← Book details Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 109 OF 116

Sashe 109

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da hantsi misalin k'arfe 11:15 Am Zaleeha ta shigo d'akin Mama wanda lokacin kenan ta fito daga d'akinta da shirin zata wuce wurin aikita, jin
muryar Yayarta Maryam da Anty Aisha da Ruda yasa ta nufi d'akin a hankali ta shiga bakinta d'auke da sallama.
sai kuma tayi turus a baki k'ofar ta tanya cikin tsananin kad'uwa da firgita,
ido ta zubawa Maryam dake tsakiyar akwatunan ta bubbud'esu gaba d'aya tana nunawa Any Aisha kayan,
Yayinda Mama kuwa da yayarta Ruda suke kan gado fuskokin nan nasu tamkar suyi ruwan jini kuma tuni sun barbaɗe ƙofar falon Mama da maganin da Ruda ta kawo wanda aka basu tabbacin in dai Zaleeha ta tsallakashi tofa bazata lamunci zaɓin mahaifin nataba zata tashi hankalin kowa har sai an janye batun auren.
cikin sanyin murya Anty Aisha take cewa.
"Allah ya sanya al'khairi yasa gidan zamanta kenan iya rai da mutuwa."
Maryam ce tace Amin Amin.
sai kuma suka juyo suka kalli Ruda dake cewa.
"Tir da addu'arki Aisha bakinki ya sari guntun kashi,
kifa kalli wannan zuk'ek'iyar budurwa ki fasalta zamanta da gurgu kuma kurma musaki mara amfani kice Allah yasa gidan zaman tane.
Ke kuma Maryam da yake baki da hankalin da kishin yar uwarki harda wani cewa Amin."
ita kam Zaleeha tamkar an dasa tane a wurin ta kasa tantance abinda kunnuwanta ke jiye mata daga bakin Maryam dake cewa.
"Addu'a ita ta dace da Zaleeha tunda dai wannan abun yin Allah ne,
ko ana so ko ba'a so in Allah yayi ita matar Saifuddeen ne dole taje gidanshi,
kuma ke Mama kin san halin Baba malam me amfanin bad'i babu rai,
yak'in da babu nasara ai gwara yin mubaya'a du du dufa auren nan saura sati d'aya ne rak."
Da sauri Zaleeha tasa tafin hannunta ta dafe k'ahon zuciyarta dake gab da tarwatsewa,
idanunta ta rumtse da azabar k'arfi kanta ta fara jujjuyawa tare da zamewa ta durk'usa gaban Mamansu murya a hargitse tace.
"Bana sonshi, bazan zauna da shiba, wlh mutuwa zanyi in aka had'ani dashi please Mama kiyi wani abu a kai."
Maryam ce ta d'an kalleta a tausashe dan tasan irin abinda Zaleeha keji a ranta tunda itama a dole aka had'ata da Ya Aminu amman gashi yanzu da tayi biyayya tabi umarnin iyayenta tana ganin ribar haka,
duk da zafin zuciya irin na ya Aminu zama yake kamar bawa a gareta,
baya son duk wani abinda zai sata zubda hawaye.
shiyasa a hankali tace.
"Zaleeha kiji tsoron Allah kiyi biyayya ga mahaifinmu zakiga ribar hakan kada ki bari rud'in duniya ya Kaiki ya baroki.
Ku dena yakice Saifuddeen dan nakasarsa dan babu wanda yasan k'arshensa, kuma in baka mutuba to ba'a k'are maka halitta ba,
shimafa bada larurarnan aka haifeshi ba, kaso 95 cikin 100 ba haihuwarsu ake da nakasaba a duniya suke samu. Kaso 5 ne na cikin 100 ake haifarsu da nakasa,
because muma bamu da yak'inin a haka zamu k'are rayuwarmu."
Cikin tsawa da masifa Mama tace.
"Rufe min baki hegiya mara zuciya,
mai mugun fata mu nan in sha Allah lfy lau zamu k'are rayuwarmu.
Kuma wlh wlh muddin ina raye Zaleeha bazata zauna da wannan gurgunba.
Dan ke kinada macecciyar zuciya sun tankwaraki kin zauna a dole to banda Zaleeha."
Cikin sanyi Maryam tace.
"Kiyi hak'uri Mama ki gafarceni in furucina ya sosa miki zuciya."
ita kuwa Zaleeha mik'ewa tayi ganin sunk'i su sarara bare su saurareta,
ficewa tayi daga gidan a guje.

A Cikin gidan kuwa, Anty Aisha ce ta kalli yayun nata cikin kafiya da fad'in gsky tacewa Mama.
"Da hankalinki da tunaninki kike biyewa zugar wacce kin san batayi imani da Allah da manzonsa ba, bare ta yarda da k'addara mai kyau ko sab'aninta."
A zafafe Ruda tace.
"Ke Rebeka ni kike gayawa haka?."
cikin tsuke fuska da tsawa tace.
"An gaya mikin! K'arya nayi ne, imanin gareki tunda har yanzu baki samu tsarkin zuciyaba, kina kafura,
mara lissafi zata zauna tana bin zugarki,
lallai ke yar uwata ce kuma yayata Amman baki da hurimin kirana da Rebeka call me Aisha in bazaki iya ki bari."
A zafafe tace.
"don't call me Rebeka again."
Sai kuma ta juya ta kalli Maryam tace.
"Maryam tashi mu tafi, ni dai ina bayan Baba Malam daga yau kuma zamu fara shirye-shiryen auren nan."
A hankali Maryam ta maida akwatunan duk wurin zamansu,
sannan ta mik'e tabi bayan Anty Shatu kamar yadda suke kiranta kenan...

Mama kuwa da kafurar Yayarta Ruda,
nan sukaci gaba da tubka da warwara,
suna tubke yadda auren Zaleeha da Abdussalam, kana suna warware auren Saifuddeen.

Ita kuwa Zaleeha tana fita kai tsaye (Jonapwd)  ta nufa tuk'in takeyi tamkar wacce zata bar garin.
tana shiga harabar wurin tayi parking, cikin sauri ta fito gaba d'aya ida nunta dishi-dishi suke mata,
kai tsaye office d'in Ishaq ta kutsa kanta sam bata iya amsawa mutanen nata gaisuwar da suke mata.
shi kuwa Ishaq tun tana babban parlour yajiyo mgnar Sani na mata sannu da zuwa so koda aka turo k'ofar office nashi aka shiga yasan itane.
Tana ganinshi kawai sai rauni ya rufe masifarta dan iya tsawon zamanta da ishaq a matsayin yayanta Ahmad take kallonshi ishaq yanada mutunci a ida nunta gashi last time ta surfa musu rashin ɗa'a kuma daga nan yake fushi da ita,
a hankali taja kujerar dake fuskantar wacce yake zaune a kai ta zauna.
sunkuyowa tayi ta kifa kanta bisa glass table dake tsakiyarsu kawai sai ta saki wani irin mawuyacin kuka mai cike da rauni da tarin k'uncin rayuwa.
cikin tsananin mmki Ishaq ya zubawa saitin inda yakejin kukan idanu tamkar yana ganinta.
sai kuma yayi shiru kamar baya wurin yana jin sautin kukanta na ratsa kunnuwanshi.
Kusan tsawon 10 minutes tana kuka,
bai kulata ba, ita kuma bata bariba,
har 20 minutes har ta zarta rabin awa tana kukan bil hak'k'i da gsky.
daga jin kukan kasan daga cikin zuciyarta yake fitowa kukane mai tattare da k'una da tsoro,
sosai Ishaq ya fara jin tausayinta na kamashi ai ko ba komai ita macece kuma mai rauni.
cikin sanyin sauti yace.
"Ya isa, ya isa haka Zaleeha kada ki cutar da kanki."
jin haka sai kukanta ya k'aru cikin kukan murya a raunace tace.
"Malam Ishaq bana sonshi, wlh bana sonshi, na tsaneshi, inada wanda nakeso wanda ya bada ranshi da lfyarshi domin kare mutun cina pleaseeee Ya Ishaq kace mishi ya janye batun aure a tsaka ninmu, wlh muddin akayi auren nan cikin mu biyu dole d'aya zai rasu."
Sosai ya nitsu yana jin kala manta sai ya kuma ji alamun tazo tana durk'ushe a gabanshi a hankali tace.
"Dan Allah Ya Ishaq ka zame min Garkuwa na mana a karo d'aya dai a rayuwa ta,
dana rok'eka abu dan Allah dan annabi kaji tausayi na mana ka rabani dashi kar in rasa raina please ya Ishaq kada ka bari ayi min auren dole."
Sai ta kuma kife kanta bisa d'aya kujerar taci gaba da kuka.
Sosai raunin ishaq ya halarto kan zuciyarshi,
me zai hana ya taimaketa, to amman bari yaji meyasa bata son Saifuddeen, a hankali yace.
"To waye kike son?." murya a raunane tace.
"Ban sanshi ba?."
fuska cike da mmki yace.
"Ina yake to me sunanshi?."
A hankali tace.
"Duk ban saniba sau d'aya muka tab'a had'uwa shiyasa a gidanmu ake cewa wai ba mutun bane al'janine."
Da sauri yace.
"Yes al'janine mana nima haka zance, tunda shi gaibune."
kuka ta kuma sakewa, sai kuwa ta d'ago kanta jin yana cewa.
"To meyasa baki son Saifuddeen?. "
Rashin sani yafi dare duhu shiyasa Zaleeha tacewa Ishaq.
"Nakasasshe nefa shi gurgune kurma ne ta yaya zan aureshi da lfyata gurgunefa ananfa kuke cemin irinsu basa aure."
da sauri ta mik'e tsaye jiki na rawa ta koma gefe dan jin yadda ishaq ya buga table dake gabanshi tare da buga mata tsawa.
"To sai me!? Shi nakasasshe ba mutun bane!? Ko shi nakasasshe baida ikon auran lafiyayyiyar mace!? To wlh Zaleeha kinyi ganganci wannan furucin naki, ni babu taimakonki da zanyi in sha Allah sai Saifuddeen ya aureki ko zaki mutu ne.
Get out of my office!."
Ya k'areshe mgnar da k'arfi tare da mik'ewa tsaye.
wanda saida mutanen cikin babban parlour nan suka jiyosu.
Ita kuwa Zaleeha cikin tafasan zuciya ta juya ta fita dan yanayinshi ya bata tsoro.

Daga nan gidansu Rashida ta nufa,
nan ta tasa Rashida a gaba tana kuka.
Murmushi Rashida tayi tare da cewa.
"Hmmmm Zaleeha kenan to ni mai zance miki,
kin dai san bazan baki goyon bayan ki bijirewa iyayeki ba, in dai k'awancenmu na gsky ne,
sannan da kiketa mai-maita shi nakasasshe ne ke kinada tabbacin a haka zaki k'arene.
Zaleeha kifa farga ki dawo nitsuwarki kin gani ko wlh wlh dani Saifuddeen yace yana so na rantse miki da zatin Allah da hannu bibbiyu zan amshi soyayyarsa,
Zaleeha inafa gaya miki kada kiyiwa kanki sakiyar da babu ruwa, kibi umarnin iyayemu ki samu rabauta duniya da k'iyama in zaki farga ki farga Ki daina wanna yarintar."
Cikin tsananin takaici ta ture Rashida da tasa hannunta tana share mata hawayenta a hatsale tace.
"Sai yau na gane asalinki Rashida, ke farin cikima kikeyi da wannan abun har dariya kikeyi ko?."
Da sauri Rashida tace.
"Tabbas farin ciki nakeyi abinda baki saniba,
ko jiya muna tare da abokan ango, d'azuma na dawo daga can anguwar tasu federal law cos, layin Sabana hospital, wurin shagon Bash wani tela ne.
Can suka kai kayayyakin d'inkinmu na biki naki da namu na k'awaye kuma komai yayi kyau,
anjima kuma zasu zo batun shagulgulan da za'ayi."
Cikin mmki da tarin takaici Zaleeha tace.
"Shegiya yar iska a ina kika sansu?."
Dariya Rashida tayi tare da cewa.
"A wayar wani ɗan kawuna Jabeer naga hoton Saifuddeen sai yake cemin abokinshi,
harma an kai lefe.
to nan nake ce mishi ai mune k'awayen amarya,
kinga daga nan komai yazo da sauk'i mu yanzu shirin bikin mukeyi babu kama hannun yaro.
nice nan na kaiwa telan kayanki yadda zai d'inka komai dai-dai dake."
bazata fa juri jin tatsuniyar Rashida da ɗan kawunta Jabeer da sauran abokan Saifuddeen ba don haka ta zari car key d'inta ta bar gidan.
Chapter 109 · 0% Book details