Sashe 78
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummi da kanta ta kira Ishaq ta sanar mishi.
Kai wannan rana wannan safiya tazowa da masoyan Saifuddeen da daddad'an labari da sanyin safiya.
Kafin zuwa shabiyu duk makota da 'yan uwa anata zuwa yiwa Ummi barka.
Bappa Alima yazo da Aunty Nina da Goggo Dada maman Ahmad,
Shi kuwa Hayatuddeen
sanin bazasu barshi ya shiga bane ya sashi komawa ya d'auki wayarshi,
aifa kusan a Jere a jere kiran abokan Hamma Saifuddeen da k'annenshi ke shigowa wayarshi,
Haka ya zauna yana musu cikekken bayani yadda komai ya faru,
sai ya k'ara da ce musu yanzu an shiga dashi wani d'akin.
Haka dai yayi ta zaman jira,
Abu wasa-wasa har azahar ba'a fito da Saifuddeen ba,
Ganin haka ya kira Dr Aliyu ya sanar mishi abibda ke faruwa,
sun gama mgna da Dr Aliyu kenan sai ga Dr Acash prasat ya shigo inda yake cikin tsananin jin dad'i ya ruggume Hayatuddeen kana ya jawoshi suka zauna cikin kula yace.
"Hayatuddeen jinya tayi kyau komai yana tafiya yadda mukeso Alhamdulillahi yanzu alamomin samun sauk'i sunata k'ara baiya a wurin d'an uwanka,
tun d'azu muna tare a kanshi duk wani bincikenmu yana bamu tabbacin kaso saba'in cikin kaso d'ari na cutar ya worke a koda yaushe Saifuddeen zai iya tashi tsaye da sawunshi.
Yanzu kuma Alhamdulillahi zai iya tashi zaune daga konce,
kuma zai iya juyawa hagu da damanshi.
Sannan zai iya durk'usawa kan guiwowinshi,
kai nan gaba kad'an ma zai iya sunkuyawa,
shine zatonmu a binciken da muketa gudanarwa a kanshi.
So yanzu ka kwanrar da hankalin ka koma masauk'inka dan sai gobe zaka kuma ganinshi."
Cikin gamsuwa da jin dad'i Hayatuddeen ya gyad'a mishi kai tare da cewa.
"Thanks Doctor."
sai ya mik'e cikin jin dadi har zai fita sai Dr Acash ya jawo hannunshi gaban wani window ya kaishi tare da cewa ya lek'a.
Hammanshi ya hango cikin wata na'ura mai girma dan k'afafunshi kadaine a woje sai kanshi kad'an.
Cikin bashi k'arfin guiwa Dr Acash yace,
"Wannan shine taimako na k'arshe da akeyi masu irin larurarsa,
Yanzu sai in an fiddashi sai bayan, wata shida za'a sake sashi,
so nanda one month za'a sallameku,
in zaku iya duk bayan 6 months sai yazo a dubashi,
a k'ara canza mishi drugs d'inshi.
So ka kontarwa iyayenku hankalin kada wani yace zai zo."
Tofa wannan abu shine Noor ala noor haske kan haske,
sosai bayanin ya kontarwa Hayatuddeen hankalin.
Shiyasa cikin k'arfin guiwa ya koma masauk'inshi.
A ranar dai kam wannan family sunyi matuk'ar shiga farin ciki.
Musammam Ummi da Hayatuddeen ya mata bayanin likita, kawai sai takeji kamar bata da wani sauran damuwa a duniya.
Hakama Dr Adnan da yaji bayani a bakin Dr Malik Khan sosai ya samu konciyar hankalin.
Ahmad kuwa a ranar ya nemo ma'aikata sukazo suka gyara side d'in Hayatuddeen dan Ummi tace anan Saifuddeen zai zauna,
So an fasa duk wani wuri mai d'an tutu ko steps d'in da zai hana keken weelchair gangarawa da wucewa a sauk'ak'e.
Sosai aka gyara side d'in.
A washe garin ranar Ahmad yasa aka kawo mishi gadon samfarin royal bed kana da kujeru suma royal d'in.
Aka canza mishi AC bedroom aka dawo dashi parlour kana aka sa sabon AC a bedroom d'in.
Hatta labulaye da carpet da blanket da beshid sabbin Ahmad yasa aka saka komai na d'akin lemon green and white ne sosai kalan ya haska d'akin,
Kayayyaki sabbi dal-dal Ahmad ya sayo yazo ya jera mishi kananu na d'inkawa kuma shida kanshi ya fito da kekken d'inkin Hayatuddeen ya fara yayyarɗa mishi ɗinkunan zamani d'inka mishi.
Sosai Ummi take cikin farin ciki.
Adda Rahma kuwa a kwanakin kullum sai tazo.
Yau kwana biyar kenan da fara tashin Saifuddeen,
suna zaune shida Hayatuddeen wanda ya kira Ummi video call sai hira da dariya suke, nan Raliya ta amshi wayar ta nuna mishi yadda aka gyara mishi side d'in da zai zauna.
Murmushi yayi cikin jin dad'i da begen komawa gidan Cikin ahlinsa.
Shiko Hayatuddeen kai ya jinjina kana yace.
"Oho wato abinma son kaine, da yake Hamma ne zai zauna a nan kalli yadda kuka wani gyara d'akin tamkar makwancin shugaban k'asa.
Wato nine jaki in na ga dama in kwan a k'asa ko?."
Cikin kewar sangartarsa tace.
"Ohoho my autanmu kaima ai yanzu side naka tas yake in kana soma sama zaka koma,
inda Hamma Saifuddeen yake da."
Cikin jin dadi yace.
"Wayyo Allah kice na zama alhajin sama."
Dariya sukayi baki d'aya kana suka d'anci gaba da hira daga bisani suka salami juna.
Yau mako biyu kenan cib da fara tashin Saifuddeen zaune,
Kuma Alhamdulillahi tuni an gama mishi duk wani abinda ya dace na sallamarsa da shared'in duk bayan wata shida zaizo a duba jikinshi.
Tuni Hayatuddeen ya gama musu dukkan shirin komawarsu da taimakon Dr Malik Khan.
Nanda kwana biyu jirginsu zai d'aga zuwa Nigeria.
A cikin asibitin.
Saifuddeen na konce shi kuwa Hayatuddeen yana harhad'a duk wani abu nasu domin gobe da asuba jirginsu zai tashi.
a hankali ya zubawa d'an uwan nashi idanu ganin yadda jikinshi ke rawa kar-kar- kar tamkar mazari idanunshi sunyi jazir,
gaba d'aya jijiyoyin kanshi sunyi rud'u-rud'u wani irin zufane ya yanko mishi a take, da sauri ya matso gaban gadon cikin tsananin fargaba da tsoro murya a birkice Hayatuddeen yayi kanshi jiki na rawa.
Sai ya kumayi dib ya tsaya wuri d'aya da yake ganin Hamman nashi na jujjuya mishi kai alamun karya matsoshi.
Idanu ya zuba mishi cikin kad'uwa sai kuma ya rink'a kame jikinshi ganin Hamman nashi so yake ya durkusa,
cikin ikon Allah kuma sai gashi a durkushe bisa tsakiyar gadon.
Kusan a tare suke sauk'e numfashi,
Dai-dai lokacin kuma Dr Anan da Dr Malik Khan suka shigo.
Samunshi a haka yayi matuk'ar sasu farin ciki nan take suka k'ara gwadashi,
kana suka dank'a mishi takardar sallama da sharad'in duk bayan watanni shida zaizo.
Nan Dr Anan ya kara ink'anta mishi durkuson nasa.
Washe gari bayan an idar da sallan Asuba Dr Malik Khan yazo ya d'aukesu, da kanshi ya Kaisu Hilton international Airport Mumbai.
Bai bar airport d'inba saida yaga tashin jirginsu.
Abuja
Amina kuwa yau satinta biyu kenan tana neman Hayatuddeen bata samunshi a waya,
gaba d'aya abin ya dameta,
gashi yanzuma ta kira layin baya tafiya,
kai ta rausayar kana tace.
"Allah yasa dai lfy, sai anjima da yamma zan kuma gwadawa."
Gombawa d'iban fari.
Yau gidan Ummi a cike yake,
Raihana mutanen kd ma tun jiya tazo da Affan d'inta.
Adda Rahma kuwa itama yau sammako tayi.
Hakama goggo Dada da Aunty Mina.
Farop da Adam sai tsalle suke yau Uncles nasu zasu dawo.
Salisu ma ya kawo Salimanshi.
Gida ya kacame da shirye-shiryen tarban Hamma Saifuddeen...!
To AL'amarin Zaleeha fa ya girmama,
Domin har Ruqquya saida aka mata dan duk an d'auka gamo tayi.
Shi kuwa Baba Malam ya sani sarai babu wani gamo,
ba iska a jikinta sai dai zallan iskanci inji Kakarsu da fad'i.
Maryam Zahira kam su dai a dole Zaliha gamo tayi,
Zeyada kuwa da Zakariyya da suke wurin Hajja Inna suma mgnar kakarsu suka bawa amanna Zaliha bata da wani iska sai zallan iskanci.
Ya Ahmad d'inta kuwa wanda kwanan suka dawo Nigeria shida matarsa dan watansu bakwai a Istanbul.
kasan cewarshi mai nitsuwa da hak'uri da k'aunar kannenshi suna dawowa da kwana d'aya ya taho gombe.
Shiyasa yau gaba d'aya Baba Malam ya tarasu,
ya jaddada musu cewar Zaleeha fa tanada sauran dama na mako biyu ta fidda miji cikin tarin masoyanta,
in kuwa ta sake mako biyun nan ya cika bata tsaida gwaniba to tabbas shi zai mata zabi kuma tayi kuka da kanta.
Koda aka tashi taron bayan Ya Ahmad d'in nata tabi suka shiga parlour Mamy gabanshi ta durk'usa cikin zubda k'walla tace.
"Ya Ahmad ina sonshi, bayan shi babu wanda nakeso dan Allah ka bawa baba malam hak'uri ya rufa min asiri kada ya rabani dashi."
Hannunta ya jawo ya ajiyeta gefenshi cikin nitsuwarsa yace.
"Kin san a duniya bamu da kamar Baba Malam ko Zaleeha.?"
Kai ta gyada mishi alamar eh,
shi kuwa cikin sanyin yanayinshi yaci gaba da cewa.
"Kin san wayeshi a wurina nida Maryam da Ziyada da Habu,
bama iya jurar ganin b'acin ransa,
bama iya lamuntan duk wani abu da zai tab'a mana daraja da mutuncin mahaifinmu,
Zaleeha koda nace miki ina tare dake namiki k'arya,
zancen gsky bayan Baba malam da Ya Ameenu nake babu yadda za'ayi kiyi ta zaman jiran gaibu,
abinda ni ganima nake Al'janine ,
to tayaya zamu lamunci ki zauna zaman jiranshi.
Kawai dolenki dollen dolene ki Zab'i d'aya daga cikin masoyanki.
Ko Abdussalam ko Managernku ko Raveel ko kuma wannan abokin nawa Al'amin wanda yayi ta nace miki zuwanki Abuja last year. In kuma kinki tsaida gwani da kanki to wllahi Allah kenan Baba malam zai zaba miki cikin su."
kife kanta tayi a kafadarshi tare da sakin nakasasshen kuka tare da cewa.
"Na shiga uku ns, wlh ya Ahmad ina sonshi."
shigowan Ya Ameenu ne yasa ta mik'e da sauri ta wuce side d'insu kai tsaye bedroom d'in Mama ta wuce bisa gado ta fad'a tana kuka.
Cikin takaici Maman ta harareta tare jan dogon tsaki kana tace.
"Shirmen banza kawai ni dai ina gaya miki wallahi ko bakya son Abdussalam sai ya aureki yaro d'an manya jikan sarakuna har zakiyi ta wainashi da me kika fishi kyau ko asali ko gata,
ni dai ina gargad'inki kada ki bari Malam ya miki zaben tumun dare yadda yayiwa Maryam auren dole to bazan lamunci a miki hakaba,
shiyasa gwara ki bar batun wancan aljanin da ya taimakeki ki rik'e Abdussalam yafi miki." wannan shine rana zafi inuwa k'una jin kalaman Mamane yasa ta mike ta koma d'akinta taci ga da koke-kokenta...
Tafiya tayi nisa cikin sararin samaniya, kowa na harkan gabanshi, autan Ummu kuwa jinshi yake a takure.
Kai wannan rana wannan safiya tazowa da masoyan Saifuddeen da daddad'an labari da sanyin safiya.
Kafin zuwa shabiyu duk makota da 'yan uwa anata zuwa yiwa Ummi barka.
Bappa Alima yazo da Aunty Nina da Goggo Dada maman Ahmad,
Shi kuwa Hayatuddeen
sanin bazasu barshi ya shiga bane ya sashi komawa ya d'auki wayarshi,
aifa kusan a Jere a jere kiran abokan Hamma Saifuddeen da k'annenshi ke shigowa wayarshi,
Haka ya zauna yana musu cikekken bayani yadda komai ya faru,
sai ya k'ara da ce musu yanzu an shiga dashi wani d'akin.
Haka dai yayi ta zaman jira,
Abu wasa-wasa har azahar ba'a fito da Saifuddeen ba,
Ganin haka ya kira Dr Aliyu ya sanar mishi abibda ke faruwa,
sun gama mgna da Dr Aliyu kenan sai ga Dr Acash prasat ya shigo inda yake cikin tsananin jin dad'i ya ruggume Hayatuddeen kana ya jawoshi suka zauna cikin kula yace.
"Hayatuddeen jinya tayi kyau komai yana tafiya yadda mukeso Alhamdulillahi yanzu alamomin samun sauk'i sunata k'ara baiya a wurin d'an uwanka,
tun d'azu muna tare a kanshi duk wani bincikenmu yana bamu tabbacin kaso saba'in cikin kaso d'ari na cutar ya worke a koda yaushe Saifuddeen zai iya tashi tsaye da sawunshi.
Yanzu kuma Alhamdulillahi zai iya tashi zaune daga konce,
kuma zai iya juyawa hagu da damanshi.
Sannan zai iya durk'usawa kan guiwowinshi,
kai nan gaba kad'an ma zai iya sunkuyawa,
shine zatonmu a binciken da muketa gudanarwa a kanshi.
So yanzu ka kwanrar da hankalin ka koma masauk'inka dan sai gobe zaka kuma ganinshi."
Cikin gamsuwa da jin dad'i Hayatuddeen ya gyad'a mishi kai tare da cewa.
"Thanks Doctor."
sai ya mik'e cikin jin dadi har zai fita sai Dr Acash ya jawo hannunshi gaban wani window ya kaishi tare da cewa ya lek'a.
Hammanshi ya hango cikin wata na'ura mai girma dan k'afafunshi kadaine a woje sai kanshi kad'an.
Cikin bashi k'arfin guiwa Dr Acash yace,
"Wannan shine taimako na k'arshe da akeyi masu irin larurarsa,
Yanzu sai in an fiddashi sai bayan, wata shida za'a sake sashi,
so nanda one month za'a sallameku,
in zaku iya duk bayan 6 months sai yazo a dubashi,
a k'ara canza mishi drugs d'inshi.
So ka kontarwa iyayenku hankalin kada wani yace zai zo."
Tofa wannan abu shine Noor ala noor haske kan haske,
sosai bayanin ya kontarwa Hayatuddeen hankalin.
Shiyasa cikin k'arfin guiwa ya koma masauk'inshi.
A ranar dai kam wannan family sunyi matuk'ar shiga farin ciki.
Musammam Ummi da Hayatuddeen ya mata bayanin likita, kawai sai takeji kamar bata da wani sauran damuwa a duniya.
Hakama Dr Adnan da yaji bayani a bakin Dr Malik Khan sosai ya samu konciyar hankalin.
Ahmad kuwa a ranar ya nemo ma'aikata sukazo suka gyara side d'in Hayatuddeen dan Ummi tace anan Saifuddeen zai zauna,
So an fasa duk wani wuri mai d'an tutu ko steps d'in da zai hana keken weelchair gangarawa da wucewa a sauk'ak'e.
Sosai aka gyara side d'in.
A washe garin ranar Ahmad yasa aka kawo mishi gadon samfarin royal bed kana da kujeru suma royal d'in.
Aka canza mishi AC bedroom aka dawo dashi parlour kana aka sa sabon AC a bedroom d'in.
Hatta labulaye da carpet da blanket da beshid sabbin Ahmad yasa aka saka komai na d'akin lemon green and white ne sosai kalan ya haska d'akin,
Kayayyaki sabbi dal-dal Ahmad ya sayo yazo ya jera mishi kananu na d'inkawa kuma shida kanshi ya fito da kekken d'inkin Hayatuddeen ya fara yayyarɗa mishi ɗinkunan zamani d'inka mishi.
Sosai Ummi take cikin farin ciki.
Adda Rahma kuwa a kwanakin kullum sai tazo.
Yau kwana biyar kenan da fara tashin Saifuddeen,
suna zaune shida Hayatuddeen wanda ya kira Ummi video call sai hira da dariya suke, nan Raliya ta amshi wayar ta nuna mishi yadda aka gyara mishi side d'in da zai zauna.
Murmushi yayi cikin jin dad'i da begen komawa gidan Cikin ahlinsa.
Shiko Hayatuddeen kai ya jinjina kana yace.
"Oho wato abinma son kaine, da yake Hamma ne zai zauna a nan kalli yadda kuka wani gyara d'akin tamkar makwancin shugaban k'asa.
Wato nine jaki in na ga dama in kwan a k'asa ko?."
Cikin kewar sangartarsa tace.
"Ohoho my autanmu kaima ai yanzu side naka tas yake in kana soma sama zaka koma,
inda Hamma Saifuddeen yake da."
Cikin jin dadi yace.
"Wayyo Allah kice na zama alhajin sama."
Dariya sukayi baki d'aya kana suka d'anci gaba da hira daga bisani suka salami juna.
Yau mako biyu kenan cib da fara tashin Saifuddeen zaune,
Kuma Alhamdulillahi tuni an gama mishi duk wani abinda ya dace na sallamarsa da shared'in duk bayan wata shida zaizo a duba jikinshi.
Tuni Hayatuddeen ya gama musu dukkan shirin komawarsu da taimakon Dr Malik Khan.
Nanda kwana biyu jirginsu zai d'aga zuwa Nigeria.
A cikin asibitin.
Saifuddeen na konce shi kuwa Hayatuddeen yana harhad'a duk wani abu nasu domin gobe da asuba jirginsu zai tashi.
a hankali ya zubawa d'an uwan nashi idanu ganin yadda jikinshi ke rawa kar-kar- kar tamkar mazari idanunshi sunyi jazir,
gaba d'aya jijiyoyin kanshi sunyi rud'u-rud'u wani irin zufane ya yanko mishi a take, da sauri ya matso gaban gadon cikin tsananin fargaba da tsoro murya a birkice Hayatuddeen yayi kanshi jiki na rawa.
Sai ya kumayi dib ya tsaya wuri d'aya da yake ganin Hamman nashi na jujjuya mishi kai alamun karya matsoshi.
Idanu ya zuba mishi cikin kad'uwa sai kuma ya rink'a kame jikinshi ganin Hamman nashi so yake ya durkusa,
cikin ikon Allah kuma sai gashi a durkushe bisa tsakiyar gadon.
Kusan a tare suke sauk'e numfashi,
Dai-dai lokacin kuma Dr Anan da Dr Malik Khan suka shigo.
Samunshi a haka yayi matuk'ar sasu farin ciki nan take suka k'ara gwadashi,
kana suka dank'a mishi takardar sallama da sharad'in duk bayan watanni shida zaizo.
Nan Dr Anan ya kara ink'anta mishi durkuson nasa.
Washe gari bayan an idar da sallan Asuba Dr Malik Khan yazo ya d'aukesu, da kanshi ya Kaisu Hilton international Airport Mumbai.
Bai bar airport d'inba saida yaga tashin jirginsu.
Abuja
Amina kuwa yau satinta biyu kenan tana neman Hayatuddeen bata samunshi a waya,
gaba d'aya abin ya dameta,
gashi yanzuma ta kira layin baya tafiya,
kai ta rausayar kana tace.
"Allah yasa dai lfy, sai anjima da yamma zan kuma gwadawa."
Gombawa d'iban fari.
Yau gidan Ummi a cike yake,
Raihana mutanen kd ma tun jiya tazo da Affan d'inta.
Adda Rahma kuwa itama yau sammako tayi.
Hakama goggo Dada da Aunty Mina.
Farop da Adam sai tsalle suke yau Uncles nasu zasu dawo.
Salisu ma ya kawo Salimanshi.
Gida ya kacame da shirye-shiryen tarban Hamma Saifuddeen...!
To AL'amarin Zaleeha fa ya girmama,
Domin har Ruqquya saida aka mata dan duk an d'auka gamo tayi.
Shi kuwa Baba Malam ya sani sarai babu wani gamo,
ba iska a jikinta sai dai zallan iskanci inji Kakarsu da fad'i.
Maryam Zahira kam su dai a dole Zaliha gamo tayi,
Zeyada kuwa da Zakariyya da suke wurin Hajja Inna suma mgnar kakarsu suka bawa amanna Zaliha bata da wani iska sai zallan iskanci.
Ya Ahmad d'inta kuwa wanda kwanan suka dawo Nigeria shida matarsa dan watansu bakwai a Istanbul.
kasan cewarshi mai nitsuwa da hak'uri da k'aunar kannenshi suna dawowa da kwana d'aya ya taho gombe.
Shiyasa yau gaba d'aya Baba Malam ya tarasu,
ya jaddada musu cewar Zaleeha fa tanada sauran dama na mako biyu ta fidda miji cikin tarin masoyanta,
in kuwa ta sake mako biyun nan ya cika bata tsaida gwaniba to tabbas shi zai mata zabi kuma tayi kuka da kanta.
Koda aka tashi taron bayan Ya Ahmad d'in nata tabi suka shiga parlour Mamy gabanshi ta durk'usa cikin zubda k'walla tace.
"Ya Ahmad ina sonshi, bayan shi babu wanda nakeso dan Allah ka bawa baba malam hak'uri ya rufa min asiri kada ya rabani dashi."
Hannunta ya jawo ya ajiyeta gefenshi cikin nitsuwarsa yace.
"Kin san a duniya bamu da kamar Baba Malam ko Zaleeha.?"
Kai ta gyada mishi alamar eh,
shi kuwa cikin sanyin yanayinshi yaci gaba da cewa.
"Kin san wayeshi a wurina nida Maryam da Ziyada da Habu,
bama iya jurar ganin b'acin ransa,
bama iya lamuntan duk wani abu da zai tab'a mana daraja da mutuncin mahaifinmu,
Zaleeha koda nace miki ina tare dake namiki k'arya,
zancen gsky bayan Baba malam da Ya Ameenu nake babu yadda za'ayi kiyi ta zaman jiran gaibu,
abinda ni ganima nake Al'janine ,
to tayaya zamu lamunci ki zauna zaman jiranshi.
Kawai dolenki dollen dolene ki Zab'i d'aya daga cikin masoyanki.
Ko Abdussalam ko Managernku ko Raveel ko kuma wannan abokin nawa Al'amin wanda yayi ta nace miki zuwanki Abuja last year. In kuma kinki tsaida gwani da kanki to wllahi Allah kenan Baba malam zai zaba miki cikin su."
kife kanta tayi a kafadarshi tare da sakin nakasasshen kuka tare da cewa.
"Na shiga uku ns, wlh ya Ahmad ina sonshi."
shigowan Ya Ameenu ne yasa ta mik'e da sauri ta wuce side d'insu kai tsaye bedroom d'in Mama ta wuce bisa gado ta fad'a tana kuka.
Cikin takaici Maman ta harareta tare jan dogon tsaki kana tace.
"Shirmen banza kawai ni dai ina gaya miki wallahi ko bakya son Abdussalam sai ya aureki yaro d'an manya jikan sarakuna har zakiyi ta wainashi da me kika fishi kyau ko asali ko gata,
ni dai ina gargad'inki kada ki bari Malam ya miki zaben tumun dare yadda yayiwa Maryam auren dole to bazan lamunci a miki hakaba,
shiyasa gwara ki bar batun wancan aljanin da ya taimakeki ki rik'e Abdussalam yafi miki." wannan shine rana zafi inuwa k'una jin kalaman Mamane yasa ta mike ta koma d'akinta taci ga da koke-kokenta...
Tafiya tayi nisa cikin sararin samaniya, kowa na harkan gabanshi, autan Ummu kuwa jinshi yake a takure.