsun Saifuddeen amman shiru bai kulaba a hankali ya fara bin k'afafunshi yana d'an lallatsawa still Saifuddeen baya ji bare ya bud'e idonshi,
sai yaci gaba da tattab'ashi tare da juyawa ya kalli Dr Adnan dake tsaye bayanshi cikin kula yace.
"Naga kurmane shi ko?."
kai ya gyad'a mishi da sauri,
cikin meda hankalin shi kan Saifuddeen yace.
"In ba matsala in kunada hali musa doctor kunne a cikin aikinshi mana."
jim kad'an Dr Adnan yayi kana ya d'an matso doctor Acash d'in tare da cewa.
"Dr kanaga zai worke ne?."
da sauri ya jujjuya mishi kai tare da cewa.
"Wannan ai sai Doctord ɗin kunnen ne zasu bamu amsar nan in sun dubashi,
sai dai muna zaton zai worke tunda ba haifarshi akayi da kuramtarba ko?."
da sauri Dr Adnan ya gyad'a mishi kai tare da mishi d'an k'arin bayanin yadda ya samu larurar kuramta,
kamar yadda yayiwa Dr Aliyu a Abuja.
dawowa sukayi suka zauna bisa kujerun da suka tashi nan suka fara musanyan basira da shawara a matsayinsu na Doctors,
sosai Doctor Adnan ya k'ara samun haske a lamarin sashin aikinshi dan zama da kwararran Dr da yayi na awa biyu.
da yawa suna kwarafin cewa shi Dr Acash in an aka shigar da mutun ba'a fitowa da wuri,
shi kuwa k'a'idar aikinshi ne ya binciki marasa lfy da kyau a nitse ya kuma samu cikikken bayani daga bakin mara lfyar ko iyayenshi.
Shiyasa yake dad'ewa da mutane,
shiyasa kuma mutane ke son ya dubasu,
anan take ya kira wani doctor da yake kula da sashin kunne.
Ba jimawa ya shigo nan sukayi 'yan dube-dubensu,
daga bisani nan take aka fara aikin gudanar da gwoje-gwajensu.
Saida suka gama duba komai sannan aka fitar dasu,
aka kaisu room d'in da za'a kwantar dashi zuwa gobe in sun duba sakamakon awun nasu.
nan ya bawa Dr Adnan number shi cewa gobe in sunzo ya shaida mishi.

D'akin babba ne mai kyau gadaje biyu ne a cikin d'akin sai kujeru guda biyu ko wanne gado da kujera d'aya,
bayan sun gama komai nan suka zauna su dukan su uku Hayatuddeen yana gefen Saifuddeen,
Ahmad kuwa yana tsaye gaban Dr Adnan da yake musu bayanin yadda sukayi da Dr da kuma gwoje-gwojen da akayi da kud'ad'ensu.
ganin lokacin salla yayi ne sukayi al'wala sannan suka tafi masallaci, sukayi salla magrib nan suka d'an jira lokacin isha yayi, hankalin konce sukayi salla dan sun san akwai masu kula da Saifuddeen.

Bayan sun idar sun koma ne suka sameshi kwance amman an d'an d'aga kan gadon in ka ganshi zakace a zaune yake irin ya d'an jinginane,
da sauri Hayatuddeen ya zauna gefenshi tare da cewa.
"Sannu Hamma Saifuddeen ya jiki?."
kanshi ya jinjina alamun da sauk'i sannan ya kuma mishi mgna cikin body language yake tambayarshi ya labarin Ummi.
da sauri Ahmad yace.
"Ummi tana lfy tace a gaidaka."
murmushi yayi cikin jin dad'i sannan ya kalli Hayatuddeen dake cewa.
"Bari in kira Raliya video call sai ku gaisa da Ummin."
matsowa yayi kusa dashi ya zauna gab dashi kana ya kira Raliya sannan ya kaikace woyar tashi ya matso da kanshi jikin Hamman nashi duk suka fuskanci wayar.
Chapter 67 · 0% Book details