Sashe 63
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna shiga su kuma suka fita dan sun gama mishi shirin baccinsa,
Yana ganin Dr Adnan yayi murmushi tare da lumshe ido kana ya bud'esu ya kalli Dr Aliyu dake zaune bisa welchair d'inshi,
a hankali ya mik'o mishi hannu sukayi musabaha,
cikin kula Dr Aliyu yace.
"Ya jikin?." lips enshi ya motsa alamun da sauk'i kana ya jinjina kai,
shi kuwa Dr Aliyu cikin tausayawa yace.
"In sha Allah in an fiddaka zuwa India nanda wani d'an lokacin zaka fara tashi zaune da kanka."
da sauri Dr Adnan yace.
"Allah yasa."
Amin Dr Aliyu yace kana ya duddubashi sannan suka d'an k'ara bashi k'arfin guiwa da sama mishi nutsuwa sannan suka fita,
a bakin harabar wurin Dr Aliyu da Dr Adnan suka had'u da Nurse d'innan Amina,
da sauri ta iso inda suke, cikin shigarsu ta nurses wanda sunyi mata cib a jikinta sai d'an k'aramin hijabi,
hannunta na cikin haljihun gefe da gefen rigardata da iya karta guiwa, rusunawa ta d'anyi tare da cewa.
"Sir barka da dare."
"Barka dai Amina Usman Jada."
murmushi tayi dan yadda ya kira cikekken sunanta, gaida Dr Adnan tayi kana tace.
"Sir bari inje in bashi maganinshi, zan wuce gida."
jim ya d'anyi kana yace.
"To ba matsala amman dan Allah kiyi sammakon zuwa, kinga na damk'a amanar wannan aikin a hannunki, dan naga bafulatanine d'an uwanki."
cikin girmamawa tace,
"In sha Allah ba matsala zan taho da wuri".
daga nan sukayi sallama ita tayi ciki su sukayi woje.
A hankali ta tura k'ofar ta shiga bakinta d'auke da sallama,
kasan cewar idonshi biyu yana rubutawa Ummi text ne yasa yaga shigowarta, baibi ta kantaba yaci gaba da sarrafa woyar tashi,
ita kuwa gefenshi ta tsaya,
tana harhad'a alluran da zatayi mishi,
bayan ta gama ne ta d'an matsoshi, tare da d'an zuba mishi idanu,
kallonshi takeyi tamkar tauraro,
gashin girarshi ta zubawa idanu wanda suke tamkar an zanasu da gazal sunyi lub lub dasu kana hancinshi zuwat har baki lips inshi jazir sai shek'ek'i sukeyi,
ido ta lumshe tare da cewa.
"Matarka taji dad'i koda ranta a bace yake in taga kekyawan fuskarnan taka farin cike zai kauda bak'in cikin."
lip's enshi ya d'an tsotsa ta ciki dan yana kallon motsin bakinta ta cikin fuskar woyarshi. So ya gane duk abinda tace.
ita kuwa yatsunshi ta zurawa ido yadda yake sassarafa wayar tamkar shi ya halicceta,
lips enshi ta kuma kalla kana tace.
"Wannan labban da ganinsu zasuyi taushi, ji yadda suke shek'i."
still bai kulata ba, ganin ta shagala wurin kallonshi,
ido ya lumshe yana tuno Zaleeha a ranshi sai yake jin inama itace kusa dashi,
a hankali taja numfashi kana tasa hannu bisa fuskarshi ta karkad'a mishi yatsunta,
d'ago lumsasshun idanunshi yayi ya d'an kalleta.
ganin ta nuna mishi allurane yasashi,
rumtse ido kana ya d'an mirgina tare da gyara zaman damtsen hannunshi na dama ya bata damar mishi allurar,
a hankali ta zira mishi allurar kana ta fara tura ruwan,
ido ya kuma rumtsewa kana yana sunkuyar da yatsun hannunshi har suna bada sautin k'aras-k'aras.
a hankali ta kalleshi cikin tausayawa tace.
"Sannu."
bai nuna mata ya ganeba dan ya lura bata san yana gane mgnar mutaneba in yana ganin bakinsu,
maganin ta babballa kana ta mik'a mishi.
Hannun dama yasa ya amsa kana ya afasu a baki tare da amsar robar ruwan da ta mik'o mishi,
sannan ya had'iyesu, bayan ta gama mishi komaine ta k'ara mishi gudun AC ganin tunda ta mishi allurar yake d'an had'a zufa,
gaban gadon ta dawo ta gyara mushi mayafin sannan ta kalleshi tare da cewa.
"Zan tafi gida, dare yayi, dan kai gobe da sassafe zan dawo Allah ya baka lfy, da masu kula da kai zasu ku kwana tare."
A ranshi yace.
"Amin ngd." a zahiri kuma bai kuma kulataba,
itako fita tayi,
shi kuwa text yayiwa Rahma da Raliyya da Hayatuddeen kana yayi addu'a ya rufe ido dan allurar ta fara sashi gyangyad'i.
Rahma kam dama da Adnan zai taho cewa yayi ta koma Side d'in Mamanshi dan yana soron kartayi ta kuka,
kuma Alhamdulillahi dake uwar mijintan na sonta suna kuma tausaya mata suna kula da ita shiyasa ta d'an sake bare yanzu da taga text d'in k'anin nata yana ce mata.
"Adda, yanzu Ya Adnan yazo, mukasha hira, yace min wai kince sai dai ku taho tare,
ni kuwa gani garau na samu sauk'i itama Ummi da Hayatudden zasu dawo, an bar gida ba manya ga Ahmad ma yazo nan, duk sun tare a kaina sai kace basu da aikin yi."
murmushi tayi tare da cewa.
"Zan zo kam in su Ummi sun dawo, in banzo na gankaba to wa zai zo ya ganka?."
murmushi yayi kana yace mata.
"Budurwata mana zatazo."
dariya tayi cikin samun nitsuwa tace.
"Iye to me sunanta surkar tawa."
kai ya rausayar tare da cewa.
"Sai na dawo zan gaya miki." daga nanne ya rufe wayar tashi.
Shiko Dr Adnan tare suka tafi da Dr Aliyu a can ya kwana.
Ummi kuwa tunda suka koma ta kasa samun sukuni duk da ta fawwala Allah lamarinta,
Amman ta kasa cin abinci,
Hayatuddeen kuwa ya d'an sake sabida yadda Ya Rabi'u, da Ya ishaq da Ahmad suka rink'a yi mishi nasiha da bashi k'arfin guiwa da nuna mishi yarda da k'addara.
Aunty Mami kuwa tausayin Ummi ya hanata sukuni sabida da ka ganta kasan tana cikin damuwa da fargaba,
shiyasa data gama shirin baccinta ta kuma soya mata gwai da biredi kana ta had'a mata tea ta nufi d'akin da suka sauk'i Ummin inda suke sauk'e Mamansu Ishaq in tazo.
bisa sallaya ta sameta tana rik'e da carbi,
gefenta ta zauna tare da tank'oshe k'afafunta, ganin har yanzu Ummi hawaye take zubdawa cikin sanyi Aunty Mamin tace.
"Kiyi hak'uri Ummi ki dena kuka dan Allah kiyi ta mishi Addu'a, insha Allah zai samu lfy."
cikin sanyin murya tace,
"Mami ya zanyi in banyi kukaba, me zanyi da hawayen nawa, ce minfa sukayi Saifuddeen na bazai sake tsayawa da k'afafunshi ba."
cikin tausasawa tace.
"A a fa Ummi ana kyautata zaton wata rana zai iya mik'ewa."
kai ta jinjina kana tace,
"Kayya ba dai boye min sukeyi ba, hakama sukayi min lokacin Nuruddeen da Abbansu."
Sai kuma ta share hawayenta cikin tarin damuwa taci gaba da cewa.
"Ina rasa nitsuwata da konciyar hankali na in naga Saifuddeen yana cikin wani hali,
ina jin tausayinshi a raina ina rasa samun nitsuwata gaba d'aya a kanshi,
ina tausayawa Saifuddeen in na tuna lfy lau na haifeshi, sai kuma abubuwa suketa biyu bayan rayuwarshi."
cikin tausayawa Aunty Mami tace.
"Ummi. Wayene Nuruddeen d'in da Abbansu?."
a hankali Ummi ta nisa kana cikin sanyi ta fara bata lbrin asalinsu Saifuddeen dama yadda ya samu larurar rashin ji...
Cikin tsananin kuka da tausayawa Aunty Mami tayi saki wani nannauyan ajiyan zuciya.
Numfashi ta fudda a hankali sannan ta jingina da gadon tana mai sheshesk'an kuka har saida Ummi ta dawo tana bata hak'uri,
cikin rauni ta share hawayenta tare da cewa.
"In sha Allah daga yanzu duk sanda nayi salla zansa Saifuddeen cikin addu'o'i na ya bani tausayi tun yana yaro k'arami yayita fuskantar k'alubalen rayuwa."
sai ta kuma gyara zamanta tare da cewa.
"Dan Allah Ummi na rok'eki ki daina yawan kuka,
kiyi ta mishi addu'a in sha Allah Saifuddeen bazai tab'eba."
Sassanyan ajiyan zuciya Ummi ta sauk'e tare da cewa.
"In sha zan daina yawan kukan zanyi ta mishi addu'a."
cikin jin dad'i ta mik'a mata kofin tea d'in,
ba musu ta karb'a tare da cewa.
"Ngd Allah ya miki al'barka."
Amin Amin tace sannan ta mik'e ta fita dan bata wuri.
Washe gari kuwa tuni Doctor Aliyu ya harhad'a dukkan bayanan cutar Saifuddeen ya turawa Dr Acash prasat wanda yake aiki a wani babban asibiti dake New Delhi India,
Ahmad kuwa E passport d'in Saifuddeen da Hayatuddeen da nashi ya tattara ya nufi Airport tun da sanyin safiya ya fara musu cuku-cukun samun visa,
A nan ya samu Adnan ya taho dan tare zasu tafi dole yayi musu jagora a matsayinshi na likita da yaso ace da Dr Aliyu zasuje to shi aiyuka sun mishi yawa,
sai da suka gama duk abinda ya dace na zirganiyar samun tafiyar nasu cikin sauri cikin sa'a kuwa suka samu jirgin da zai tashi jibi nan zuwa India direct New Delhi Indira Gandhi Enternational Airport, saida suka gama komai na tafiyar sannan suka baro airport d'in.
Ummi kuwa da Ishaq da Saifuddeen Ya Rabi'u ne ya kaisu Asibitin.
Suna isa Dr Batulu tayi musu jagora har d'akin da Saifuddeen d'in yake,
sosai Ummi taji dad'in samunshi cikin nitsuwa yana rik'e da wayarshi fuskarshi d'auke da murmushi,
da sauri ta isa bakin gadon kujerar dake kusa dashi taja ta zauna,
ishaq kuwa yana isa bakin gadon ya rik'e k'arfen gadon ya tsaya,
Hayatudddeen kuwa gefen shi ya tsaya kusa da Umminsu,
da sauri ya ajiye wayarshin tare da juyawa inda suke jin Ummi na shafa kanshi,
murmushin ya kumayi tare d'ago hannunshi ya shafa kan Hayatuddeen yayinda Ummi kuwa ke shafa kanshi,
sai ya kuma mik'o hannunshi d'aya ya kamo hannun ishaq.
Ya Rabi'u ne ya d'anyi murmushi tare da cewa.
"Masha Allah. Alhamdulillahi jiki da sauk'i ko?."
kai ya jinjina alamum eh.
Dr Batulu kuwa sai binsu da idanu takeyi cikin shawar shak'uwar dake tsakaninsu.
Cikin kula Ummi tace.
"Sannu ko babana ya jikin?."
wayarshi ya d'auka da sauri ya rubuta mata.
"Alhamdulillahi jiki da sauk'i."
cikin jin dad'i duk sukace.
"Allah ya k'aro mana sauk'i."
Amin Amin ya amsa a saman lab'b'ansa.
Yana ganin Dr Adnan yayi murmushi tare da lumshe ido kana ya bud'esu ya kalli Dr Aliyu dake zaune bisa welchair d'inshi,
a hankali ya mik'o mishi hannu sukayi musabaha,
cikin kula Dr Aliyu yace.
"Ya jikin?." lips enshi ya motsa alamun da sauk'i kana ya jinjina kai,
shi kuwa Dr Aliyu cikin tausayawa yace.
"In sha Allah in an fiddaka zuwa India nanda wani d'an lokacin zaka fara tashi zaune da kanka."
da sauri Dr Adnan yace.
"Allah yasa."
Amin Dr Aliyu yace kana ya duddubashi sannan suka d'an k'ara bashi k'arfin guiwa da sama mishi nutsuwa sannan suka fita,
a bakin harabar wurin Dr Aliyu da Dr Adnan suka had'u da Nurse d'innan Amina,
da sauri ta iso inda suke, cikin shigarsu ta nurses wanda sunyi mata cib a jikinta sai d'an k'aramin hijabi,
hannunta na cikin haljihun gefe da gefen rigardata da iya karta guiwa, rusunawa ta d'anyi tare da cewa.
"Sir barka da dare."
"Barka dai Amina Usman Jada."
murmushi tayi dan yadda ya kira cikekken sunanta, gaida Dr Adnan tayi kana tace.
"Sir bari inje in bashi maganinshi, zan wuce gida."
jim ya d'anyi kana yace.
"To ba matsala amman dan Allah kiyi sammakon zuwa, kinga na damk'a amanar wannan aikin a hannunki, dan naga bafulatanine d'an uwanki."
cikin girmamawa tace,
"In sha Allah ba matsala zan taho da wuri".
daga nan sukayi sallama ita tayi ciki su sukayi woje.
A hankali ta tura k'ofar ta shiga bakinta d'auke da sallama,
kasan cewar idonshi biyu yana rubutawa Ummi text ne yasa yaga shigowarta, baibi ta kantaba yaci gaba da sarrafa woyar tashi,
ita kuwa gefenshi ta tsaya,
tana harhad'a alluran da zatayi mishi,
bayan ta gama ne ta d'an matsoshi, tare da d'an zuba mishi idanu,
kallonshi takeyi tamkar tauraro,
gashin girarshi ta zubawa idanu wanda suke tamkar an zanasu da gazal sunyi lub lub dasu kana hancinshi zuwat har baki lips inshi jazir sai shek'ek'i sukeyi,
ido ta lumshe tare da cewa.
"Matarka taji dad'i koda ranta a bace yake in taga kekyawan fuskarnan taka farin cike zai kauda bak'in cikin."
lip's enshi ya d'an tsotsa ta ciki dan yana kallon motsin bakinta ta cikin fuskar woyarshi. So ya gane duk abinda tace.
ita kuwa yatsunshi ta zurawa ido yadda yake sassarafa wayar tamkar shi ya halicceta,
lips enshi ta kuma kalla kana tace.
"Wannan labban da ganinsu zasuyi taushi, ji yadda suke shek'i."
still bai kulata ba, ganin ta shagala wurin kallonshi,
ido ya lumshe yana tuno Zaleeha a ranshi sai yake jin inama itace kusa dashi,
a hankali taja numfashi kana tasa hannu bisa fuskarshi ta karkad'a mishi yatsunta,
d'ago lumsasshun idanunshi yayi ya d'an kalleta.
ganin ta nuna mishi allurane yasashi,
rumtse ido kana ya d'an mirgina tare da gyara zaman damtsen hannunshi na dama ya bata damar mishi allurar,
a hankali ta zira mishi allurar kana ta fara tura ruwan,
ido ya kuma rumtsewa kana yana sunkuyar da yatsun hannunshi har suna bada sautin k'aras-k'aras.
a hankali ta kalleshi cikin tausayawa tace.
"Sannu."
bai nuna mata ya ganeba dan ya lura bata san yana gane mgnar mutaneba in yana ganin bakinsu,
maganin ta babballa kana ta mik'a mishi.
Hannun dama yasa ya amsa kana ya afasu a baki tare da amsar robar ruwan da ta mik'o mishi,
sannan ya had'iyesu, bayan ta gama mishi komaine ta k'ara mishi gudun AC ganin tunda ta mishi allurar yake d'an had'a zufa,
gaban gadon ta dawo ta gyara mushi mayafin sannan ta kalleshi tare da cewa.
"Zan tafi gida, dare yayi, dan kai gobe da sassafe zan dawo Allah ya baka lfy, da masu kula da kai zasu ku kwana tare."
A ranshi yace.
"Amin ngd." a zahiri kuma bai kuma kulataba,
itako fita tayi,
shi kuwa text yayiwa Rahma da Raliyya da Hayatuddeen kana yayi addu'a ya rufe ido dan allurar ta fara sashi gyangyad'i.
Rahma kam dama da Adnan zai taho cewa yayi ta koma Side d'in Mamanshi dan yana soron kartayi ta kuka,
kuma Alhamdulillahi dake uwar mijintan na sonta suna kuma tausaya mata suna kula da ita shiyasa ta d'an sake bare yanzu da taga text d'in k'anin nata yana ce mata.
"Adda, yanzu Ya Adnan yazo, mukasha hira, yace min wai kince sai dai ku taho tare,
ni kuwa gani garau na samu sauk'i itama Ummi da Hayatudden zasu dawo, an bar gida ba manya ga Ahmad ma yazo nan, duk sun tare a kaina sai kace basu da aikin yi."
murmushi tayi tare da cewa.
"Zan zo kam in su Ummi sun dawo, in banzo na gankaba to wa zai zo ya ganka?."
murmushi yayi kana yace mata.
"Budurwata mana zatazo."
dariya tayi cikin samun nitsuwa tace.
"Iye to me sunanta surkar tawa."
kai ya rausayar tare da cewa.
"Sai na dawo zan gaya miki." daga nanne ya rufe wayar tashi.
Shiko Dr Adnan tare suka tafi da Dr Aliyu a can ya kwana.
Ummi kuwa tunda suka koma ta kasa samun sukuni duk da ta fawwala Allah lamarinta,
Amman ta kasa cin abinci,
Hayatuddeen kuwa ya d'an sake sabida yadda Ya Rabi'u, da Ya ishaq da Ahmad suka rink'a yi mishi nasiha da bashi k'arfin guiwa da nuna mishi yarda da k'addara.
Aunty Mami kuwa tausayin Ummi ya hanata sukuni sabida da ka ganta kasan tana cikin damuwa da fargaba,
shiyasa data gama shirin baccinta ta kuma soya mata gwai da biredi kana ta had'a mata tea ta nufi d'akin da suka sauk'i Ummin inda suke sauk'e Mamansu Ishaq in tazo.
bisa sallaya ta sameta tana rik'e da carbi,
gefenta ta zauna tare da tank'oshe k'afafunta, ganin har yanzu Ummi hawaye take zubdawa cikin sanyi Aunty Mamin tace.
"Kiyi hak'uri Ummi ki dena kuka dan Allah kiyi ta mishi Addu'a, insha Allah zai samu lfy."
cikin sanyin murya tace,
"Mami ya zanyi in banyi kukaba, me zanyi da hawayen nawa, ce minfa sukayi Saifuddeen na bazai sake tsayawa da k'afafunshi ba."
cikin tausasawa tace.
"A a fa Ummi ana kyautata zaton wata rana zai iya mik'ewa."
kai ta jinjina kana tace,
"Kayya ba dai boye min sukeyi ba, hakama sukayi min lokacin Nuruddeen da Abbansu."
Sai kuma ta share hawayenta cikin tarin damuwa taci gaba da cewa.
"Ina rasa nitsuwata da konciyar hankali na in naga Saifuddeen yana cikin wani hali,
ina jin tausayinshi a raina ina rasa samun nitsuwata gaba d'aya a kanshi,
ina tausayawa Saifuddeen in na tuna lfy lau na haifeshi, sai kuma abubuwa suketa biyu bayan rayuwarshi."
cikin tausayawa Aunty Mami tace.
"Ummi. Wayene Nuruddeen d'in da Abbansu?."
a hankali Ummi ta nisa kana cikin sanyi ta fara bata lbrin asalinsu Saifuddeen dama yadda ya samu larurar rashin ji...
Cikin tsananin kuka da tausayawa Aunty Mami tayi saki wani nannauyan ajiyan zuciya.
Numfashi ta fudda a hankali sannan ta jingina da gadon tana mai sheshesk'an kuka har saida Ummi ta dawo tana bata hak'uri,
cikin rauni ta share hawayenta tare da cewa.
"In sha Allah daga yanzu duk sanda nayi salla zansa Saifuddeen cikin addu'o'i na ya bani tausayi tun yana yaro k'arami yayita fuskantar k'alubalen rayuwa."
sai ta kuma gyara zamanta tare da cewa.
"Dan Allah Ummi na rok'eki ki daina yawan kuka,
kiyi ta mishi addu'a in sha Allah Saifuddeen bazai tab'eba."
Sassanyan ajiyan zuciya Ummi ta sauk'e tare da cewa.
"In sha zan daina yawan kukan zanyi ta mishi addu'a."
cikin jin dad'i ta mik'a mata kofin tea d'in,
ba musu ta karb'a tare da cewa.
"Ngd Allah ya miki al'barka."
Amin Amin tace sannan ta mik'e ta fita dan bata wuri.
Washe gari kuwa tuni Doctor Aliyu ya harhad'a dukkan bayanan cutar Saifuddeen ya turawa Dr Acash prasat wanda yake aiki a wani babban asibiti dake New Delhi India,
Ahmad kuwa E passport d'in Saifuddeen da Hayatuddeen da nashi ya tattara ya nufi Airport tun da sanyin safiya ya fara musu cuku-cukun samun visa,
A nan ya samu Adnan ya taho dan tare zasu tafi dole yayi musu jagora a matsayinshi na likita da yaso ace da Dr Aliyu zasuje to shi aiyuka sun mishi yawa,
sai da suka gama duk abinda ya dace na zirganiyar samun tafiyar nasu cikin sauri cikin sa'a kuwa suka samu jirgin da zai tashi jibi nan zuwa India direct New Delhi Indira Gandhi Enternational Airport, saida suka gama komai na tafiyar sannan suka baro airport d'in.
Ummi kuwa da Ishaq da Saifuddeen Ya Rabi'u ne ya kaisu Asibitin.
Suna isa Dr Batulu tayi musu jagora har d'akin da Saifuddeen d'in yake,
sosai Ummi taji dad'in samunshi cikin nitsuwa yana rik'e da wayarshi fuskarshi d'auke da murmushi,
da sauri ta isa bakin gadon kujerar dake kusa dashi taja ta zauna,
ishaq kuwa yana isa bakin gadon ya rik'e k'arfen gadon ya tsaya,
Hayatudddeen kuwa gefen shi ya tsaya kusa da Umminsu,
da sauri ya ajiye wayarshin tare da juyawa inda suke jin Ummi na shafa kanshi,
murmushin ya kumayi tare d'ago hannunshi ya shafa kan Hayatuddeen yayinda Ummi kuwa ke shafa kanshi,
sai ya kuma mik'o hannunshi d'aya ya kamo hannun ishaq.
Ya Rabi'u ne ya d'anyi murmushi tare da cewa.
"Masha Allah. Alhamdulillahi jiki da sauk'i ko?."
kai ya jinjina alamum eh.
Dr Batulu kuwa sai binsu da idanu takeyi cikin shawar shak'uwar dake tsakaninsu.
Cikin kula Ummi tace.
"Sannu ko babana ya jikin?."
wayarshi ya d'auka da sauri ya rubuta mata.
"Alhamdulillahi jiki da sauk'i."
cikin jin dad'i duk sukace.
"Allah ya k'aro mana sauk'i."
Amin Amin ya amsa a saman lab'b'ansa.