Sashe 66
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sassanyan ajiyan zuciya yaja a hankali,
ido ya lumshe tare da bud'esu ya juya ya kalli gabas da yamma kudu da arewa, a fili yace.
"Gari banban Allah d'aya."
Ahmad ne ya juyo ya kalleshi tare da cewa.
"Ko wanne wuri da irin kalar ni'imar da Allah yake musu."
da sauri suka juyo suka kalli ya Adnan dake ce musu.
"Ni zan shiga ciki zamu isa wurin Dr Acash prasat zan kama mana layi,
duk dai Dr Aliyu ya mana hanyar ganinshi a watannan to dole sai munbi layi.
So kai Ahmad ga can taxi ku shiga sai ku duba mana hotel nan kusa mu samu masauk'i."
cikin gamsuwa da hakan Ahmad yace.
"To ba matsala bari mu d'auki kayan mu."
Shi kuwa Hayatuddeen da sauri yabi bayan nurses da suka fito da Saifuddeen dake kan gado,
yana isa ya bawa Saifuddeen hannu tare da cewa.
"Zamuje nan kusa, ya Adnan zai shiga ciki da kai."
kai ya gyad'a mishi alamar sai sun dawo hakama Ahmad yazo ya salla meshi sannan Dr Adnan yabi bayansu, suka nufi cikin ainihin asibitin,
tafiya kad'an sukayi suka ratsa cikin wani babban corridor mai girma,
tafiya yar kad'an suka isa bakin wata babbar k'ofa,
suna bud'ewa wasu nurses d'in suka karb'eshi,
kana wad'an nan suka juya sukayi baya,
su kuma wannan da suka k'arbeshi sai suka canza mishi gado suka d'auranshi kan irin k'ananun gadajen tura marasa lfyn,
sannan da sauri Dr Adnan kuwa ya mik'a d'aya daga cikinsu wata takarda,
bayan ya karb'a ya duba sai ya juyo ya kalli d'aya nurse dake tura gadon yayi mishi mgna cikin indiyancin.
Sai kuma suka canza hanya suka fuskanci wani ratsetsen gini mai azabar kyau amman shi ba benaye bane.
suna isa harabar wannan wurin wasu nurses d'in suka karb'eshi kana suka basu wannan takardar da takeda tambarin National Hospital Abuja,
a k'asa kuma ga sa hannun Dr Aliyu,
can gefe kuma ga shaidar transfer zuwansu wannan asibitin da.
shi dai Dr Adnan binsu yake a baya.
A hankali suka bud'e wata k'ofa mai girma suka shiga Dr Adnan na biye dasu a baya,
yana sa k'afarsa cikin Reception d'in nasu yayi wani irin ajiyan zuciya dan wani azabebben sanyi da ya cika wurin,
gaba d'aya reception d'in cike yake mak'il da mutane duk da girmanshi sai dai duk ana zaune bisa tsari ba hayaniya,
shi kuwa Saifuddeen kanshi ya d'an juya ya kalli gefen hagunshi da damanshi,
jerin gadaje ne a gefen hagunshi mutane na konce a Kai,
d'aya gefen kuwa kekunan weelchair ne a jere wasu na zazzaune a ciki.
gefen gadajen aka tura gadon da Saifuddeen ke kwance,
sannan nurse d'in ya yafito Adnan kana suka nufi gaban inda nurses ke zaune suna bada kati dama masu bud'e folda
suna isa suka mik'awa d'aya daga cikin matan dake wurin takardar,
mgna suka d'anyi cikin yarensu da Adnan baya ji ya dai ji suna kiran Nigeria,
sai kuma nurse d'in da aka kira da Divia ta juyo ta kalli Adnan tare da mishi tambayar ina fayel nasu na asibitin da aka turosu nan cikin turanci.
Da sauri ya mik'a mata fayel d'in amsa tayi sannan ta had'a da takardar da wannan d'in ya bata,
juyawa tayi ta d'auko polder sannan ta bud'e wanna fayel d'in kana ta d'auki biro ta fara rubutu a saman poldern sai kuma ta fara bud'a fayel d'in nan ta d'anyi 'yan rubuce-rubuce sannan ta mik'awa Adnan hand card data zaro cikin polder d'in,
amsa yayi ya duba kasan cewarshi Dr ras ya gane rubutunsu na doctors da yafi kama da jagwalgwale,
kai ya jinjina ganin bata saurari tambayarshi sunan mara lfy da shekaru ba duk ta samesu cikin fayel d'in da suka zo dashi.
kai ta sunkuyar kana ta matso kusa da system d'in dake gabanta a hankali ta fara sassarafashi,
daga bisani ta d'ago kai tace mishi yaje ya zauna za'a nemeshi.
Gefen da Saifuddeen yake yaje,
nan ya samu yana bacci dan ya samu irin sanyin da jikinshi ke buk'ata, kasan cewar masu larurar cutar lakar jiki suna da yawan jin zafi, shiyasa suƙe matuƙar so da jin daɗin wurin dake wadace da tsabta da sanyi,
fita yayi daga cikin wurin hanyar da suka bi sukazo ita yabi d'an suna wucewa yaga wani d'an k'aramin masallaci a hanyarsu,
yana isa wurin yayi Al'wala kana yayi sallan azahar da la'asar da niyar k'asaru.
yana idarwa ya mik'e da sauri ya koma.
Still har yanzu yana bacci hakan ne yasa ya koma gefe ya zauna,
yana kallon yadda aketa shiga da fita.
In an d'an jima wata nurse ta fito ta d'ebi wasu polder ta shiga dasu,
hakama wata bisa dukkan alamu likitocin guda uku ne suke duba marasa lfyan,
a hankali ya fara kallon rubutun dake saman k'ofofin office d'in na forko ansa Dr Biru Sahastara Dubbe,
sai na tsakiyar da akasa Dr Acash prasat,
sai na k'arshen da aka saka Dr Abdul Malik Khan.
kai ya meda ya jingina da kujera dan ganin dare ya rufa,
kuma da yawa sunata fita.
Da sauri ya d'ago kanshi jin motsin bud'e k'ofa ta tsakiyar nan,
ido ya zubawa saman aljihun rigar mutumin inda aka rubuta Dr Biru S D,
ga kuma nurses guda biyu suna biye dashi a baya yayinda wani kuma yake rufe k'ofar office d'in.
Bai gama nazartan mutuminba ya kuma hango an bud'e d'aya k'ofar ido ya zubawa saman al'jihun rigarshi inda aka rubuta Dr Malik Khan.
tafiya yakeyi cikin nitsuwa kanshi d'auke da hular tab'a kaji hadis ɗin nan,
bisa dukkan alamu nurses dake binshi a baya ma,
musulmaine,
yana isowa tsakiyar Reception d'in sai ya d'aga hannunshi duka biyu ya fiskanci mutanen dake gefen damanshi yace.
"Assalamu laikum."
kad'an daga ciki da suka kasance musulmai ne suka amsa da.
"Wa alaikassalam."
sai ya kuma d'an tsayawa tare da kallon marasa lafiyan kana yace.
"Lah ba'as d'uhuru in sha Allah."
sai ya kuma juya gefen hagunshi in da ya kuma yi musu sallama,
kasan cewar Adnan ne kad'ai musulmi a layin shiyasa shi kad'ai ne ya amsa da.
"Wa alaikassalam."
cikin kula ya kalli Adnan tare da mishi murmishi ya tambashi shi d'an wacce k'asar ce. Cikin jin dad'i Dr Adnan yace.
"Nigeria."
sunanshi ya tambayeshi ya gaya mishi sanna ya kuma tambayarshi su sabbin zuwa ne ko,
dan duk wad'an nan sauran sun kai kwana huɗu zuwa biyar suna bin layi,
kuma ba'a fara k'arb'an sabbin zuwa ba.
mik'ewa Dr Adnan yayi ya matso kusa dashi cikin nitsuwa da iya sarrafa harsher ya mishi bayanin da zai fahimta sosai a matsayinsu na doctors kuma kusan duk abu d'aya suka karanta,
ya k'ara da mishi bayanin doctor daya turosu da kuma sani Dr Acash prasat.
Kai ya jinjina cikin gamsuwa sannan ya tamb'ayeshi ina mara lfyan,
da sauran ya nufi gadon Saifuddeen binshi yayi a baya cikin k'are mishi kallo yake tambayarshi wai Saifuddeen ba d'an Nigeria bane ko.
cikin sakin fuska Dr Adnan yace mishi cikekken d'an Nigeria ne.
kai ya rusunar ya shafa sumar kan Saifuddeen tare da tambayar Dr Adnan wai to shi wacce k'abilane.
sosai Dr Adnan yayi murmushi dan ya fahimci Dr malik irin mutannane masu raha da sauk'in kai jin suna k'abilar Saifuddeen Fulani sai yacewa Dr Adnan,
to k'abilar tanada alak'a da indiyawa ko wai sabida Africa ba irin masu kamarsu?
dariya sukayi baki d'aya sannan yacewa Dr Adnan ai tun d'azu Dr Acash ya bar cikin asibitin nan shi da zuwa kuma sai gobe da rana.
sai ya kuma k'ara da cewa. Tunda yau kukazo baku samu an dubashi bama ba,
ni zan d'an taimaka muku zan had'aku da Divia zata barku ku kwana a nan sashin,
sannan zan bar wancan nurse d'in ya gyara mishi jikinshi da mishi abinda ya dace."
cikin jin dad'i Dr Adnan ya mishi godiya.
haka kuwa akayi,
nan Divia ta nuna musu wurin da zasu fake sannan nurse d'in nan namijin nan ya gyarawa Saifuddeen jikinshi, sannan ya taimaka mishi yayi al'wala kana yayi niyar salla ya fara biyan sallolin da bai samu yayiba.
Shi kuwa Ya Adnan fita yayi ya tambayi inda zai samu abinda zai saya musu suci.
Wani k'aton Restaurant dake cikin asibitin wanda ana yin kalan abincin ko wanne k'asa,
Snacks and drinks ya samo musu sannan ya koma ya tallafawa Saifuddeen ya d'anci sannan shima yaci kana ya koma gefe ya konta bisa kujerun silver dake wurin.
Su Ahmad kuwa suna shiga taxi d'in suka cewa drivern ya kaisu hotel mafi kusa da asibitin,
to yace musu kana ya ja motar suka fita daga harabar adibitin tafiya kad'an sukayi sukaga ya ratsa cikin wani tamfatsetsen hotel mai azabar kyau da tsari na zamani,
suna fitowa Ahmad ya zubawa sunan hotel d'in idanu.
Hyatt regency Delhi, ido ya zubawa benayen da sukasha k'awanya da abubawan alatu na duniya,
da sauri Ahmad ya koma cikin motar kana ya kalli Driver tare da cemishi.
da ganin wannan hotel d'in zaiyi tsada, to in dai da akwai wani k'arami a nan kusa ya ka kaisu.
kai driver ya jujjuya mishi tare da mishi bayanin cewa babu wani hotel nan kusa in banda wannan sai wani dake gabanshi kad'an kuma duk tsadarsu d'aya,
ya k'ara da ce musu gwara kuma su kama wannan d'in zasu huta da biyan kud'in texi na zirga-zirgan zuwansu da dawowa,
ya shaida musu ko an bashi gado baza'a barsu su zauna dashi ba, dan akwai masu kula dasu.
jin haka yasa dole suka fito,
Direct reception d'in hotel d'in suka nufa,
suna zuwa Ahmad ya k'arb'a musu d'aki d'aya tare da biyan kud'in sati biyu duk da yawan kud'in ya bashi tsoro to amman ya zaiyi.
Key aka basu bayan an rubuta sunayensu da time and date na zuwansu cikin littafin ajiyan shige da ficen mutane.
ido ya lumshe tare da bud'esu ya juya ya kalli gabas da yamma kudu da arewa, a fili yace.
"Gari banban Allah d'aya."
Ahmad ne ya juyo ya kalleshi tare da cewa.
"Ko wanne wuri da irin kalar ni'imar da Allah yake musu."
da sauri suka juyo suka kalli ya Adnan dake ce musu.
"Ni zan shiga ciki zamu isa wurin Dr Acash prasat zan kama mana layi,
duk dai Dr Aliyu ya mana hanyar ganinshi a watannan to dole sai munbi layi.
So kai Ahmad ga can taxi ku shiga sai ku duba mana hotel nan kusa mu samu masauk'i."
cikin gamsuwa da hakan Ahmad yace.
"To ba matsala bari mu d'auki kayan mu."
Shi kuwa Hayatuddeen da sauri yabi bayan nurses da suka fito da Saifuddeen dake kan gado,
yana isa ya bawa Saifuddeen hannu tare da cewa.
"Zamuje nan kusa, ya Adnan zai shiga ciki da kai."
kai ya gyad'a mishi alamar sai sun dawo hakama Ahmad yazo ya salla meshi sannan Dr Adnan yabi bayansu, suka nufi cikin ainihin asibitin,
tafiya kad'an sukayi suka ratsa cikin wani babban corridor mai girma,
tafiya yar kad'an suka isa bakin wata babbar k'ofa,
suna bud'ewa wasu nurses d'in suka karb'eshi,
kana wad'an nan suka juya sukayi baya,
su kuma wannan da suka k'arbeshi sai suka canza mishi gado suka d'auranshi kan irin k'ananun gadajen tura marasa lfyn,
sannan da sauri Dr Adnan kuwa ya mik'a d'aya daga cikinsu wata takarda,
bayan ya karb'a ya duba sai ya juyo ya kalli d'aya nurse dake tura gadon yayi mishi mgna cikin indiyancin.
Sai kuma suka canza hanya suka fuskanci wani ratsetsen gini mai azabar kyau amman shi ba benaye bane.
suna isa harabar wannan wurin wasu nurses d'in suka karb'eshi kana suka basu wannan takardar da takeda tambarin National Hospital Abuja,
a k'asa kuma ga sa hannun Dr Aliyu,
can gefe kuma ga shaidar transfer zuwansu wannan asibitin da.
shi dai Dr Adnan binsu yake a baya.
A hankali suka bud'e wata k'ofa mai girma suka shiga Dr Adnan na biye dasu a baya,
yana sa k'afarsa cikin Reception d'in nasu yayi wani irin ajiyan zuciya dan wani azabebben sanyi da ya cika wurin,
gaba d'aya reception d'in cike yake mak'il da mutane duk da girmanshi sai dai duk ana zaune bisa tsari ba hayaniya,
shi kuwa Saifuddeen kanshi ya d'an juya ya kalli gefen hagunshi da damanshi,
jerin gadaje ne a gefen hagunshi mutane na konce a Kai,
d'aya gefen kuwa kekunan weelchair ne a jere wasu na zazzaune a ciki.
gefen gadajen aka tura gadon da Saifuddeen ke kwance,
sannan nurse d'in ya yafito Adnan kana suka nufi gaban inda nurses ke zaune suna bada kati dama masu bud'e folda
suna isa suka mik'awa d'aya daga cikin matan dake wurin takardar,
mgna suka d'anyi cikin yarensu da Adnan baya ji ya dai ji suna kiran Nigeria,
sai kuma nurse d'in da aka kira da Divia ta juyo ta kalli Adnan tare da mishi tambayar ina fayel nasu na asibitin da aka turosu nan cikin turanci.
Da sauri ya mik'a mata fayel d'in amsa tayi sannan ta had'a da takardar da wannan d'in ya bata,
juyawa tayi ta d'auko polder sannan ta bud'e wanna fayel d'in kana ta d'auki biro ta fara rubutu a saman poldern sai kuma ta fara bud'a fayel d'in nan ta d'anyi 'yan rubuce-rubuce sannan ta mik'awa Adnan hand card data zaro cikin polder d'in,
amsa yayi ya duba kasan cewarshi Dr ras ya gane rubutunsu na doctors da yafi kama da jagwalgwale,
kai ya jinjina ganin bata saurari tambayarshi sunan mara lfy da shekaru ba duk ta samesu cikin fayel d'in da suka zo dashi.
kai ta sunkuyar kana ta matso kusa da system d'in dake gabanta a hankali ta fara sassarafashi,
daga bisani ta d'ago kai tace mishi yaje ya zauna za'a nemeshi.
Gefen da Saifuddeen yake yaje,
nan ya samu yana bacci dan ya samu irin sanyin da jikinshi ke buk'ata, kasan cewar masu larurar cutar lakar jiki suna da yawan jin zafi, shiyasa suƙe matuƙar so da jin daɗin wurin dake wadace da tsabta da sanyi,
fita yayi daga cikin wurin hanyar da suka bi sukazo ita yabi d'an suna wucewa yaga wani d'an k'aramin masallaci a hanyarsu,
yana isa wurin yayi Al'wala kana yayi sallan azahar da la'asar da niyar k'asaru.
yana idarwa ya mik'e da sauri ya koma.
Still har yanzu yana bacci hakan ne yasa ya koma gefe ya zauna,
yana kallon yadda aketa shiga da fita.
In an d'an jima wata nurse ta fito ta d'ebi wasu polder ta shiga dasu,
hakama wata bisa dukkan alamu likitocin guda uku ne suke duba marasa lfyan,
a hankali ya fara kallon rubutun dake saman k'ofofin office d'in na forko ansa Dr Biru Sahastara Dubbe,
sai na tsakiyar da akasa Dr Acash prasat,
sai na k'arshen da aka saka Dr Abdul Malik Khan.
kai ya meda ya jingina da kujera dan ganin dare ya rufa,
kuma da yawa sunata fita.
Da sauri ya d'ago kanshi jin motsin bud'e k'ofa ta tsakiyar nan,
ido ya zubawa saman aljihun rigar mutumin inda aka rubuta Dr Biru S D,
ga kuma nurses guda biyu suna biye dashi a baya yayinda wani kuma yake rufe k'ofar office d'in.
Bai gama nazartan mutuminba ya kuma hango an bud'e d'aya k'ofar ido ya zubawa saman al'jihun rigarshi inda aka rubuta Dr Malik Khan.
tafiya yakeyi cikin nitsuwa kanshi d'auke da hular tab'a kaji hadis ɗin nan,
bisa dukkan alamu nurses dake binshi a baya ma,
musulmaine,
yana isowa tsakiyar Reception d'in sai ya d'aga hannunshi duka biyu ya fiskanci mutanen dake gefen damanshi yace.
"Assalamu laikum."
kad'an daga ciki da suka kasance musulmai ne suka amsa da.
"Wa alaikassalam."
sai ya kuma d'an tsayawa tare da kallon marasa lafiyan kana yace.
"Lah ba'as d'uhuru in sha Allah."
sai ya kuma juya gefen hagunshi in da ya kuma yi musu sallama,
kasan cewar Adnan ne kad'ai musulmi a layin shiyasa shi kad'ai ne ya amsa da.
"Wa alaikassalam."
cikin kula ya kalli Adnan tare da mishi murmishi ya tambashi shi d'an wacce k'asar ce. Cikin jin dad'i Dr Adnan yace.
"Nigeria."
sunanshi ya tambayeshi ya gaya mishi sanna ya kuma tambayarshi su sabbin zuwa ne ko,
dan duk wad'an nan sauran sun kai kwana huɗu zuwa biyar suna bin layi,
kuma ba'a fara k'arb'an sabbin zuwa ba.
mik'ewa Dr Adnan yayi ya matso kusa dashi cikin nitsuwa da iya sarrafa harsher ya mishi bayanin da zai fahimta sosai a matsayinsu na doctors kuma kusan duk abu d'aya suka karanta,
ya k'ara da mishi bayanin doctor daya turosu da kuma sani Dr Acash prasat.
Kai ya jinjina cikin gamsuwa sannan ya tamb'ayeshi ina mara lfyan,
da sauran ya nufi gadon Saifuddeen binshi yayi a baya cikin k'are mishi kallo yake tambayarshi wai Saifuddeen ba d'an Nigeria bane ko.
cikin sakin fuska Dr Adnan yace mishi cikekken d'an Nigeria ne.
kai ya rusunar ya shafa sumar kan Saifuddeen tare da tambayar Dr Adnan wai to shi wacce k'abilane.
sosai Dr Adnan yayi murmushi dan ya fahimci Dr malik irin mutannane masu raha da sauk'in kai jin suna k'abilar Saifuddeen Fulani sai yacewa Dr Adnan,
to k'abilar tanada alak'a da indiyawa ko wai sabida Africa ba irin masu kamarsu?
dariya sukayi baki d'aya sannan yacewa Dr Adnan ai tun d'azu Dr Acash ya bar cikin asibitin nan shi da zuwa kuma sai gobe da rana.
sai ya kuma k'ara da cewa. Tunda yau kukazo baku samu an dubashi bama ba,
ni zan d'an taimaka muku zan had'aku da Divia zata barku ku kwana a nan sashin,
sannan zan bar wancan nurse d'in ya gyara mishi jikinshi da mishi abinda ya dace."
cikin jin dad'i Dr Adnan ya mishi godiya.
haka kuwa akayi,
nan Divia ta nuna musu wurin da zasu fake sannan nurse d'in nan namijin nan ya gyarawa Saifuddeen jikinshi, sannan ya taimaka mishi yayi al'wala kana yayi niyar salla ya fara biyan sallolin da bai samu yayiba.
Shi kuwa Ya Adnan fita yayi ya tambayi inda zai samu abinda zai saya musu suci.
Wani k'aton Restaurant dake cikin asibitin wanda ana yin kalan abincin ko wanne k'asa,
Snacks and drinks ya samo musu sannan ya koma ya tallafawa Saifuddeen ya d'anci sannan shima yaci kana ya koma gefe ya konta bisa kujerun silver dake wurin.
Su Ahmad kuwa suna shiga taxi d'in suka cewa drivern ya kaisu hotel mafi kusa da asibitin,
to yace musu kana ya ja motar suka fita daga harabar adibitin tafiya kad'an sukayi sukaga ya ratsa cikin wani tamfatsetsen hotel mai azabar kyau da tsari na zamani,
suna fitowa Ahmad ya zubawa sunan hotel d'in idanu.
Hyatt regency Delhi, ido ya zubawa benayen da sukasha k'awanya da abubawan alatu na duniya,
da sauri Ahmad ya koma cikin motar kana ya kalli Driver tare da cemishi.
da ganin wannan hotel d'in zaiyi tsada, to in dai da akwai wani k'arami a nan kusa ya ka kaisu.
kai driver ya jujjuya mishi tare da mishi bayanin cewa babu wani hotel nan kusa in banda wannan sai wani dake gabanshi kad'an kuma duk tsadarsu d'aya,
ya k'ara da ce musu gwara kuma su kama wannan d'in zasu huta da biyan kud'in texi na zirga-zirgan zuwansu da dawowa,
ya shaida musu ko an bashi gado baza'a barsu su zauna dashi ba, dan akwai masu kula dasu.
jin haka yasa dole suka fito,
Direct reception d'in hotel d'in suka nufa,
suna zuwa Ahmad ya k'arb'a musu d'aki d'aya tare da biyan kud'in sati biyu duk da yawan kud'in ya bashi tsoro to amman ya zaiyi.
Key aka basu bayan an rubuta sunayensu da time and date na zuwansu cikin littafin ajiyan shige da ficen mutane.