Sashe 26
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Washe gari kuwa ta kama ranar ne ishirin da tara ga watan Ramadan wonda ana zaton ganin watan salla yau ko gobe dan haka da zai fita tafiya gombe sai ya harhad'a duk sauran kud'ad'en da yake adanawa ya sasu a aljihu ya tafi dasu.
To koda ya gama rarraba ledodinshi kamar kullun ya saro omonshi yayi ta yawatawa har aka k'arfe uku saura kwata bayan ya had'a ribarshi ya wuce ya maida omonshi daya rage,
daga nan ya wuce shagon Alhaji Kabiru wanda ake saida duk wani kayan d'and'anon miya kama daga Magi, raico, onga gishiri kafi Mai, Manja, fulawa, madara, sugar, sufageti, macaroni, indomi. da dai sauransu suna bada sari suna saida kad'an-kad'an kuma suma shine ke saida musu ledodin da suke zubawa kostomominsu kaya in sunyi sayayya.
Sun saba sosai da Alhaji Kabiru dan shima yanada d'anshi kurma shiyasa yake tsananin son Saifuddeen,
yana isa bak'in k'aton shagon nasu ya zaro pepar da biro ya rubuta musu duk abinda yakeso,
nan Alhaji Kabiru ya amsa da kanshi ya ware mishi duk abinda ya lissafa bayan ya gama sasu a leda cikin nitsuwarshi yace.
"Masha Allah Saifuddeen Allah yasa Isma'il d'ina ya zama mai nagarta kamarka, kalli yanzu wasu manyan magidan tama basuyi azamar cefenen sallaba amman gashi kai tuni ka gama komai abinka."
kai ya d'an sunkuyar tare da gyara hannun riganshi sannan ya d'ago kanshi tare da yin murmushi cikin girmamawa ya amshi ledan da yake mik'o mishi sannan ya bashi kud'inshi tare da mishi godiya da sallama sannan ya juya ya tafi.
Layin masu yankan kaji yaje nanma ya sashi zabbinshi guda biyar ya bada kudi kana yace musu in sun gyarasu su sa mishi su cikin firij sai k'arfe shida da rabi zaizo ya amsa,
dagana kuma ya sayi jan nama na dubu 3 sannan ya wuce layin masu tattasai, inda yaje ya sayi,
Tattasan, attaruhu, tumatur, al'basa, kabeji, karas, green beans. Da dai sauransu,
sai ya kuma sayi dankalin turawa kond'o d'aya,
daga nan ya wuce shagon da yake saran pure water inda ya samu Rabi'u nan ya sayi katon d'in fanta da Coca-Cola sai rabin ledan molt sannan ya had'a duk su tattasai ya kai aka marked'a mishi sannan ya ware wasu tattasan da taruhu da al'basan kuma wanda ba'a marked'aba ko za'a buk'acesu hakan.
Kana ya harhad'a duk abinda ya sayan a shagonsu Rabi'un dan yasan shi da masu nama suna kai har dare kuma dama ya gayawa Salisu yau sai anyi sallan isha zasu kama hanyar tafiya dukku,
k'arfe uku da rabi dai-dai ya gama duk sayyarshi sannan ya nufi masallaci ganin anata haraman sallan la'asar, baya an idar da sallan ne ya kama hanyan gidansu Ishaq wanda shi kuma tun jiya yake zuba idon ganinshi.
K'arfe hud'u saura mai machine ya sauk'eshi k'ofar gidansu Ishaq dake cikin tudun wadan nan layin fad'a,
yana sauk'a ya nufi cikin gidan,
tare da sallama a ranshi ya shiga.
Mommy ya samu a tsakar gida mai aikinsu tana mata kitso,
tana ganinshi ta fad'ad'a murmushinta tare da bud'a baki cikin d'aga sauti tace.
"Wa alaikassalam lale marhabin da Saifudddeen Ishaq ina kake ga amininka ya iso."
shi kuwa gefenta ya rusuna tare da gaita,
shi kuwa Ishaq da Imaran da Mamansu kusan a tare suka fito,
yana ganin ishaq ya mik'e ya nufi inda yake yayinda shi kuma ishaq k'amshi turaren Saifuddeen d'inne ke masa jagora,
ruggume juna sukayi lokacin da suka had'u sai kuma ishaq ya sakeshi sannan ya ware hannunshi ya manna bisa fuskan Saifuddeen cikin raha yace .
"Iye iyeh my friend watoma kai azumin nan k'ara maka kyau yayi ka ganka kuwa yadda kayi kyau."
dariya sukayi baki d'aya dan ganin yadda Ishaq yakeyin abu kamar mai gani,
shiko Saifuddeen wayar ishaq ya karb'a tare da rubuta mishi.
"To kanari sarkin zance da wanne idon kaga kyan nawa?."
da sauri ya kauce ganin Ishaq d'in zai kai mishi bugu shi kuwa Ishaq cikin fara'arshi yace.
"To kai da wanne kunnen kaji abinda nace?."
murmushi yayi tare da kuma rubuta mishi amsa a wayarshi da duk abinda aka rubuta sai ta fad'i amman shi kad'ai yake gane irin yadda sautin mgnar ke fita dan ko kanaji bazaka ganeba,
"Ni da idanuna na gane abinda kake cewa."
murmushi yayi tare da kamo hannun aminin nashi yace.
To ni kuma da idon zuciyata da tafin hannuna na gane kyawunka."
daga nan kuma sai suka nufi gaban Mama da taketa binsu da ido tana murmushi cikin fara'a tace.
"Yoh ai ba damuwa Saifuddeen ta amininka kake ni kam ko ka kulani."
kanshi ya shafa tare girgiza mata kai kana ya tonk'oshe kai alamun afwan Mama,
daga nan suka gaisa sannan suka shiga parlour Mama nan sukaci gaba da hira suna cikin hira Mama ta fito daga bedroom,
wani d'an k'aramin kwali mai kyau ta mik'owa Saifuddeen, wanda ya zubawa kwalin idanu cike da mmki ya kalli Mama da take ce mishi.
"G...!
By
*GARKUWAR FULANI*
8
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 8*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
_Wannan shafin shima Sadaukarwa ne ga Umar ibrahim Wambai fatan al'khairi da addu'ar samun lagiya a gareka da dukkan masu larurar jinya cuta ko wacce irice._
*Jinjina da fatam alkhairi tare da tarin godiya mai ɗimɓin yawa ga ƙungiyar Nakasassu ta jihar Gombe, joint national association of persons with disabilities. Gombe state chapter. All the best!!!!.👍🏻 (Jonopwd) ina godiya a gareku bisa samun goyon bayanku da bani ƙarfin guiwa da karsashin akan rubuta wannan littafin nawa ,ngd matuƙa da yabawarku gareni*
_Ina mai baku haƙuri masoyana masoyan littafaina, dan Allah duk masu turo min hoton katin mtn da suke saya dan biyan kuɗin karanta littafi pleees ba hoton zaku turo minba numbers ɗin zaku rubuto ku turomin ku ɗan hutar dani aiki, sannan masuyi min transfer ɗin katin etisalat dan Allah ku bari. Katin mtn zaka/ki turo min na 300 kacal a wannan number 09097853276 kuma dashi nakeyin whatsapp, ko kuma ku yuro ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa sai ka/ki turo min shaidar biyan naki ta wannan number dai har lau 09097853276. Dan Allah banda kira bana son kira, sai dai in kayan mata kikeso to nan ki kirani, masoyana na Niger ga number da zakuyiwa magana ita zata gaya muku katin da zaku tura +22788137740 500CF zaku bada. Dan Allah masu taɓayata tsoffin littafaina ku bari,nima bani dashk ku nema a gruops zaku samu_
"Gashi wannan inji Yayanku yace a kawo maka."
ido ya zubawa Mama kamar bai gane me take fad'a mishiba,
Ishaq kuwa hararanshi ya d'anyi da idanunshi da in ka gansu zakayi zaton masu ganine,
mik'a hannunshi yayi da lalube ya amshi kalin wayar da Mama ke mik'awa Saifuddeen tare da cewa.
"Kawo shi nan Mama shi wannan d'an naki fulaku ne ke damunshi."
mik'a mishi tayi sannan ta koma gefe ta zauna tare da jawo wata leda mai d'an girma ta kuma mik'o mushi,
ganin yadda fuskarta yayi alamun bata son ya mata gardama ne yasashi sa hannu,
ya amsa tare da yin murmushi cikin kurma-kurma yayi mata godiya tare sa hannu ya karb'i kwalin wayar da Ishaq ke mik'a mishi wanda SIM card d'inshi na mtn yana ciki da yana cewa.
"Dama ai na san halinka kai komai aka baka sai kace baka so har yau baka d'aukeni d'an uwanka ba,
sai kayi ta nuna min fulaku ni kuma da yake banda zuciya duk abinda na gani a wurin Ummi amsa nakeyi."
amsar woyar yayi tare da yiwa Ishaq d'in alamun to ya isa sarkin k'orafi,
sai ya kuma kalli Mama tare da mata alamun ta mishi godiya a wurin Ya Rabi'u,
sai ya kuma amshi wayar Ishaq ya rubuta sak'on godiya ya turawa Ya Rabi'u babban yayansu Ishaq kenan,
daga nan kuma suka nufi d'akin ishaq nan sukayi ta hira.
Suna cikin hira Saifuddeen ya duba time ganin lokacin salla ya kusane ya sashi mik'ewa ya shiga wonka yana fitowa ya shafa mai tare da canza kaya yasa kayanshi daya cire jiya ya wonke imran kuma ya goge mishi.
Shima ishaq wonkan ya shiga yana fitowa ana kiran sallan magrib,
suna shirin fita imran ya shigo d'auke da tire yana cike da kayan bud'a baki,
dabino sukaci sannan suka sha kankana da abarba daga nan suka fito, suka nufi masallacin fadar masarautan Gombe bayan an idar da salla ne kuma suka dawo gida,
nan sukaci abinci sannan suka zauna suna hira a parlour Mama nan ishaq ya ware mishi d'inkunan da Ya Rabi'u ya musu d'aya riga da wondo ne da babbar riga sai takalmi da hula,
sai d'aya kuma riga da wondo d'inkin zamanin sai boxers and vest guda uku-uku,
sai ledar da Mama ta bashi kuma atampa ce da shadda sunsha d'inki atampar dai-dai Adda Rahma shaddan kuma dai-dai Ummi,
godiya yayi sosai,
daga nan ya had'a komai sannan sukaci gaba da hira,
dan yau ana tsumayin ganin wata.
A dukku kuwa su Warisu da Mudassir kamar kullum sukaje sukaci abinci a gidansu Saifuddeen.
To koda ya gama rarraba ledodinshi kamar kullun ya saro omonshi yayi ta yawatawa har aka k'arfe uku saura kwata bayan ya had'a ribarshi ya wuce ya maida omonshi daya rage,
daga nan ya wuce shagon Alhaji Kabiru wanda ake saida duk wani kayan d'and'anon miya kama daga Magi, raico, onga gishiri kafi Mai, Manja, fulawa, madara, sugar, sufageti, macaroni, indomi. da dai sauransu suna bada sari suna saida kad'an-kad'an kuma suma shine ke saida musu ledodin da suke zubawa kostomominsu kaya in sunyi sayayya.
Sun saba sosai da Alhaji Kabiru dan shima yanada d'anshi kurma shiyasa yake tsananin son Saifuddeen,
yana isa bak'in k'aton shagon nasu ya zaro pepar da biro ya rubuta musu duk abinda yakeso,
nan Alhaji Kabiru ya amsa da kanshi ya ware mishi duk abinda ya lissafa bayan ya gama sasu a leda cikin nitsuwarshi yace.
"Masha Allah Saifuddeen Allah yasa Isma'il d'ina ya zama mai nagarta kamarka, kalli yanzu wasu manyan magidan tama basuyi azamar cefenen sallaba amman gashi kai tuni ka gama komai abinka."
kai ya d'an sunkuyar tare da gyara hannun riganshi sannan ya d'ago kanshi tare da yin murmushi cikin girmamawa ya amshi ledan da yake mik'o mishi sannan ya bashi kud'inshi tare da mishi godiya da sallama sannan ya juya ya tafi.
Layin masu yankan kaji yaje nanma ya sashi zabbinshi guda biyar ya bada kudi kana yace musu in sun gyarasu su sa mishi su cikin firij sai k'arfe shida da rabi zaizo ya amsa,
dagana kuma ya sayi jan nama na dubu 3 sannan ya wuce layin masu tattasai, inda yaje ya sayi,
Tattasan, attaruhu, tumatur, al'basa, kabeji, karas, green beans. Da dai sauransu,
sai ya kuma sayi dankalin turawa kond'o d'aya,
daga nan ya wuce shagon da yake saran pure water inda ya samu Rabi'u nan ya sayi katon d'in fanta da Coca-Cola sai rabin ledan molt sannan ya had'a duk su tattasai ya kai aka marked'a mishi sannan ya ware wasu tattasan da taruhu da al'basan kuma wanda ba'a marked'aba ko za'a buk'acesu hakan.
Kana ya harhad'a duk abinda ya sayan a shagonsu Rabi'un dan yasan shi da masu nama suna kai har dare kuma dama ya gayawa Salisu yau sai anyi sallan isha zasu kama hanyar tafiya dukku,
k'arfe uku da rabi dai-dai ya gama duk sayyarshi sannan ya nufi masallaci ganin anata haraman sallan la'asar, baya an idar da sallan ne ya kama hanyan gidansu Ishaq wanda shi kuma tun jiya yake zuba idon ganinshi.
K'arfe hud'u saura mai machine ya sauk'eshi k'ofar gidansu Ishaq dake cikin tudun wadan nan layin fad'a,
yana sauk'a ya nufi cikin gidan,
tare da sallama a ranshi ya shiga.
Mommy ya samu a tsakar gida mai aikinsu tana mata kitso,
tana ganinshi ta fad'ad'a murmushinta tare da bud'a baki cikin d'aga sauti tace.
"Wa alaikassalam lale marhabin da Saifudddeen Ishaq ina kake ga amininka ya iso."
shi kuwa gefenta ya rusuna tare da gaita,
shi kuwa Ishaq da Imaran da Mamansu kusan a tare suka fito,
yana ganin ishaq ya mik'e ya nufi inda yake yayinda shi kuma ishaq k'amshi turaren Saifuddeen d'inne ke masa jagora,
ruggume juna sukayi lokacin da suka had'u sai kuma ishaq ya sakeshi sannan ya ware hannunshi ya manna bisa fuskan Saifuddeen cikin raha yace .
"Iye iyeh my friend watoma kai azumin nan k'ara maka kyau yayi ka ganka kuwa yadda kayi kyau."
dariya sukayi baki d'aya dan ganin yadda Ishaq yakeyin abu kamar mai gani,
shiko Saifuddeen wayar ishaq ya karb'a tare da rubuta mishi.
"To kanari sarkin zance da wanne idon kaga kyan nawa?."
da sauri ya kauce ganin Ishaq d'in zai kai mishi bugu shi kuwa Ishaq cikin fara'arshi yace.
"To kai da wanne kunnen kaji abinda nace?."
murmushi yayi tare da kuma rubuta mishi amsa a wayarshi da duk abinda aka rubuta sai ta fad'i amman shi kad'ai yake gane irin yadda sautin mgnar ke fita dan ko kanaji bazaka ganeba,
"Ni da idanuna na gane abinda kake cewa."
murmushi yayi tare da kamo hannun aminin nashi yace.
To ni kuma da idon zuciyata da tafin hannuna na gane kyawunka."
daga nan kuma sai suka nufi gaban Mama da taketa binsu da ido tana murmushi cikin fara'a tace.
"Yoh ai ba damuwa Saifuddeen ta amininka kake ni kam ko ka kulani."
kanshi ya shafa tare girgiza mata kai kana ya tonk'oshe kai alamun afwan Mama,
daga nan suka gaisa sannan suka shiga parlour Mama nan sukaci gaba da hira suna cikin hira Mama ta fito daga bedroom,
wani d'an k'aramin kwali mai kyau ta mik'owa Saifuddeen, wanda ya zubawa kwalin idanu cike da mmki ya kalli Mama da take ce mishi.
"G...!
By
*GARKUWAR FULANI*
8
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 8*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
_Wannan shafin shima Sadaukarwa ne ga Umar ibrahim Wambai fatan al'khairi da addu'ar samun lagiya a gareka da dukkan masu larurar jinya cuta ko wacce irice._
*Jinjina da fatam alkhairi tare da tarin godiya mai ɗimɓin yawa ga ƙungiyar Nakasassu ta jihar Gombe, joint national association of persons with disabilities. Gombe state chapter. All the best!!!!.👍🏻 (Jonopwd) ina godiya a gareku bisa samun goyon bayanku da bani ƙarfin guiwa da karsashin akan rubuta wannan littafin nawa ,ngd matuƙa da yabawarku gareni*
_Ina mai baku haƙuri masoyana masoyan littafaina, dan Allah duk masu turo min hoton katin mtn da suke saya dan biyan kuɗin karanta littafi pleees ba hoton zaku turo minba numbers ɗin zaku rubuto ku turomin ku ɗan hutar dani aiki, sannan masuyi min transfer ɗin katin etisalat dan Allah ku bari. Katin mtn zaka/ki turo min na 300 kacal a wannan number 09097853276 kuma dashi nakeyin whatsapp, ko kuma ku yuro ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa sai ka/ki turo min shaidar biyan naki ta wannan number dai har lau 09097853276. Dan Allah banda kira bana son kira, sai dai in kayan mata kikeso to nan ki kirani, masoyana na Niger ga number da zakuyiwa magana ita zata gaya muku katin da zaku tura +22788137740 500CF zaku bada. Dan Allah masu taɓayata tsoffin littafaina ku bari,nima bani dashk ku nema a gruops zaku samu_
"Gashi wannan inji Yayanku yace a kawo maka."
ido ya zubawa Mama kamar bai gane me take fad'a mishiba,
Ishaq kuwa hararanshi ya d'anyi da idanunshi da in ka gansu zakayi zaton masu ganine,
mik'a hannunshi yayi da lalube ya amshi kalin wayar da Mama ke mik'awa Saifuddeen tare da cewa.
"Kawo shi nan Mama shi wannan d'an naki fulaku ne ke damunshi."
mik'a mishi tayi sannan ta koma gefe ta zauna tare da jawo wata leda mai d'an girma ta kuma mik'o mushi,
ganin yadda fuskarta yayi alamun bata son ya mata gardama ne yasashi sa hannu,
ya amsa tare da yin murmushi cikin kurma-kurma yayi mata godiya tare sa hannu ya karb'i kwalin wayar da Ishaq ke mik'a mishi wanda SIM card d'inshi na mtn yana ciki da yana cewa.
"Dama ai na san halinka kai komai aka baka sai kace baka so har yau baka d'aukeni d'an uwanka ba,
sai kayi ta nuna min fulaku ni kuma da yake banda zuciya duk abinda na gani a wurin Ummi amsa nakeyi."
amsar woyar yayi tare da yiwa Ishaq d'in alamun to ya isa sarkin k'orafi,
sai ya kuma kalli Mama tare da mata alamun ta mishi godiya a wurin Ya Rabi'u,
sai ya kuma amshi wayar Ishaq ya rubuta sak'on godiya ya turawa Ya Rabi'u babban yayansu Ishaq kenan,
daga nan kuma suka nufi d'akin ishaq nan sukayi ta hira.
Suna cikin hira Saifuddeen ya duba time ganin lokacin salla ya kusane ya sashi mik'ewa ya shiga wonka yana fitowa ya shafa mai tare da canza kaya yasa kayanshi daya cire jiya ya wonke imran kuma ya goge mishi.
Shima ishaq wonkan ya shiga yana fitowa ana kiran sallan magrib,
suna shirin fita imran ya shigo d'auke da tire yana cike da kayan bud'a baki,
dabino sukaci sannan suka sha kankana da abarba daga nan suka fito, suka nufi masallacin fadar masarautan Gombe bayan an idar da salla ne kuma suka dawo gida,
nan sukaci abinci sannan suka zauna suna hira a parlour Mama nan ishaq ya ware mishi d'inkunan da Ya Rabi'u ya musu d'aya riga da wondo ne da babbar riga sai takalmi da hula,
sai d'aya kuma riga da wondo d'inkin zamanin sai boxers and vest guda uku-uku,
sai ledar da Mama ta bashi kuma atampa ce da shadda sunsha d'inki atampar dai-dai Adda Rahma shaddan kuma dai-dai Ummi,
godiya yayi sosai,
daga nan ya had'a komai sannan sukaci gaba da hira,
dan yau ana tsumayin ganin wata.
A dukku kuwa su Warisu da Mudassir kamar kullum sukaje sukaci abinci a gidansu Saifuddeen.