← Book details Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 116

Sashe 36

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Su Ahmad da Mudassir kuwa Karatu yayi nisa hakama Salisu,
tuni Saminu kuwa sune masu gama wannan shekaran.

Yayinda Saifuddeen kuwa sune 'yan level 100.

Bayan shekara d'aya, kasuwa taci gaba da gudana komai yana tafiya dai-dai da tsari na taimakon talakawa da marasa k'arfi.
Kullum jarinsu habaka yakeyi da d'an riban da suke bi da kuma kud'in hayansu,
inda kayan masarufi yake mallakin jarin Saifuddeen ne halak d'inshi ba surkin kud'in gadonsu.

Yau kusan wata d'aya kenan Saifuddeen da Bappa Ali sunata kan harhad'a cinikinsu na tsawon shekarar suna ware ribar su da hauhawar jarinsu.
Koda suka gama had'e komai sai suka fara ware hak'insu Bello da Warisu sunka biyasu biya mai daraja a matsayinsu na masu kula da kasuwancin,
daga nan kuma suka ware adadin zakkar da zasu fidda na shekarar bayan sun gama ware zakkar tasu,
sun bawa wad'anda shariya ta misalta da a basu sai kuma suka fara shirye-shiryen sari tako wanne sashi inda Bappa Ali zai sarar musu kayayyakin abinci a kasuwannin k'auyuka kamar yadda suka saba,
shiko Saifuddeen zai yi musu sarin kayan masarufi wanda wasu direct daga company yake musu sarin shiyasa suke samun damar sakin farashinsu da rahusa,
dole zuwa yanxu sunfi k'arfin shago d'aya hakan yasa suka nemi k'arin hayan wani k'aton shagon dake kusa da nasu, ba b'ata lokaci aka basu da yake na Alhaji Kabiru ne,
cikin kwana uku aka had'a shagunan sannan aka barsu da k'ofofi biyu.

Ya Adnan kuwa tuni ya isar da batun soyayyarshi da Adda Rahma ga manya tuni mgna ta kankama dan iyayensu Adnan sun san nagartar Rahma tunda a gabansu ta girma shiyasa basuyi wata rigimaba,
tuni antsaida ranar aurensu bayan sallan layya da mak'o d'aya.

Saminu kuwa ya gama karatunshi har ya samu damar tafiya bautan k'asa mgnar sosayyarshi da Raihana kuma tanata kankama har iyaye sun shiga,
an bari a kan cewa sai ya gama bautan k'asanshi ya fara aiki sannan ayi musu auren.

Mudassir da Ahmad da Ishaq ma duk sun kusa gamawa.

Hayatuddeen kuwa shima yana shekararshi ta k'arshe a primary school,
Faruq kuwa yana primary 3 Adam na primary 2,
Raliyya kuma tana SS 1.

Abba yaron Bappa Ali shima ya girma har an yayeshi.

Rayuwa dai taci gaba da gudana cikin nasara da ci gaba.

Anyi bikin Ya Adnan da Rahma lfy an watse lfy,
ta tare a gidanshi dake cikin Gombe wanda yake cikin jerin gida jan ma'akatan lfy na Medical Center Gombe,
wannan had'i yayi matuk'ar yiwa Ahmad da Mudassir dad'i dan dama a gidan Ya Adnan d'in suke sukewa kansu girki a cewarsu yanzu sun huta sun samu mai musu girki.

Bayan bikin da mako ukune Ya Adnan yaje har dukku da batun yana son a basu Faruq da Adam a cewarsa zai rik'esu,
to Ummi dai tak'i amincewa ganin ya tasa gabata da magiya ne yasata ce mishi Saifuddeen ne ya hana ba itaba kuma shi yana can gomben,
jin haka yasa Ya Adnan tura mishi text cewar,
yana son ganinshi gobe, yana ganin text d'in ya maida mishi amsa da to Allah ya kaimu.
daga nan Adnan ya sallami Ummi ya tafi gidansu a nan ya wuni sai da yamma ya koma.

Washe gari da safe Salisu da Saifuddeen ko breakfast basu tsaya yiba suka wuce cikin gombe,
kasan cewar basu da lectures da wuri sai zuwa k'arfe biyu so kai tsaye gidan ya Adnan suka nufa,
a harabar gidan Salisu yayi parking,
sannan suka nufi bakin mashigar ainihin cikin gidan,
a bakin k'ofa suka tsaya door bell suka d'an danna,
jim kad'an aka bud'e k'ofar ganin Ahmad ya bud'e musu k'ofar ne yasa su yin murmushi shima murmushin yayi tare da bawa Salisu hannu tafawa sukayi cikin salon gaisuwa ta abokai da suka shak'u da juna,
sai ya kuma juyo ya d'aga hannu alamun zai tafa hannu da Saifuddeen da k'arfi irin yadda yayi da Salisu,
shi kuwa Saifuddeen ganin haka yayi saurin janye hannunshi tare da rab'awa gefenshi ya wuce yayi cikin parlour,
cikin dariyar shek'iyanci Ahmad ya kalli Salisu da shima dariyar yakeyi, sai ya kuma juyo ya kalli Saifuddeen da tuni ya isa tsakar parlour suna ruggume da juna shida Mudassir, dariya ya kumayi tare da cewa.
"Hege mai d'an karen son jiki da tsoron wahala."
cikin dariya Salisu yace.
"Yaseen gskyanshi nima d'in ai bani kuma yarda ka kima min wannan hannun naka, kalli yadda hannuna yayi jazir hege mai suffar samudawa."
duka ya kaiwa Salisu,
da sauri ya kauce tare da cewa.
"Wayyo Ya Adnan kaga Ahmad ko."
da sauri Rahma ta yunk'ura zata tashi ta fita jiyo muryar Salisu tasan sarai da Saifuddeen suka zo.
Shi kuwa Ya Adnan da sauri ya jawota jikinshi tare da cewa.
"Ina zakije?."
fuska ta d'an marairaice tare da cewa.
"Parlour zanje kaji su Saifuddeen sun zo."
ido ya d'an kashe mata tare da cewa.
"Barsu suyi ta sabgoginsu muma muyi namu in mun gama ma fita."
cikin sanyi tace.
"Allah ko nayi missing Saifuddeen tunda akayi bikin nanfa bai zoba."
mik'ewa yayi tare da kamota ya tsayar da ita sannan yace.
"To muje muyi wonka."
a dole ta bishi suka shiga bathroom.

Su Ahmad kuwa a falo hira sukayi tayi na yaushe gamo,
daga nan suka shiga kitchen suda kansu suka fara kiciniyar had'a breakfast nasu.
to Ahmad da Mudassir su sun iya sun saba,
Salisu da Saifuddeen kuwa basu iyaba,
shiyasa suka kame suka zauna gefe,
Ahmad na fire dankali shi kuwa Mudassir yana kiciniyar tafasa musu ruwan tea.

Bayan kamar 35 minutes Rahma da Adnan suka fito a tare a parlour ta tsaya tana kasa kunne dan jiyo ta inda hayaniyarsu take,
jinsu a kitchen ne yasa tayi sauri ta nufi kitchen d'in tana shiga duk suka juyo murmushi tayi musu ganin duk suna murmushi,
sai kuma Saifuddeen yayi saurin tasowa ya iso gabanta murmushi ya kuma yi tare da mata alamun,
"Iye-iye kinyi kyau fa."
kunnenshi ta d'an rik'e tare da d'an matsewa da d'an k'arfi, d'an tsalle yayi tare da yarfa hannu,
Ahmad kuwa sai tsalle yakeyi yana dariya tare da cewa.
"Yauwa Adda Rahma matse da kyau."
Mudassir kuwa fuska ya kwab'e tare da cewa.
"Please Adda Rahma sakar mishi kunne kinsan baya son wahala."
Salisu ne yayi dariya tare da cewa.
"Kaji banza to waye ke son wahala,
kuma a yar wannan matsarne wahalar."
shi kuwa Saifuddeen hannunshi d'aya yasa ya kamo d'aya kunnenshi cikin body language ya mata alamun ya tuba.
ganin haka yasa ta sakar mishi kunne tare da cewa.
"Zaka sake yin sati uku har kusan hud'u baka zoba kuma kana cikin lfy."
Kai ya jujjuya mata yana mai shafa kunenshin,
daga nan sukaci gaba da hira tana mai tayasu aikin nanda nan suka gama girkin suka jera komai a dinning table,
daga nan suka zauna suka karya,
Saifuddeen ne ya fara cire hannu sai kuma Rahma sannan Salisu nandai duk sukaci sukayi nak,
suna gamawa Ahmad ya tattare wurin sannan ya nufi d'akinsu dan yana son watsa ruwa,
Salisu ne yabi bayanshi sai kuma Mudassir.
Chapter 36 · 0% Book details