← Book details Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 116

Sashe 18

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Yana shiga kai tsaye dilansu ya wuce yana zuwa ko yayi sa'a ba layi sosai tofa nan take aka bashi na 60k ganin bashi da wurin zubasu ne sai yace musu bari yazo,
shagonsu Hisham yaje yace musu kwali yakeso nan take suka bashi yankekken kwalin Gas
yana amsa yaje ya cika kwalin da lododin.
Da shagon ba mishkila ya fara dan yafi kusa dashi kuma yasan me yawa zasu karb'a zasu rage mishi nauyi,
yana zuwa kuma ya samu shagon a cike mak'il da masu sayan abubuwa irin su Gero, kunu gyad'a kunun wake k'osai, waken awara.
Rid'i, sugar, madara, acca, al,kama, masara, maiwa, shinkafa, dawa, fulawa, da dai sauransu a k'alla yaran shagon sun kai goma amman still ga layin masu awu,
d'aya daga cikin yaran shagon ne ya yafitoshi tare mik'o mishi 5k d'in jiyan kana yace.
"Alhaji yace yau na 15k zaka bamu ko?."
kai ya gyad'a mishi kana ya sunkuyo ya rink'a mik'o mushi faket-faket na ledodin hawa-hawa kamar dai yadda yaga Baba Bello ya basu jiya.
Yana basu ya rubuta kana ya bawa yaron shima yasa hannu,
daga nan ya fara bin duk shagunan da Dottijon ya nuna mishi,
inda yasamu wasu basu firfitoba,
sai ya wuce gaba, wasu a dawowa sai ya samu suna bud'e shagun nasu sai ya basu,
yana basu suna bashi kud'in na jiya,
haka dai tuni kafin k'arfe sha d'aya ya gama rabawa,.
Cikin nitsuwa ya koma rumfar dilan nasu inda ya had'a lissafin kud'in ya samu dubu hamsin da shida ne ga 2k d'in da Baba Bella ya bashi jiya nan ya had'asu wuri d'aya 8k kenan.
wato fad'in farin cikin da Saifuddeen yayi a wannan lokacin bazai yuwuba.
Kawai sai yayi sujjada ya godewa Allah gashi yau da ribarshi kusan 8k.
ai cikin aminci da farin ciki ya basu kud'insu 50k dai-dai kana aka d'auko littafi akayi alamar ya biya na jiya sai kuma na gobe 60k cikin tsananin farin ciki yasa kud'inshi a al'jihu kana ya bar shagon da zummar sai gobe.

Tuni kasuwa ta cika tayi tambul sabida yawanci akanzo da sanyin safiya koda maraice sabida yanayin azumi ba'a zuwa da tsakiyar rana.

Bayan ya gama rabawanne
sai ya kuma d'auko botikin pure water inshi ya saro leda d'aya,
dan bin shawaran baba bello amman ina a gari na gombe garin musulmai zakayi yawa har ka gaji cikin kasuwar gombe da wuya kaga arne ba irin kasuwar Yolanmu ba,
ita kasuwar gombe du musulmaine sai yerobawa da terawa kuma duk masallatane bana ce ba kirsoticiba amman gsky basu da yawa.
ganin wahalar banza zaisha sai ya rabawa Al'majirai ruwan.

Shagonsu Jabeer yaje wai ko su d'an tab'a hira amman ina sai ya samu shagon mak'il da mata ba ko hanyar wucewa,
dole ya wuce shagonsu Hisham still nanma shagon cike yake da mata,
gun bayarben nan mai robobi yaje canma kazalika,
koda ya koma shagonsu Kabir mai ruwa kuma sai ya sumu sun rufe wai saida yamma zasu dawo su bud'e.
gefen shagon nasu ya zauna ya lumshe ido yana nazarin to sana'ar me zaiyi,
ya dad'e yana tunani a ranshi yake cewa.
"Alhamdulillahi Allah ban raina sana'ar daka baniba,
Allah kaine mai badawa ka kuma k'arawa mutun ya rabbil izzati ka nunamin wata sana'ar da zanyi mana kar in wuni zaman kare a karofi."
yana gama fad'in haka a ranshi sai ya bud'e idanunshi yana bud'esu ko sai kan wani mai saida omo irinsu Good mama kilin Zep viva sabulun kamaru da dai sauransu.
da sauri ya mik'e yaje ga saurayin mai amalanken kana ya yagi takarda ya rubuta mishi cewa,
shima yana son saida su omon ya nuna mishi inda zai sara,
cikin gatsali da zoleya saurayin yace.
"Hahaha kanada amalanken ne, ko akai zaka d'ora kana da kud'in jarin ne?."
rubuta mishi amsa yayi cewa a kwali zasu bashi zai d'aura a kai.
cikin zolaya ya nuna mishi shagon da suke sari,
aiko yana zuwa sai yaga suma shagon ya kawo musu leda koda ya rubuta wa mai shagon dalilinshi ba b'ata lokaci ya bashi su Omo kan ya saida ya d'auki ribarshi ya kawo mishi uwar kud'i.

Kamar wasa ya aza kwalin su omo yana yawo koro-koro sak'o da luggu,
amman ina ko asi bai saidaba.
har azahar har yayi niyar in yayi salla zai maida musu sai ya kuma fasa,
koda akayi salla sai yaci gaba da zagaye har ya shiga layin yan badaru,
nan aka fara kiranshi ana saya kad'an-kad'an sai gashi kafin la'asar ya saida stab yana had'a kudin yaga dubu hud'u ne kuma kayan 3,500 aka bashi kenan yaci ribar d'ari biyar a ciki dan harda irin manyan nan na 500.
koda ya kai kud'in sai ya kuma amsar wani cikin ikon Allah shima ya saida.
aifa ranar da Jabeer ya ganshi dasu Omo da sabulu ya mishi tsiya wai ko dai aure yake bid'ane.

K'arfe biyar saura ya maida kwalin oman da sauran nan ya samu ribar 200 lissafin ribarshi yau dubu takwas kenan,
hamdala yayi kana ya duba agogon hannunshi ganin biyar saura kwata,
sai ya nufi gaban wani mai dabino,
mudu d'aya ya saya, kana ya fito bakin kasuwar inda yaga mai kankana dasu lemu da ayaba kankana ya saya babba da k'ari kana ya sayi lemun d'ari uku,
duk dai dubu d'aya ya kashe tsakanin dabino da lemu da ayaba,
ganin saura 7 minutes buyer ta cika sai ya gangara gefen masu nama/naman 1k ya saya,
sannan ya sayi su tattasai, albasa, attaruhu, karas, kabeji. da dai sauransu a ta k'aice dai 3k ya kashe kana sannan ya adana 5kbda zummar in ya koma zaiyi musu asusunsu da ban ribar omo d'ari takwai d'innan kuma ya barsu a aljihu ko ya rink'a jin kud'i a jikinshi. biyar dai-da Salisu yazo suka tafi.

Alhamdulillahi sun isa Dukku rana tanayin mudun kuyangi alamun ta kusa fad'uwa.
inda ya samu tuni Rahma sarkin aiki ita da Raihana sun gama komai,
inda sukayi kunun gyad'a mai kyau, da tea daya sha kayan k'amshi sai soyayyan doya daya sha kwai dasu albasa da citta kanumfari onga,
sai kuma tea wanda akayi dan Saifuddeen da Bappa Ali,
kana sai jolof d'in taliya da yasha kifi,
sannan sai biredi da aka soya da kwai sai kuma su dabinon da kankana da ayaba da lemun daya kawosu yanzu.
da sauri Raihana ta amshi ledodin kana ta mik'awa Adda Rahma ledan naman dasu tattasan,
ita kuma ta d'ebo ruwa a roba tare da d'an tarfa gijishi kana tazo wonkesu ayaban da kankanan da lemun kafin ta yankasu kana dabinonma ta wonke,
shi kuwa tuni ya shiga wonka yana fitowa yasa Hayatuddeen yaje ya kira mishi Salisu,
kafin ya shafa mai ya fito har sun taho tare,
kana su Ummi sun gama shirya komai Raliyya ta kaiwa Aunty Nina nata sannan na bappa Ali da ban,
tuni ita kuma Rahma ta had'awa Saifuddeen nashi da abokinshi,
su kuwa duk sunyi al'wala kowa na zaune rik'e da carbi,
yayinda Raliyya ke rik'e da dabino a hannu alamun kiran salla kawai take jira Raihana kuma ruwa tafi bege,
ana kiran salla duk sukayi addu'a kana aka fara bud'a baki,
da sauri Ummi ta rik'e hannun Raihana kana tace.
"Ki fara da dabino kafin kisha ruwa."
da sauri ta amshi dabinon.

Su kuwa Saifuddeen da Salisu dabinon sukaci bayan sunyi addu'a sannan suka sha kankanar da Adda Rahma tayi mata mayafi da garin madara,
saida sukayi gyatsa kana suka mik'e jin ana shirin tada ik'ama a massalacin nasu yasa suka kuskure baki kana suka tafi dan dama duk sunyi al'wala suna fita harbar matsallacin ana...!

By
*GARKUWAR FULANI*

*NAKASA BA KASAWA BACE*

*PAGE 6*

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

```Hukuncin Allah fans one ku na musamman ne a gareni fatana, Allah ya bar zumunci da ƙauna a tsakaninmu```

_Littafinga na kuɗine nairanki ɗari uku kacal ya biya miki buƙata ,turo katin mtn na 300 ta wannan number 09097853276 ko transfer ta 0005388578 jaiz bank Aisha Garkuwa Aliyu, sai ka/ki turo shaidar biyanki ta wannan number 09097853276_

free page

Suna isa harabar masallacin suka d'an k'ara sauri sabida tuni liman ya kabbarta.
Bayan anyi salla an idar duk sai kowa ya firfito dan a d'anci wani abu, wasu kuma zafine yasa suka fito sabida babu wuta kuma basu da gen kana in mutun ya wuni da azumi tofa lokacin da kasha ruwa zufa na iya keto maka.

To hakane ta kasance dasu d'in.
da yawa cikin gida suka shisshiga,
haka ma su Saifuddeen da Salisu tare da Mudassir da suka samu a masallacin,
suna shiga Ummi suka gaida kana suka wuce d'akin Saifuddeen inda suna shiga wuta ta dawo,
dan haka cikin farin ciki suka zauna Rahma da kanta ta kawo musu abincin suma tea sukace zasu sha dan haka ta kawo musu kana ta aika musu ruwan sanyi soyayyan doya da kwan sukaci suna korawa da ruwan tea da yaketa k'amshi,
daga nan kuma cikinsu ya cika,
suna cikin hira sukaji an kira sallan isha,
kusan a tare suka mik'e sukaje suka sabunta al'wala a tsakar gidan kana suka nufi woje suna fita suka shiga sahu, bayan anyi isha sai kuma aka fara yin sallan asham.
Suma su Ummi suka sabunta al'wala kana suka fara sallan.
Chapter 18 · 0% Book details