Sashe 7
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Washe gari da safe duk suna tsakiyar gidan time to time in Ummi ta kallesu sai tayi ta zubda hawaye.
ganin haka duk sai jikinsu yayi sanyi,
Rahma kam tuni kuka takeyi dan ita kam rayuwa ta mata zafi ba miji ba uba ba yayansu jigonsu, wanda suke ganin zai zama gatan nasu kuma gashi kurmane.
jin kukan Rahma yasa Ummi tsananta kukanta,
shi kuwa Saifuddeen idanu ya rumtse sabida ba abinda yafi tsana a duniya kamar yaga hawayen Umminshi,
Raihana kuwa ruggume Hayatuddeen tayi tana kuka Raliyya kuwa su Faruq ta ruggume.
Suna cikin haka sukaji sallama,
cikin sauri Ummi ta d'ago kanta jin muryar Bappanta k'anin babanta da Goggonta, sai matar Bappan nata iya bukku muguwar mace, shiyasa Ummi take rayuwa tamkar bata da dangin Uba.
da sauri ta taso ta nufi Goggonta,
kan taburma suka zube nan raunin Ummi ya tashi ganin danginta kife kanta tayi kan cinyar Goggo Rabinta d'in ta saki wani marayan kuka.
itama Goggo Rabi kukan takeyi dan tausayawa d'iyar yayanta.
hakama Bappa idintan shima kukan yakeyi dan tausayawa rayuwar Ummi da yaranta,
ita kuwa Iya Bukku sai wani mugun kallo na rashin imani take bin su Rahma dashi.
Yayinda shi kuwa Saifuddeen ita ya zubawa idanu ganin mugun kallom data juyo tana yiwa Ummimshi.
cikin tausayawa Goggo Rabi ta d'ago Ummi cikin sanyin murya tace.
"Kiyi hak'uri Bisije dukkan tsanani yana tare da sauk'i, ki dena musu kuka Allah yana sane dake da marayunki."
murya a disashe Ummi tace.
"Goggo Rabi ya zanyi ina zan shiga a duniyar nan inji dad'i wa zai rik'e min yarayuna wazai tallafawa maraicina dana yarana da marayun jikokina?".
sai ta kuma juyowa ta kalli Bappa idin nata cikin rawan murya tace.
"Bappa ya zanyi wa zai zama gatanmu wa zai zama garkuwarmu, tunda shima bappan su Rahma ba wadata yakeda shiba, sana'ar me zanyi in rik'e yarana?."
kafin Bappa idin yayi mgna tuni iya bukku ta cab'e mgnar da cewa.
"Wannan kurman d'an naki mai kama da dutse shi baida amfanin komai ne?."
sai ta kuma tsuke fuska dan bata son bappa idi yace zai d'aukesu su koma garinsu dasu,
da sauri ta kauda kanta lokacin da ta kalli Saifuddeen sabida wani irin mugun kallo daya watsa mata.
sai kuma ta tsuke fuska kana taci gaba da cewa.
"In dai bazai amfanekiba ai sai ku jefar dashi ku huta da ciyar da mai zubin mutanen b'oye yaro tun yana k'arami ni tsoro yake bani dan wannan kyawun nashi ya zarta na mutanen mu.
in kuma bazaki iyaba, tunda ke jakar 'ya'yace akan yaranki zaki mutu,
to sai ki shiga cikin gari kije gidajen masu kud'i kina musu share-share da wanke-wanke da girki, suna baki dubu 6 a wata kullum kuma kina kwatsawa zugan yaran naki tuwo, nasan harda k'anzo zasuke baki."
wani irin mugun kallo da tsana Saifuddeen yake cilla mata,
domin tunda yake a duniya bai tab'a jin mgnar da tai mishi zafi kamar wannarba, kana bai taba jin mutun mai munanan kalamaiba kamar iya Bukku ba.
Goggo Rabi kuwa kai ta rink'a jujjuyawa alamar batajin dad'in kalaman da matar yayan nata takewa d'iyar yayanta marigayi.
Bappa idi kuwa sunkuyar da kanshi yayi dan yasan motsi kad'an zaiyi iya Bukku zata solleshi.
Raihana ce ta share hawayenta tare da murgud'a mata baki kana tace.
"Allah ya kiyaye Umminmu tayi ai katau a gidajen wasu,
kuma Hamma Saifunmu ba k'aton banza bane kurwarshi kur sai dai kici kanki wlh yafi k'arfinki,
har zakice mishi baida amfani to in sha Allah aniyarki kanki zata kom...!"
da sauri tayi shiru dan bugun da taji Ummi ta kaimata a baki tare da cewa.
"Raihana ki kiyayeni fa, banfa miki irin wannan tarbiyarba maza tashi ki bar nan."
cikin sanyi ta mik'e tare watsawa iya Bukku harara kana tace.
"Kiyi hak'uri Umminmu bazan k'araba."
Goggo Rabi kuwa ji tayi kamar ta goya Raihana dan dad'in ta sulle iya Bukku.
shima bappa idin dad'i yaji.
shi kuwa Saifuddeen, Ummi ya zubawa ido yana karanto bac'in ranta,
sai ya kuma juyawa ya kalli Rahma da ta sunkuyar da kanta hawaye na zubo mata.
itako Iya Bukku cikin masifa da rashin mutunci tace.
"Kaji hegiyar yarinya mai kama da aljan kujiye min fitsarerriyar yariya da uwarta bata haifeta da bisimillaba,
ke har kin kai ki zageni?
to na fad'a bashi da amfani, ai da yana da amfanin da ya tsare muku maraicinku,
ya zauna kamar dutse ya wani zuba min shegun idanunshi ya had'e wannan fuska tashi mai kama data al'jamu."
sai ta kuma ja tsaki kana ta mik'e tsaye tare da juyowa ta kalli Saifuddeen da zuciyarshi ke tafarfasa da sauri ta kauda idonta daga kanshi sabidah arararda yake watsa.
cikin k'arfin hali tace.
"Wannan da gani rabi mutum ne rabi aljan, mutun da aljan.
Dan duk zuriyar kakanunku babu kekyawa kamanshi wannan kyau bana Allah da annabi bane, hege mai jajen kunnuwa da labban baki."
sai ta kuma juyo ta fuskancesu baki d'aya kana tace.
"Bisije in kin yarda da shawarata wlh ki kaishi bakin kogi dan da gani wannan d'an ruwane,
in kuma kingi to ki bashi k'ok'on bara yaje yayi ta bara a cikin Gombe nasan wasu ko dan kyanshi zasu bashi sadaka, tunda nakasasshene bararce kawai aikinshi ai."
cikin zafin rai Rahma ta mik'e tare da tsuke fuska kana tace.
"Bamu jikiba! aniyar kura tabi daji!
k'anina ba nakassashe bane, domin nakasar zuciya itace sahihiyar nakasa ba nakasar gangan jikiba.
In sha Allah har abadan Saifuddeen bazaiyi bara ba, in Allah ya yarda hannunshi bazasu tab'a rik'e k'ok'on baraba.
Kuma acan zuriyarku ne ba kyawawa mu ki kallemu gaba d'ayanmu ba mummuna ki kuma bincika zuriyarmu kab kyawawane waya ce miki Baddukke yana muni bare bak'i,
to mu mune dukku jinin Dukku bamu da mutuwar zuciya,
bare muyi maula,
ki kama bakinki sai randa muka nemi al'farma a wurinki kafin ki gaya mana ba sugari,
in kyawun Saifuddeen ke baki tsoro to sai dai ki makance. Ke! da kin san k'uruciyar Abbanmu sanda yanada lfy da suma zakiyi in kin ganshi, dan haka mu kyau gadanshi mukayi ki dena cewa k'anina d'an ruwa eh!."
shiru Ummi tayi dan tasan Rahma nada hak'uri k'ureta akayi,
Raliyya kuwa sai harara taketa dokawa iya Bukku,
Goggo Rabi kuwa murmushin jin dad'i take.
Bappa idi kuwa tsorone ya rufeshi yasan in sun koma zaisha rashin mutunci dan sunfi kwana biyar da jin mutuwar tace bazasu zoba da yake can garin Hashidu suke.
shi yayi ta lallabata kan dole su zo, to yasan kanshi zata huce cewa zatayi da gayya yasata suka zo dan jikokinshi suci mata zarafi,
shiyasa duk sai ya tsure da yake dama mijin tacene.
Ita kuwa iya Bukku mari ta yarfawa Rahma,
wanda yasa suka mik'e gaba d'ayansu kana cikin masifa tace.
"To me amfanin kyan naku? Uban naku da yayi kyau d'in ina da aljani ya rayu a jikinsa ya zama mahaukaci tuburan.
To wane rana kyan naku ya muku,
tunda gaki ke bazawara baki auruba ga kuma kitika-kitikan yan mata har biyu suma basu auruba,
wata k'il basu da ko mashunshini,
gaya min me amfanin kyan naku, uwar rashin kunya?."
gaba d'aya jikin Saifuddeeem b'ari yakeyi sabida zafin zuciya irin na kurame,
ita kuwa Rahma rik'e hab'arta tayi tana kuka hakama Ummi.
Itako iya Bukku cikin iya bak'ar mgna taci gaba da cewa.
"To tunda baki san amfanin da kyan naku zai mukuba, ni bari in gaya miki,
kuje ku fara *KARUWANCI* nasan tabbas zakuyi kasuwa, kuyi karuwanci ku tara kudi dan nasan shima wannan Saifuddeen aljanin uban naku kanshi zasu dawo dan haka kuje kuyi karuwanc...?"
bata kai ga k'arishe mgnarba ta kurma wani irin razanenne ihu da ya cika unguwar baki d'aya.
bata ida dawowa haiyacintaba ta kuma kurma wani azabebben ihu,
sabida wasu zafafan maruka da Saifuddeen ya yarfa mata,
wanda a take sai ga hagwaranta a biyu a k'asa.
Ihu ta kumayi jin yasa k'afarshi ya tad'eta ta zube kasa rakacab ji kake d'im kamar an tila kayan wonki,
cikin rufewar ido da fita haiyaci Saifuddeen ya zaro ball inshi ya tsula mata d'aya zai kuma na biyu ne Ummi ta rik'o hannunshi tana kuka tana cewa.
"Saifuddeen ka rufa mana asiri muji da maraicinmu,
gaishemu fa sukazo yi."
Raliyya kuwa da Raihana sai murmushin jin dad'i suke yayinda Hayatuddeen yake tsalle yana cewa.
"Allah shi k'ara Ummi barshi ya dakata hegiya mai k'aton d'uwawu."
iya Bukku kuwa ai tana samun Ummi ta rike mata Saifuddeen cikin tsananin gigita da tsoro,
ta mike ta wawuri takalmanta a hannu gabas ta nufa a gigice sai ta kumayi kona tayi yamma kana ta juyo arewa, ganin har yanzu dai bata gane hanyar fitarba sai ta kuma yi kudu cikin tsananin gudu ta fita tare da cewa.
"Rabi, malam ku fito mugudu, aljanin sun motsa dama ba nace muku ruwa biyu bane shi ku fito mu gudu karya kashemu."
ita kam Goggo rabi niyarta zata tsaya, to ganin yayanta yabi matar tashi a guje shiyasa itama tabi bayansu a saba'in suka bar garim Dukku akan baburdin Bappa idin.
ganin haka duk sai jikinsu yayi sanyi,
Rahma kam tuni kuka takeyi dan ita kam rayuwa ta mata zafi ba miji ba uba ba yayansu jigonsu, wanda suke ganin zai zama gatan nasu kuma gashi kurmane.
jin kukan Rahma yasa Ummi tsananta kukanta,
shi kuwa Saifuddeen idanu ya rumtse sabida ba abinda yafi tsana a duniya kamar yaga hawayen Umminshi,
Raihana kuwa ruggume Hayatuddeen tayi tana kuka Raliyya kuwa su Faruq ta ruggume.
Suna cikin haka sukaji sallama,
cikin sauri Ummi ta d'ago kanta jin muryar Bappanta k'anin babanta da Goggonta, sai matar Bappan nata iya bukku muguwar mace, shiyasa Ummi take rayuwa tamkar bata da dangin Uba.
da sauri ta taso ta nufi Goggonta,
kan taburma suka zube nan raunin Ummi ya tashi ganin danginta kife kanta tayi kan cinyar Goggo Rabinta d'in ta saki wani marayan kuka.
itama Goggo Rabi kukan takeyi dan tausayawa d'iyar yayanta.
hakama Bappa idintan shima kukan yakeyi dan tausayawa rayuwar Ummi da yaranta,
ita kuwa Iya Bukku sai wani mugun kallo na rashin imani take bin su Rahma dashi.
Yayinda shi kuwa Saifuddeen ita ya zubawa idanu ganin mugun kallom data juyo tana yiwa Ummimshi.
cikin tausayawa Goggo Rabi ta d'ago Ummi cikin sanyin murya tace.
"Kiyi hak'uri Bisije dukkan tsanani yana tare da sauk'i, ki dena musu kuka Allah yana sane dake da marayunki."
murya a disashe Ummi tace.
"Goggo Rabi ya zanyi ina zan shiga a duniyar nan inji dad'i wa zai rik'e min yarayuna wazai tallafawa maraicina dana yarana da marayun jikokina?".
sai ta kuma juyowa ta kalli Bappa idin nata cikin rawan murya tace.
"Bappa ya zanyi wa zai zama gatanmu wa zai zama garkuwarmu, tunda shima bappan su Rahma ba wadata yakeda shiba, sana'ar me zanyi in rik'e yarana?."
kafin Bappa idin yayi mgna tuni iya bukku ta cab'e mgnar da cewa.
"Wannan kurman d'an naki mai kama da dutse shi baida amfanin komai ne?."
sai ta kuma tsuke fuska dan bata son bappa idi yace zai d'aukesu su koma garinsu dasu,
da sauri ta kauda kanta lokacin da ta kalli Saifuddeen sabida wani irin mugun kallo daya watsa mata.
sai kuma ta tsuke fuska kana taci gaba da cewa.
"In dai bazai amfanekiba ai sai ku jefar dashi ku huta da ciyar da mai zubin mutanen b'oye yaro tun yana k'arami ni tsoro yake bani dan wannan kyawun nashi ya zarta na mutanen mu.
in kuma bazaki iyaba, tunda ke jakar 'ya'yace akan yaranki zaki mutu,
to sai ki shiga cikin gari kije gidajen masu kud'i kina musu share-share da wanke-wanke da girki, suna baki dubu 6 a wata kullum kuma kina kwatsawa zugan yaran naki tuwo, nasan harda k'anzo zasuke baki."
wani irin mugun kallo da tsana Saifuddeen yake cilla mata,
domin tunda yake a duniya bai tab'a jin mgnar da tai mishi zafi kamar wannarba, kana bai taba jin mutun mai munanan kalamaiba kamar iya Bukku ba.
Goggo Rabi kuwa kai ta rink'a jujjuyawa alamar batajin dad'in kalaman da matar yayan nata takewa d'iyar yayanta marigayi.
Bappa idi kuwa sunkuyar da kanshi yayi dan yasan motsi kad'an zaiyi iya Bukku zata solleshi.
Raihana ce ta share hawayenta tare da murgud'a mata baki kana tace.
"Allah ya kiyaye Umminmu tayi ai katau a gidajen wasu,
kuma Hamma Saifunmu ba k'aton banza bane kurwarshi kur sai dai kici kanki wlh yafi k'arfinki,
har zakice mishi baida amfani to in sha Allah aniyarki kanki zata kom...!"
da sauri tayi shiru dan bugun da taji Ummi ta kaimata a baki tare da cewa.
"Raihana ki kiyayeni fa, banfa miki irin wannan tarbiyarba maza tashi ki bar nan."
cikin sanyi ta mik'e tare watsawa iya Bukku harara kana tace.
"Kiyi hak'uri Umminmu bazan k'araba."
Goggo Rabi kuwa ji tayi kamar ta goya Raihana dan dad'in ta sulle iya Bukku.
shima bappa idin dad'i yaji.
shi kuwa Saifuddeen, Ummi ya zubawa ido yana karanto bac'in ranta,
sai ya kuma juyawa ya kalli Rahma da ta sunkuyar da kanta hawaye na zubo mata.
itako Iya Bukku cikin masifa da rashin mutunci tace.
"Kaji hegiyar yarinya mai kama da aljan kujiye min fitsarerriyar yariya da uwarta bata haifeta da bisimillaba,
ke har kin kai ki zageni?
to na fad'a bashi da amfani, ai da yana da amfanin da ya tsare muku maraicinku,
ya zauna kamar dutse ya wani zuba min shegun idanunshi ya had'e wannan fuska tashi mai kama data al'jamu."
sai ta kuma ja tsaki kana ta mik'e tsaye tare da juyowa ta kalli Saifuddeen da zuciyarshi ke tafarfasa da sauri ta kauda idonta daga kanshi sabidah arararda yake watsa.
cikin k'arfin hali tace.
"Wannan da gani rabi mutum ne rabi aljan, mutun da aljan.
Dan duk zuriyar kakanunku babu kekyawa kamanshi wannan kyau bana Allah da annabi bane, hege mai jajen kunnuwa da labban baki."
sai ta kuma juyo ta fuskancesu baki d'aya kana tace.
"Bisije in kin yarda da shawarata wlh ki kaishi bakin kogi dan da gani wannan d'an ruwane,
in kuma kingi to ki bashi k'ok'on bara yaje yayi ta bara a cikin Gombe nasan wasu ko dan kyanshi zasu bashi sadaka, tunda nakasasshene bararce kawai aikinshi ai."
cikin zafin rai Rahma ta mik'e tare da tsuke fuska kana tace.
"Bamu jikiba! aniyar kura tabi daji!
k'anina ba nakassashe bane, domin nakasar zuciya itace sahihiyar nakasa ba nakasar gangan jikiba.
In sha Allah har abadan Saifuddeen bazaiyi bara ba, in Allah ya yarda hannunshi bazasu tab'a rik'e k'ok'on baraba.
Kuma acan zuriyarku ne ba kyawawa mu ki kallemu gaba d'ayanmu ba mummuna ki kuma bincika zuriyarmu kab kyawawane waya ce miki Baddukke yana muni bare bak'i,
to mu mune dukku jinin Dukku bamu da mutuwar zuciya,
bare muyi maula,
ki kama bakinki sai randa muka nemi al'farma a wurinki kafin ki gaya mana ba sugari,
in kyawun Saifuddeen ke baki tsoro to sai dai ki makance. Ke! da kin san k'uruciyar Abbanmu sanda yanada lfy da suma zakiyi in kin ganshi, dan haka mu kyau gadanshi mukayi ki dena cewa k'anina d'an ruwa eh!."
shiru Ummi tayi dan tasan Rahma nada hak'uri k'ureta akayi,
Raliyya kuwa sai harara taketa dokawa iya Bukku,
Goggo Rabi kuwa murmushin jin dad'i take.
Bappa idi kuwa tsorone ya rufeshi yasan in sun koma zaisha rashin mutunci dan sunfi kwana biyar da jin mutuwar tace bazasu zoba da yake can garin Hashidu suke.
shi yayi ta lallabata kan dole su zo, to yasan kanshi zata huce cewa zatayi da gayya yasata suka zo dan jikokinshi suci mata zarafi,
shiyasa duk sai ya tsure da yake dama mijin tacene.
Ita kuwa iya Bukku mari ta yarfawa Rahma,
wanda yasa suka mik'e gaba d'ayansu kana cikin masifa tace.
"To me amfanin kyan naku? Uban naku da yayi kyau d'in ina da aljani ya rayu a jikinsa ya zama mahaukaci tuburan.
To wane rana kyan naku ya muku,
tunda gaki ke bazawara baki auruba ga kuma kitika-kitikan yan mata har biyu suma basu auruba,
wata k'il basu da ko mashunshini,
gaya min me amfanin kyan naku, uwar rashin kunya?."
gaba d'aya jikin Saifuddeeem b'ari yakeyi sabida zafin zuciya irin na kurame,
ita kuwa Rahma rik'e hab'arta tayi tana kuka hakama Ummi.
Itako iya Bukku cikin iya bak'ar mgna taci gaba da cewa.
"To tunda baki san amfanin da kyan naku zai mukuba, ni bari in gaya miki,
kuje ku fara *KARUWANCI* nasan tabbas zakuyi kasuwa, kuyi karuwanci ku tara kudi dan nasan shima wannan Saifuddeen aljanin uban naku kanshi zasu dawo dan haka kuje kuyi karuwanc...?"
bata kai ga k'arishe mgnarba ta kurma wani irin razanenne ihu da ya cika unguwar baki d'aya.
bata ida dawowa haiyacintaba ta kuma kurma wani azabebben ihu,
sabida wasu zafafan maruka da Saifuddeen ya yarfa mata,
wanda a take sai ga hagwaranta a biyu a k'asa.
Ihu ta kumayi jin yasa k'afarshi ya tad'eta ta zube kasa rakacab ji kake d'im kamar an tila kayan wonki,
cikin rufewar ido da fita haiyaci Saifuddeen ya zaro ball inshi ya tsula mata d'aya zai kuma na biyu ne Ummi ta rik'o hannunshi tana kuka tana cewa.
"Saifuddeen ka rufa mana asiri muji da maraicinmu,
gaishemu fa sukazo yi."
Raliyya kuwa da Raihana sai murmushin jin dad'i suke yayinda Hayatuddeen yake tsalle yana cewa.
"Allah shi k'ara Ummi barshi ya dakata hegiya mai k'aton d'uwawu."
iya Bukku kuwa ai tana samun Ummi ta rike mata Saifuddeen cikin tsananin gigita da tsoro,
ta mike ta wawuri takalmanta a hannu gabas ta nufa a gigice sai ta kumayi kona tayi yamma kana ta juyo arewa, ganin har yanzu dai bata gane hanyar fitarba sai ta kuma yi kudu cikin tsananin gudu ta fita tare da cewa.
"Rabi, malam ku fito mugudu, aljanin sun motsa dama ba nace muku ruwa biyu bane shi ku fito mu gudu karya kashemu."
ita kam Goggo rabi niyarta zata tsaya, to ganin yayanta yabi matar tashi a guje shiyasa itama tabi bayansu a saba'in suka bar garim Dukku akan baburdin Bappa idin.