Sashe 77
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Raveel kuwa tunda ta kwad'a mishi mari ya sunkuyar da kanshi k'asa,
saida yaji ta saki ihunne yayi sauri ya kutsa kai cikin gidan.
Maryam kuwa tana isowa parlour sai ta koma gefe ta zuba musu ido.
Raveel d'inne yayi k'arfin halin kamo hannun ya Ameenu tare da cewa.
"Dan Allah dan darajar iyayenmu kayi hak'uri ya Ameenu mu bita a hankali please kada ka daketa."
Ita kam Zaliha tuni tayi bedroom d'in Maryam a guje tana shiga tayi fad'uwan 'yam bori bisa gadon kana ta saki wani marayan kuka.
Shi kuwa Ya Aminu bisa kujera ya zauna tare da nunawa Raveel kujera alamun ya zauna.
Bayan sun zaunane ya kalli Raveel cikin sanyi da tafasan zuciya yace.
"Raveel kayi hak'uri da abinda Zaleeha tayi maka,
In sha Allah daga kanka bazata sake gigin marin wani d'a namiji ba."
Cikin sanyin Raveel yace.
"Ba komai ya Aminu, Allah ya tabbatar mana da al'khairi."
Amin Amin yace kana yayiwa Raveel rakiya har bakin gate.
Ita kuwa Maryam ganin mijin nata ya fitane yasa ta juya a hankali tabi bayan k'anwar tata,
tana shiga ta maida k'ofar ta rufe.
Da sauri ta haura kan gadon cikin tausayawa tace.
"Zaleeha, kiyi hak'uri kiyi shiru kukan ya isa haka please kinga ga Ayman ma ya fara kuka,
Gaya min make faruwa?."
A hankali ta mirgino tare da kife kanta bisa cinyar maryam cikin tsananin kuka tace.
"Raveel ne ya tura iyayensa wurin Baba malam wai suna neman izinin zance.
yau tunda safe ya aika ya Habu ya kirani ina shiga ya hauni da fada.
Wai zan maidashi mutumin banza ya za'ayi inyi ta turo mishi dattawan mutane.
A karshe yace dole cikin manema in fidda goni ko shi yamin zabi, yace min wai karfa inga yayi shiru yana sane k'a'idar da ya bani saura wata d'aya".
Numfashi ta sauk'e a hankali tace.
"To ke Zaliha auren ne bakya so?."
cikin shesshek'a da miryar tausayi tace.
"A a ni bance bana son aureba."
Cikin kula tace.
"To bakida masoya ne?."
Still hawaye na zuba tace.
"Ina dasu amman ni bana sonsu."
Gyara zamanta tayi tare da cewa.
"To wa kike so?."
hannunta tasa duka biyu ta matse kanta da k'arfi cikin rauni da tashin hankalin dan a duniya tasan wannan amsar itace tafi komai wahal da ita cikin muryar kuka tace.
"Adda Maryam ya kike min tambaya kamar bakisan komai a kanshi ba?."
cikin sin cire mata wannan tunanu Maryam tace.
"Shi waye ɗin kenan?."
Kai tajujjuya kana tace.
"Shi nakeso! Shine farin cikin rayuwata, in dai ba shine yace baya sonaba to bazan auri kowaba, ya sadaukar da rayuwarshi a kaina, ya kareni a lokacin da nafi tsananin buk'atar neman kariya,
Ya zama garkuwata ya tsare min kimata ya bada ranshi da lfyarshi a kaina, ina sonshi."
Sai kuma ta tashi zaune ta rik'o hannayen yayar tata cikin zubda k'walla murya na rawa tace.
"Ina sonshi, wlh ina sonshi bazan iya son wani d'an namiji ba in ba shiba."
Cikin kad'uwa maryam tace.
"Wai waye ne?."
Da k'arfi tace.
"Ban saniba."
Cikin mmki Maryam ta zaro ido woje kana tace.
"Me sunanshi? Ina gidansu yake? Me sana'arsa?."
Nanma kuka tasa tare da cewa.
"I don't know."
Zuwa yanzu abin ya fara bawa Maryam tsoro cikin tsoro tace.
"To ina yake?."
Da k'arfi tasa hannunta tana dukan kanta tare da cewa.
"Ban sanshi ba, bai sanniba bansan ina yakeba bansan sunanshi ba.
daga sau d'ayan dai dana tab'a ganinshi nanma gabanin magriba ne, to ban sake ganinshi ba."
Nan ta k'ara bawa Maryam labarin had'uwarta da Dalla da yadda Saifuddeen ya taimaketa, dan ganin yadda Maryam ta nuna mata kamar bata gane waye take nufi ba, ta k'arishe mgnar cikin tsananin kuka tace.
"Bansan ina zan sake ganinshi ba, ina sonshi, shine nakeso ya zama mijina wlh in ban aureshi ba bazanyi aureba,
wlh in ban sake ganinshi ba zan haukace."
Tsorone mai tsanani ya rufe Maryam,
cikin zubda hawaye muryarta a sanyaye tace.
"Innalillahi wa Inna'ilaihi rajiun, Zaliha ko dai kinyi gamone, kodai al'janine ba mutun ba?."
da sauri ta durk'usa gaban yayartata cikin kid'ima da jujjuya Kai tace.
"Mutum ne shi kamar ni, wlh ba al'jani bane shima d'an adam ne,
na tabbata da al'janine da ya sake zuwamin koda a mafarki ne.
Ni tsorona bansan wani hali yake cikiba, yana lfy ko sun illatashi."
Wani nannauyan ajiyan zuciya Maryam ta sauk'e sannan tasa hannu ta share hawayenta kana ta sharewa Zaliha nata cikin fuskantarta da kyau a hankali tace.
"Wannan zancen naki ba'ak'i ce dashi gaibuba,
domin tatsuniya ce mai zaman kanta, zancene da hankalin bazai kamaba,
Zaliha ki yarda al'janine ya taimaka miki, in ko mutunne to ya mutu."
Wani irin zabura tayi tare da rushewa da kuka tana jujjuya kai tare da yarfa hannu take cewa.
"Bai mutuba yana raye mutun ne ba aljanba ki gane mana ina jinshi a cikin duk wani bugun da zuciyata keyi."
Ganin yadda ta gigicene yasa Maryam cewa.
"Na game mutum ne kuma yana raye."
Jin haka sai ta koma ta konta rubdaciki tana mai ci gaba da kuka.
Ita kuwa Maryam da sauri ta d'iro daga kan gadon ganin Ya Ameenun yana tsaye a bakin k'ofa bisa dukkan alamu yaji duk batun da sukayi.
tana isa inda yake kawai sai ta fad'a jikinshi tare da sakin sassanyan kuka.
Da sauri ya tallabota dan a duniya Ameenu duk zafinsa baya son abinda zai tab'a mishi salihar matarshi mai tarin hak'uri da biyeyya.
parlour ya fito da ita inda ya ruggumeta da kyau a jikinshi,
jin haka yasa rauninta k'aruwa cikin rawar murya take cewa.
"Shi kenan Ya Ameenu Zaleeha tayi gamo, al'jani ya shiga jikinta.
Zai haukata min k'anwata ya Ameenu kuyi mata Ruqyah kada ya haukatata."
ganin sosai take kukanne ya sashi d'ago kanta bakinsu ya had'e wuri d'aya wani irin zazzafan kiss yake mata wanda dole yasa tayi shiru, har saida yaga ta nitsu kana ya jawota suka zauna kan kujera,
tafin hannunshi yasa yana share mata hawaye tare da cewa.
"Am so sorry my happiness kiyi shiru ba abinda zai sameta sai al'khairi ki daina kuka,
zan mata duk abinda kike so kinji ko Ummu Ayman?."
Kanta ta gyad'a mishi alamun gamsuwa, duk da haka bai bartaba har saida ya sama mata cikekkiyar nitsuwa.
Ita kuwa Zaleeha tuni wani baccin kuka ya kwasheta.
Shi kuwa Raveel koda yaje office ya kasa samun sukuni.
Sai sak'onnin ban hak'uri yaketa tura mata.
Abuja
Amina ce ke zaune bisa sallayarta,
yayinda ta bud'e hannayenta sama Cikin sanyin lafazi take cewa.
"Ya haiyu ya k'aiyum ya ubangijin sammai da k'asai ya rabbil izzati kaine mai rayawa mai kashewa ya Allah ka raya min wannan bawa naka Saifuddeen.
Ya Allah ka bashi lfy, Allah ka jib'anci lamuranshi ka sanya salama da farin ciki a rayuwarshi ya Allah ka cika mishi dukkan buk'atunshi na al'khairi."
A hankali ta shafa addu'ar tare da zamewa ta kwanta a nan bisa sallayar,
tare da jawo wayarta hotonshi dake bisa fuskar wayarta ta zubawa ido. murmushin da yake a hoton sai takega kamar ita yakeyiwa.
Indian Mumbai
A guje nurses da Doctors suka shigo d'akinda Saifuddeen ke ciki sabida ihu da kururuwan da Hayatuddeen keyi.
Ihu yakeyi yana tsalle tamkar yaro kana yana yarfa hannu yana cewa.
"Wayyo Allah na yau farin ciki zai kasheni,
Wayyo ni Hayatuddeen waye zai tayani farin ciki,
Wayyo Ummi na yau ga Hamma Saifuddeen d'ina a zaune da k'ugunshi, ya tashi ya zauna da kanshi ba tare da taimakon kowaba.
Wayyo Adda Rahma Raihana, Raliya d'an uwanmu ya fara zama da kanshi.
Ya Adnan ya Ahmad Bappa Ali ina kuke?."
sai kuma yayi kan Hamman nashi wanda tuni likitoci sun zagayeshi,
yayinda suma duk fuskokinsu ke cike da farin ciki.
Wani Irin sassanyan rugguma yayiwa Saifuddeen sai kuma ya fashe da wani irin kuka wanda daga kaji kasan daga cikin zuciyarshi kukan ke fitowa.
Ganin haka yasa Saifuddeen ruggumeshi da kyau tare da d'an bubbuga bayanshi kana ya d'agoshi ya share mishi hawayenshi tare da mishi alamun.
Shin irin godiyar daya dace yayi Allah kenan?.
gane hakan ya sashi yin sujhadar shukur da sauri,
wanda kafin ya d'ago daga sujjadar tuni an tura gadon da Saifuddeen ke kai an shiga dashi wani d'aki na musamman.
Ummi kuwa duk abinda Hayatuddeen keyi da fad'i tanaji,
Lokaci d'aya hawayen farin ciki ya rufeta,
cikin tsananin happy ta sanarwa Raliyya abinda taji,
ruggume juna sukayi dan tsananin farin ciki,
daga nan Raliya ta fita a guje side d'insu ta nufa,
tana shiga ta samu ya Ahmad d'in baya parlour da gudu ta kutsa kai bedroom nanma baya ciki.
Jin motsin ruwane yasa tayi saurin bud'e k'ofar bathroom d'in,
hangoshi tayi k'asan shower yana tsaye ba komai a jikinshi,
cikin wani irin tsalle ta fad'a jikinshi dan ta mance cewa wai gudunshi tayi.
Da sauri ya ruggumota ganin yadda taketa tsalle kawai sai yaga ta fara mammanna mishi kiss tako ina najikinshi.
Sam ta kasa cewa komai ganin haka sai ya fara zame mata kayan jikinta,
bata bi ta kanshi ba bare ta hanashi sai ma k'ara mak'aleshi tayi cikin fizgo mgna tace.
"Al'bishirinka Ya Ahmad."
cilla rigarta gefe yayi tare da had'e jikinsu wuri d'aya kana yace.
"Goro fari k'al."
kiss ta manna mishi a goshi sannan tace.
"Jikin Hamma Saifuddeen da sauk'i ya shida kanshi ya tashi zaune ba taimakon kowa."
Wata iriyar amintacciyar rugguma Ahmad yayi mata tare da giggicewa gaba d'aya ya abka mata,
bata da zabi dole ta karb'eshi a yadda ya zo mata,
mgna d'aya sukayi ta maimaitawa juna,
"Hamma Saifuddeen ya fara workewa yana zama da kanshi."
shi kuma sai yace.
"Alhamdulillahi ya Allah mun gode maka ka nuna mana ranar da zai kuna tsayuwa da sawunshi."
A haka dai sukayi ta kabta nanayensu.
Ummi kuwa wayarta ta d'auka ta gaya dukkan 'yan uwa da abokan arziki.
Adda Rahma kam kawai sai taje gaban surkarta tana kuka tana sanar da ita, cikin kula tace.
"A a Rahma to ai wannan abin farin cikine bana kukaba Allah zamu godewa."
A gefen Raihana ma haka abin yake,
dan ita cewa ma tayi dole Saminu ya kawota gida gombe.
Su Salisu, Mudassir, Warisu, da Bappa Ali kuwa duk Ahmad ya sanar dasu.
saida yaji ta saki ihunne yayi sauri ya kutsa kai cikin gidan.
Maryam kuwa tana isowa parlour sai ta koma gefe ta zuba musu ido.
Raveel d'inne yayi k'arfin halin kamo hannun ya Ameenu tare da cewa.
"Dan Allah dan darajar iyayenmu kayi hak'uri ya Ameenu mu bita a hankali please kada ka daketa."
Ita kam Zaliha tuni tayi bedroom d'in Maryam a guje tana shiga tayi fad'uwan 'yam bori bisa gadon kana ta saki wani marayan kuka.
Shi kuwa Ya Aminu bisa kujera ya zauna tare da nunawa Raveel kujera alamun ya zauna.
Bayan sun zaunane ya kalli Raveel cikin sanyi da tafasan zuciya yace.
"Raveel kayi hak'uri da abinda Zaleeha tayi maka,
In sha Allah daga kanka bazata sake gigin marin wani d'a namiji ba."
Cikin sanyin Raveel yace.
"Ba komai ya Aminu, Allah ya tabbatar mana da al'khairi."
Amin Amin yace kana yayiwa Raveel rakiya har bakin gate.
Ita kuwa Maryam ganin mijin nata ya fitane yasa ta juya a hankali tabi bayan k'anwar tata,
tana shiga ta maida k'ofar ta rufe.
Da sauri ta haura kan gadon cikin tausayawa tace.
"Zaleeha, kiyi hak'uri kiyi shiru kukan ya isa haka please kinga ga Ayman ma ya fara kuka,
Gaya min make faruwa?."
A hankali ta mirgino tare da kife kanta bisa cinyar maryam cikin tsananin kuka tace.
"Raveel ne ya tura iyayensa wurin Baba malam wai suna neman izinin zance.
yau tunda safe ya aika ya Habu ya kirani ina shiga ya hauni da fada.
Wai zan maidashi mutumin banza ya za'ayi inyi ta turo mishi dattawan mutane.
A karshe yace dole cikin manema in fidda goni ko shi yamin zabi, yace min wai karfa inga yayi shiru yana sane k'a'idar da ya bani saura wata d'aya".
Numfashi ta sauk'e a hankali tace.
"To ke Zaliha auren ne bakya so?."
cikin shesshek'a da miryar tausayi tace.
"A a ni bance bana son aureba."
Cikin kula tace.
"To bakida masoya ne?."
Still hawaye na zuba tace.
"Ina dasu amman ni bana sonsu."
Gyara zamanta tayi tare da cewa.
"To wa kike so?."
hannunta tasa duka biyu ta matse kanta da k'arfi cikin rauni da tashin hankalin dan a duniya tasan wannan amsar itace tafi komai wahal da ita cikin muryar kuka tace.
"Adda Maryam ya kike min tambaya kamar bakisan komai a kanshi ba?."
cikin sin cire mata wannan tunanu Maryam tace.
"Shi waye ɗin kenan?."
Kai tajujjuya kana tace.
"Shi nakeso! Shine farin cikin rayuwata, in dai ba shine yace baya sonaba to bazan auri kowaba, ya sadaukar da rayuwarshi a kaina, ya kareni a lokacin da nafi tsananin buk'atar neman kariya,
Ya zama garkuwata ya tsare min kimata ya bada ranshi da lfyarshi a kaina, ina sonshi."
Sai kuma ta tashi zaune ta rik'o hannayen yayar tata cikin zubda k'walla murya na rawa tace.
"Ina sonshi, wlh ina sonshi bazan iya son wani d'an namiji ba in ba shiba."
Cikin kad'uwa maryam tace.
"Wai waye ne?."
Da k'arfi tace.
"Ban saniba."
Cikin mmki Maryam ta zaro ido woje kana tace.
"Me sunanshi? Ina gidansu yake? Me sana'arsa?."
Nanma kuka tasa tare da cewa.
"I don't know."
Zuwa yanzu abin ya fara bawa Maryam tsoro cikin tsoro tace.
"To ina yake?."
Da k'arfi tasa hannunta tana dukan kanta tare da cewa.
"Ban sanshi ba, bai sanniba bansan ina yakeba bansan sunanshi ba.
daga sau d'ayan dai dana tab'a ganinshi nanma gabanin magriba ne, to ban sake ganinshi ba."
Nan ta k'ara bawa Maryam labarin had'uwarta da Dalla da yadda Saifuddeen ya taimaketa, dan ganin yadda Maryam ta nuna mata kamar bata gane waye take nufi ba, ta k'arishe mgnar cikin tsananin kuka tace.
"Bansan ina zan sake ganinshi ba, ina sonshi, shine nakeso ya zama mijina wlh in ban aureshi ba bazanyi aureba,
wlh in ban sake ganinshi ba zan haukace."
Tsorone mai tsanani ya rufe Maryam,
cikin zubda hawaye muryarta a sanyaye tace.
"Innalillahi wa Inna'ilaihi rajiun, Zaliha ko dai kinyi gamone, kodai al'janine ba mutun ba?."
da sauri ta durk'usa gaban yayartata cikin kid'ima da jujjuya Kai tace.
"Mutum ne shi kamar ni, wlh ba al'jani bane shima d'an adam ne,
na tabbata da al'janine da ya sake zuwamin koda a mafarki ne.
Ni tsorona bansan wani hali yake cikiba, yana lfy ko sun illatashi."
Wani nannauyan ajiyan zuciya Maryam ta sauk'e sannan tasa hannu ta share hawayenta kana ta sharewa Zaliha nata cikin fuskantarta da kyau a hankali tace.
"Wannan zancen naki ba'ak'i ce dashi gaibuba,
domin tatsuniya ce mai zaman kanta, zancene da hankalin bazai kamaba,
Zaliha ki yarda al'janine ya taimaka miki, in ko mutunne to ya mutu."
Wani irin zabura tayi tare da rushewa da kuka tana jujjuya kai tare da yarfa hannu take cewa.
"Bai mutuba yana raye mutun ne ba aljanba ki gane mana ina jinshi a cikin duk wani bugun da zuciyata keyi."
Ganin yadda ta gigicene yasa Maryam cewa.
"Na game mutum ne kuma yana raye."
Jin haka sai ta koma ta konta rubdaciki tana mai ci gaba da kuka.
Ita kuwa Maryam da sauri ta d'iro daga kan gadon ganin Ya Ameenun yana tsaye a bakin k'ofa bisa dukkan alamu yaji duk batun da sukayi.
tana isa inda yake kawai sai ta fad'a jikinshi tare da sakin sassanyan kuka.
Da sauri ya tallabota dan a duniya Ameenu duk zafinsa baya son abinda zai tab'a mishi salihar matarshi mai tarin hak'uri da biyeyya.
parlour ya fito da ita inda ya ruggumeta da kyau a jikinshi,
jin haka yasa rauninta k'aruwa cikin rawar murya take cewa.
"Shi kenan Ya Ameenu Zaleeha tayi gamo, al'jani ya shiga jikinta.
Zai haukata min k'anwata ya Ameenu kuyi mata Ruqyah kada ya haukatata."
ganin sosai take kukanne ya sashi d'ago kanta bakinsu ya had'e wuri d'aya wani irin zazzafan kiss yake mata wanda dole yasa tayi shiru, har saida yaga ta nitsu kana ya jawota suka zauna kan kujera,
tafin hannunshi yasa yana share mata hawaye tare da cewa.
"Am so sorry my happiness kiyi shiru ba abinda zai sameta sai al'khairi ki daina kuka,
zan mata duk abinda kike so kinji ko Ummu Ayman?."
Kanta ta gyad'a mishi alamun gamsuwa, duk da haka bai bartaba har saida ya sama mata cikekkiyar nitsuwa.
Ita kuwa Zaleeha tuni wani baccin kuka ya kwasheta.
Shi kuwa Raveel koda yaje office ya kasa samun sukuni.
Sai sak'onnin ban hak'uri yaketa tura mata.
Abuja
Amina ce ke zaune bisa sallayarta,
yayinda ta bud'e hannayenta sama Cikin sanyin lafazi take cewa.
"Ya haiyu ya k'aiyum ya ubangijin sammai da k'asai ya rabbil izzati kaine mai rayawa mai kashewa ya Allah ka raya min wannan bawa naka Saifuddeen.
Ya Allah ka bashi lfy, Allah ka jib'anci lamuranshi ka sanya salama da farin ciki a rayuwarshi ya Allah ka cika mishi dukkan buk'atunshi na al'khairi."
A hankali ta shafa addu'ar tare da zamewa ta kwanta a nan bisa sallayar,
tare da jawo wayarta hotonshi dake bisa fuskar wayarta ta zubawa ido. murmushin da yake a hoton sai takega kamar ita yakeyiwa.
Indian Mumbai
A guje nurses da Doctors suka shigo d'akinda Saifuddeen ke ciki sabida ihu da kururuwan da Hayatuddeen keyi.
Ihu yakeyi yana tsalle tamkar yaro kana yana yarfa hannu yana cewa.
"Wayyo Allah na yau farin ciki zai kasheni,
Wayyo ni Hayatuddeen waye zai tayani farin ciki,
Wayyo Ummi na yau ga Hamma Saifuddeen d'ina a zaune da k'ugunshi, ya tashi ya zauna da kanshi ba tare da taimakon kowaba.
Wayyo Adda Rahma Raihana, Raliya d'an uwanmu ya fara zama da kanshi.
Ya Adnan ya Ahmad Bappa Ali ina kuke?."
sai kuma yayi kan Hamman nashi wanda tuni likitoci sun zagayeshi,
yayinda suma duk fuskokinsu ke cike da farin ciki.
Wani Irin sassanyan rugguma yayiwa Saifuddeen sai kuma ya fashe da wani irin kuka wanda daga kaji kasan daga cikin zuciyarshi kukan ke fitowa.
Ganin haka yasa Saifuddeen ruggumeshi da kyau tare da d'an bubbuga bayanshi kana ya d'agoshi ya share mishi hawayenshi tare da mishi alamun.
Shin irin godiyar daya dace yayi Allah kenan?.
gane hakan ya sashi yin sujhadar shukur da sauri,
wanda kafin ya d'ago daga sujjadar tuni an tura gadon da Saifuddeen ke kai an shiga dashi wani d'aki na musamman.
Ummi kuwa duk abinda Hayatuddeen keyi da fad'i tanaji,
Lokaci d'aya hawayen farin ciki ya rufeta,
cikin tsananin happy ta sanarwa Raliyya abinda taji,
ruggume juna sukayi dan tsananin farin ciki,
daga nan Raliya ta fita a guje side d'insu ta nufa,
tana shiga ta samu ya Ahmad d'in baya parlour da gudu ta kutsa kai bedroom nanma baya ciki.
Jin motsin ruwane yasa tayi saurin bud'e k'ofar bathroom d'in,
hangoshi tayi k'asan shower yana tsaye ba komai a jikinshi,
cikin wani irin tsalle ta fad'a jikinshi dan ta mance cewa wai gudunshi tayi.
Da sauri ya ruggumota ganin yadda taketa tsalle kawai sai yaga ta fara mammanna mishi kiss tako ina najikinshi.
Sam ta kasa cewa komai ganin haka sai ya fara zame mata kayan jikinta,
bata bi ta kanshi ba bare ta hanashi sai ma k'ara mak'aleshi tayi cikin fizgo mgna tace.
"Al'bishirinka Ya Ahmad."
cilla rigarta gefe yayi tare da had'e jikinsu wuri d'aya kana yace.
"Goro fari k'al."
kiss ta manna mishi a goshi sannan tace.
"Jikin Hamma Saifuddeen da sauk'i ya shida kanshi ya tashi zaune ba taimakon kowa."
Wata iriyar amintacciyar rugguma Ahmad yayi mata tare da giggicewa gaba d'aya ya abka mata,
bata da zabi dole ta karb'eshi a yadda ya zo mata,
mgna d'aya sukayi ta maimaitawa juna,
"Hamma Saifuddeen ya fara workewa yana zama da kanshi."
shi kuma sai yace.
"Alhamdulillahi ya Allah mun gode maka ka nuna mana ranar da zai kuna tsayuwa da sawunshi."
A haka dai sukayi ta kabta nanayensu.
Ummi kuwa wayarta ta d'auka ta gaya dukkan 'yan uwa da abokan arziki.
Adda Rahma kam kawai sai taje gaban surkarta tana kuka tana sanar da ita, cikin kula tace.
"A a Rahma to ai wannan abin farin cikine bana kukaba Allah zamu godewa."
A gefen Raihana ma haka abin yake,
dan ita cewa ma tayi dole Saminu ya kawota gida gombe.
Su Salisu, Mudassir, Warisu, da Bappa Ali kuwa duk Ahmad ya sanar dasu.