Sashe 102
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
A tare suka shigo duk suna riƙe da akwatuna harda ma'aikatan gidan,
haka suka dinga shigowa da haɗaɗɗun akwatunan cikin falon, saida suka ƙare
sannan suka juya suka fiti suna haki, dan sosai akwatunan suke da nauyi kasancewar kowanne ashaƙe yake da kaya.
Aunty Kubra ce ta kalli Raliya dake riƙe da ɗan Maryam tana mishi wasa,
tace.
"Ke ƙanwar ango ai bakici ta zama tashi ki nuna musu kayan."
murmushi tayi tare da cewa.
"To Aunty Kubra amman dai a tayani."
Murmushi sukayi baki ɗaya ganin yadda taketa kiciniyar bubbude akwatunan,
tare da cewa.
"Wannan turamene a ciki wannan laces, wannan shadda wanna boyel."
sai kuma ta fara jawo na ƙananun kaya dana kayan shafa wanda ta buɗe akwatuna biyu wanda suke cike maƙil da ababen shafawa na kwalliyar jiki irin na mata.
Da sauri Mommy matar Malam Adam tace.
"Masha Allah. Gsky ki huta kawai, wannan ai yafi ƙarfinki muma masu gani har mun gaji,
wani abun ai bazai ganuba,
sai dai muce Allah ya sanya al'khairi yasa al'barka a ciki."
Aunty Lubna kuwa kai kawai take jinjinawa domin idonta ya raina fata,
nakasasshen da ake zatawa riƙe ƙoƙon bara da bin kwararo lungu da saƙo yana allazi wahidin,
shine da wannan kayan lefe wanda ita dai a iya ganinta lefen Zahra buhari ne kawai ta taɓa gani wanda zatace yafi wannan, a dai gani da idonta.
Goggo Maryama kuwa tausayi suka bata ganin irin ruwan dukiya da suka binne a kan yarinyar da ta sani tabbas uwarta bazata barta ta zauna a gidan Saifuddeen ba.
Mamy ma tabbas tausayinsu taji ganin yadda sukayi ɓarin naira.
Maryam kuwa sai addu'a takeyi a ranta tana cewa.
"Ya Allah ka rufa mana asiri,
ka hana mahaifinmu jin kunya da tozarta, ya Allah ka tausasa mana zuciyar wannan baiwar taka Zaleeha kasa tayiwa mahaifinmu biyayya ta zauna lfy da mijinta da yan uwanshi."
sosai Maryam ke jin tsoron abinda zai zubarwa mahaifinsu darajarsa da mutuncinsa.
Adda Rahamace ta ɗanyi dariya kana ta jawo ɗan kit ɗin da saraƙuna suke ciki, ta buɗe babban gwal ɗin da Saifuddeen ya saya a India ta zaro ta miƙawa Mommy dake kusa da ita cikin sanyi tace.
"To ga wannan ko za'a adanashi da ban, duk da cewa sauran ma gwala gwalaine amma shi tsadansa dabanne."
sosai Mommy ta girgiza da girma da darajan gwal ɗin, mai surki da ruwan farin zinari.
amsa tayi tare da miƙawa Mamy,
mamakinsu ya ƙaru ne lokacin da Aunty Kubra ta miƙawa Aunty Lubna car key ɗin kia d'innan tare da cewa.
"Ga wannan Key d'in motar amaryarmun ce,
motar tana nan waje.
zuwa yanzu fa Mamy abin ya fara zarta zatonta cikin dattaku da nitsuwarta da iliminta tace.
"Anya kuwa, gsky Malam zaiyi faɗa in muka karɓi abubuwan nan, ko lefen ma in ya gani zaiyi faɗa."
Da sauri Goggo Dada da Aunty Kubra sukace.
"Dan Allah da manzonsa kar muyi haka daku,
Saifuddeen bazaiji daɗiba tunda shi ya gani zai iya yiwa matarsa komai,
kuma abinda nanda wani ɗan lokaci ta zama matarsa."
Murmushi Aunty Lubna tayi tare da cewa.
"Kuma shi za'ayiwa kolliyar ba."
Ta ƙarishe mgnar tana kallon Aunty Kubra wacce bazata wuce sa'arta ba.
da sauri Aunty Kubra tace.
"Ato kunga ai kanshi yayiwa tanadi, mutun da matarsa."
Goggo Maryama ne tace.
"To mu dai tunda kunce dan Allah da manzonsa to zamu amshi kayan,
saura mgna kuma tana wurin Yaya Malam."
Hajia Rabi ce tace.
"Shima anjima da dare za'a kawo sadaki fatanmu Allah yasa,
a saka bikin nanda mako ɗaya."
Amin Amin sukace baki ɗaya.
Maryam ce tace.
"ai kam naga alaman Saifuddeen ya zaƙu yana son matarsa nan kusa tunda gashi harda kayan rufi kuka kawo."
Cikin sakin fuska Adda Rahma tace.
"Sosai makuwa ,ai shi ko yau ya sameta yana so."
Daga nan suka ɗan taɓa hira sannan suma miƙe tare da cewa.
"To mu zamu tafi sai kuma in munzo ɗaukan amaryarmu."
Da sauri Mommy ta kalli Maryam da Lubna ta musu alamun su ɗauko food flasks ɗin dake cike da ababen mƙulashe.
Ganin sunata cika musu kulolin a gabansu yasa,
Goggo Dada cewa.
"wannan abu yayi yawa ku barshi."
da Saudi Goggo Maryama tace.
"A a ai yaba kyauta tukuici, ku barmu muma muyi iya iyawarmu."
Hajia Rabi ce ta kalli Mommy matar Malam Adam dake miƙa mata damin kuɗin tukuicinsu rafa guda shida yan dubu daddaya.
A hankali tace.
"Hajia wannan kuɗin kuma na menene duka?."
Cikin salon girma ba batun ƙaramta Mommy tace.
"Yaba kyauta tukuici, ba ku muka bawa ba yaran da suka shigo da kayan muka bawa."
Akan dole su,suka karɓa, nan Aunty Lubna taƙira biyu daga cikin masu aikin gidan Baba Malam ɗin suka shiga jidan food flask ɗin suna kaiwa cikin motocin da su Adda Rahama suka zo dashi.
Har bakin gate suka rakosu baki d'ayan su,
aka rabu cikin mutunci da jin dadi.
Bayan sun koma cikin gida ne,
Aunty Lubna ta kalli Maryam tare da cewa.
"Ke zo muga kayannan da kyau,".
Dariya Maryam tayi kana ta matso ta fara bubbud'e akwatunan, Mommy, Mamy, goggo Dada kuwa suma zama sukayi suna kallon kayan d'aya bayan d'aya.
yayinda tuni Aunty Lubna keta viewing tana d'aukan komai a zazzafar wayarta.
Sune basu gama ba har aka kira sallan magrib, dole suka hak'ura suka k'arisa kallon a gaggauce kana suka rufe komai,
suka shirgeshi a cikin d'akin Mama,
kana duk sukayi al'wala dan gabatar da salla.
Bayan sunyi sallah harda na isha,
sukaci abinci,
sukaci gaba da hira,
dan Maryam jira take mijinta ne zaizo ya d'auketa hakama Mommy Malam Adam ne zaizo ya d'auketa,
Goggo Maryama kuwa Ya Ahmad ne zai maidata gida.
Baba Malam kuwa, tunda yamma yake gidan Malam Adam,
dan amaryarshi bata zoba.
Ya Ahmad kuwa da Ya Aminu tunda safe suka tafi dukku kai ziyara dan Ya Ahmad ya kusa komawa Abuja.
Saida akayi sallan magriba suka dawo,
Kai tsaye parlour'n Baba Malam suka nufa,
nan Maryam ta kawo musu abinci,
bayan sun gama cine sukayi al'wala suka nufi masallaci a nan suka samu Baba malam da Malam Adam.
Koda aka idar da salla tare suka shigo cikin gida.
Suna shiga bada dad'ewa ba,
Dirankadi da Bappa Ali da Malam Ashiru suka iso harabar gidan.
Dirankadi ne ya kira Baba malam ya shaida masa isowarsu,
jin haka ya kalli Ahmad tare da cewa.
"Ahmad tashi kaje ka shigo da iyayen Saifuddeen."
Cikin tsananin girmamawa da sanin darajar mahaifa Ahmad yace.
"To." sannan ya miƙe tsaye ya fita.
Yana zuwa yayi musu jagora har zuwa parlour'n Baba Malam ɗin, sunyi farin cikin ganin juna sosai.
haka suka dinga shigowa da haɗaɗɗun akwatunan cikin falon, saida suka ƙare
sannan suka juya suka fiti suna haki, dan sosai akwatunan suke da nauyi kasancewar kowanne ashaƙe yake da kaya.
Aunty Kubra ce ta kalli Raliya dake riƙe da ɗan Maryam tana mishi wasa,
tace.
"Ke ƙanwar ango ai bakici ta zama tashi ki nuna musu kayan."
murmushi tayi tare da cewa.
"To Aunty Kubra amman dai a tayani."
Murmushi sukayi baki ɗaya ganin yadda taketa kiciniyar bubbude akwatunan,
tare da cewa.
"Wannan turamene a ciki wannan laces, wannan shadda wanna boyel."
sai kuma ta fara jawo na ƙananun kaya dana kayan shafa wanda ta buɗe akwatuna biyu wanda suke cike maƙil da ababen shafawa na kwalliyar jiki irin na mata.
Da sauri Mommy matar Malam Adam tace.
"Masha Allah. Gsky ki huta kawai, wannan ai yafi ƙarfinki muma masu gani har mun gaji,
wani abun ai bazai ganuba,
sai dai muce Allah ya sanya al'khairi yasa al'barka a ciki."
Aunty Lubna kuwa kai kawai take jinjinawa domin idonta ya raina fata,
nakasasshen da ake zatawa riƙe ƙoƙon bara da bin kwararo lungu da saƙo yana allazi wahidin,
shine da wannan kayan lefe wanda ita dai a iya ganinta lefen Zahra buhari ne kawai ta taɓa gani wanda zatace yafi wannan, a dai gani da idonta.
Goggo Maryama kuwa tausayi suka bata ganin irin ruwan dukiya da suka binne a kan yarinyar da ta sani tabbas uwarta bazata barta ta zauna a gidan Saifuddeen ba.
Mamy ma tabbas tausayinsu taji ganin yadda sukayi ɓarin naira.
Maryam kuwa sai addu'a takeyi a ranta tana cewa.
"Ya Allah ka rufa mana asiri,
ka hana mahaifinmu jin kunya da tozarta, ya Allah ka tausasa mana zuciyar wannan baiwar taka Zaleeha kasa tayiwa mahaifinmu biyayya ta zauna lfy da mijinta da yan uwanshi."
sosai Maryam ke jin tsoron abinda zai zubarwa mahaifinsu darajarsa da mutuncinsa.
Adda Rahamace ta ɗanyi dariya kana ta jawo ɗan kit ɗin da saraƙuna suke ciki, ta buɗe babban gwal ɗin da Saifuddeen ya saya a India ta zaro ta miƙawa Mommy dake kusa da ita cikin sanyi tace.
"To ga wannan ko za'a adanashi da ban, duk da cewa sauran ma gwala gwalaine amma shi tsadansa dabanne."
sosai Mommy ta girgiza da girma da darajan gwal ɗin, mai surki da ruwan farin zinari.
amsa tayi tare da miƙawa Mamy,
mamakinsu ya ƙaru ne lokacin da Aunty Kubra ta miƙawa Aunty Lubna car key ɗin kia d'innan tare da cewa.
"Ga wannan Key d'in motar amaryarmun ce,
motar tana nan waje.
zuwa yanzu fa Mamy abin ya fara zarta zatonta cikin dattaku da nitsuwarta da iliminta tace.
"Anya kuwa, gsky Malam zaiyi faɗa in muka karɓi abubuwan nan, ko lefen ma in ya gani zaiyi faɗa."
Da sauri Goggo Dada da Aunty Kubra sukace.
"Dan Allah da manzonsa kar muyi haka daku,
Saifuddeen bazaiji daɗiba tunda shi ya gani zai iya yiwa matarsa komai,
kuma abinda nanda wani ɗan lokaci ta zama matarsa."
Murmushi Aunty Lubna tayi tare da cewa.
"Kuma shi za'ayiwa kolliyar ba."
Ta ƙarishe mgnar tana kallon Aunty Kubra wacce bazata wuce sa'arta ba.
da sauri Aunty Kubra tace.
"Ato kunga ai kanshi yayiwa tanadi, mutun da matarsa."
Goggo Maryama ne tace.
"To mu dai tunda kunce dan Allah da manzonsa to zamu amshi kayan,
saura mgna kuma tana wurin Yaya Malam."
Hajia Rabi ce tace.
"Shima anjima da dare za'a kawo sadaki fatanmu Allah yasa,
a saka bikin nanda mako ɗaya."
Amin Amin sukace baki ɗaya.
Maryam ce tace.
"ai kam naga alaman Saifuddeen ya zaƙu yana son matarsa nan kusa tunda gashi harda kayan rufi kuka kawo."
Cikin sakin fuska Adda Rahma tace.
"Sosai makuwa ,ai shi ko yau ya sameta yana so."
Daga nan suka ɗan taɓa hira sannan suma miƙe tare da cewa.
"To mu zamu tafi sai kuma in munzo ɗaukan amaryarmu."
Da sauri Mommy ta kalli Maryam da Lubna ta musu alamun su ɗauko food flasks ɗin dake cike da ababen mƙulashe.
Ganin sunata cika musu kulolin a gabansu yasa,
Goggo Dada cewa.
"wannan abu yayi yawa ku barshi."
da Saudi Goggo Maryama tace.
"A a ai yaba kyauta tukuici, ku barmu muma muyi iya iyawarmu."
Hajia Rabi ce ta kalli Mommy matar Malam Adam dake miƙa mata damin kuɗin tukuicinsu rafa guda shida yan dubu daddaya.
A hankali tace.
"Hajia wannan kuɗin kuma na menene duka?."
Cikin salon girma ba batun ƙaramta Mommy tace.
"Yaba kyauta tukuici, ba ku muka bawa ba yaran da suka shigo da kayan muka bawa."
Akan dole su,suka karɓa, nan Aunty Lubna taƙira biyu daga cikin masu aikin gidan Baba Malam ɗin suka shiga jidan food flask ɗin suna kaiwa cikin motocin da su Adda Rahama suka zo dashi.
Har bakin gate suka rakosu baki d'ayan su,
aka rabu cikin mutunci da jin dadi.
Bayan sun koma cikin gida ne,
Aunty Lubna ta kalli Maryam tare da cewa.
"Ke zo muga kayannan da kyau,".
Dariya Maryam tayi kana ta matso ta fara bubbud'e akwatunan, Mommy, Mamy, goggo Dada kuwa suma zama sukayi suna kallon kayan d'aya bayan d'aya.
yayinda tuni Aunty Lubna keta viewing tana d'aukan komai a zazzafar wayarta.
Sune basu gama ba har aka kira sallan magrib, dole suka hak'ura suka k'arisa kallon a gaggauce kana suka rufe komai,
suka shirgeshi a cikin d'akin Mama,
kana duk sukayi al'wala dan gabatar da salla.
Bayan sunyi sallah harda na isha,
sukaci abinci,
sukaci gaba da hira,
dan Maryam jira take mijinta ne zaizo ya d'auketa hakama Mommy Malam Adam ne zaizo ya d'auketa,
Goggo Maryama kuwa Ya Ahmad ne zai maidata gida.
Baba Malam kuwa, tunda yamma yake gidan Malam Adam,
dan amaryarshi bata zoba.
Ya Ahmad kuwa da Ya Aminu tunda safe suka tafi dukku kai ziyara dan Ya Ahmad ya kusa komawa Abuja.
Saida akayi sallan magriba suka dawo,
Kai tsaye parlour'n Baba Malam suka nufa,
nan Maryam ta kawo musu abinci,
bayan sun gama cine sukayi al'wala suka nufi masallaci a nan suka samu Baba malam da Malam Adam.
Koda aka idar da salla tare suka shigo cikin gida.
Suna shiga bada dad'ewa ba,
Dirankadi da Bappa Ali da Malam Ashiru suka iso harabar gidan.
Dirankadi ne ya kira Baba malam ya shaida masa isowarsu,
jin haka ya kalli Ahmad tare da cewa.
"Ahmad tashi kaje ka shigo da iyayen Saifuddeen."
Cikin tsananin girmamawa da sanin darajar mahaifa Ahmad yace.
"To." sannan ya miƙe tsaye ya fita.
Yana zuwa yayi musu jagora har zuwa parlour'n Baba Malam ɗin, sunyi farin cikin ganin juna sosai.