Sashe 13
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Yau tunda yaje yaketa sintirin saida ruwanshi dasu Fantan har sai bayan la'asar ya je shagonsu Hisham da niyan zai tattauna dashi sai ya samu tuni ya tafi gida ya kai cefenen dare.
haka yasa ya wuce shagonsu Jabeer yana zuwa suka zauna dan lokacin mata sun d'an tsagaita,
rubutu yayi na neman shawarar sana'ar da zai fara saida ya gama rubutawa kana ya mik'awa Jabeer takardar dai-dai lokacin daya karb'a dai-dai lokacin kuma baba Bello ya iso wannan dottijon.
karantawa Jabber yayi kana ya kalli Saifuddeen da yake mik'o mishi banduran ledodin daya amsa a hannun Dottijon cikin yanayinshi na wasa da dariya yace.
"Yoh balarabe ga sana'ar da zakayi a hannunka ai kawai ka fara saida leda, gashi dama Baba bello bai saida leda a Ramadan kaga sai ka karb'eshi bayan salla in an dawo sai ka bashi sana'arshi kai ka koma pure waternka ko?."
Ido suka zuba mishi baki d'aya,
shi kuwa ba tare daya bi ta kan kallon da duk suke mishiba ya matso kusa da Dottijon cikin nitsuwa yace.
"Kana ji ko baba Bello shi Balarabe ruwa yake sedawa da kayan zak'i irin namu na yara,
to kuma kaga ga Ramadan yana zuwa to duk abin saidawa in dai na cine cinikinshi ya mutu da rana sai dai in darene,
to kaga ita kuma kasuwa da rana takeci,
shi kuma d'an dukkune kullum zuwa yake da safe bayan sallan isha yake komawa,
toh shine yaketa nazarin wani abu zai fara saidawa cikin azumin,
da yayi zaton zaike saida dabino da kwakwa to gsky itana sana'ar yawace kuma kada yaje garin talla ya tsalli dabino ya afa a baki."
Ya k'arishe mgnar cikin tsokana da wasa,
k'eyarshi Saifuddeen ya bugi tare zare mishi irin yadda akewa yara masu surutu,
dariya sukayi baki d'aya ganin yadda Jabeer ya tura baki tare da cewa.
"To nayi shiru."
shi kuwa ogansu Jabeer gyara zama yayi tare da cewa.
"Baba Bello bananma da wuri zaka shiga itikafin ne?."
cikin kauda zancen Dottijon yace.
"Waya ce da kai itikafi nake shiga,
kawai dai ina ajiye kasuwancin ne da ramadan sabida tsufa yazo kuma azumi na wahaldani."
Murmushi kawai Alhaji Adamu yayi sabida yasa Baba Bello itikafi yake shiga shi kuma yana b'oyewa sabida gudun riya,
shiyasa yake ce musu hutun Ramadan kawai yakeyi.
shiko Dottijon cikin kulla ya kalli Saifuddeen kana murya a tausashe yace.
"Yaro na zaka iya yawon bin shago layi-layi kana raba musu ledodi, suna yi maka biyan bashin daddawan k'auye?."
murmushi yayi tare da gyad'a mishi kai alamar zai iya.
Shiko Dottijon sauk'owa yayi daga kan keken nashi kana ya zauna kusa da Saifuddeen cikin tattausan lafazi yace.
"Kullum in azumi yayi ina barin kasuwa duk costomomina sai dai suyi ta kame-kamen sayan leda wurin wasu,
anayin salla kuma da kwana biyu zan dawo to duk masu kawo musu sai su bari inci gaba da kawo musu kamar kullum to amman tunda gashi bana Allah ya had'ani da kai, in dai ka amince kayi al'k'awarin rik'e amana to zan kaika wurin babban dilanmu da yake bamu talla bisa farashi mai sauk'i,
zaike baka kaya ba tare da ka bashi ko asiba,
sai kai kuma ka tallata ka d'ora ribarka,
misali yau in ka kawo bazasu baka kud'iba sai gobe in ka kawo musu sai su baka kud'in na yau,
na yau kuma sai ka kawo musu na gobe.
to wasu ba ruwansu kana kai musu zasu biyaka,
wasu kuma dole sai goben,
to anan amanar da nakeso ka rik'e zan kaika gaban dilanmu amatsayin kai jikanane dan in baisan wani nakaba bazai bakaba,
in ya amince zai baka kuma zan had'aka da costomomina baki d'aya, nasan duk masu amana da gsky ne, suma kuma zan basu amanarka kada su ganka bakaji su cuceka, nasan zaka iya kasuwancin kam tunda kayi karatu zaku rink'ayin komai a rubuce."
cikin lumshe ido Saifuddeen ya had'e hannunsu wuri d'aya kana ya jinjina mishi sannan ya zaro biro ya fara rubutu a tafin hannunshi saida ya gama kana ya nunawa Jabeer nan Jabeer ya fara karanta abinda ya rubutan.
"In sha Allah Baba bazan kasance mara gsky ba a cikin had'akarmu,
nayi alk'awarin rik'oda gsky da amana bazan kunyataka ba,
ga Oga Adamu da abokina Jabeer da sauran maikatan shagon nan su zama shaida, Allah kuma ya bamu sa'a ngd matuk'a Allah ya k'ara lfy da wadata."
Murmushi sukayi baki d'aya,
daga nan Dottijon nan yayi gaba Saifuddeen na binshi a baya har shagon babban dilansu na leda,
nan ya gabatar dashi ga Alhaji Babayo,
ba wani dogon bincike Alhaji Babayo ya aminta da Saifuddeen sabida ganin Baba Bello ne ya kawoshi Dottijon da sunfi shekaru 20 suna tare a harkar leda.
shi kuwa Baba Bello ya musu bayanin Saifuddeen kurmane amman yana gane duk abinda ake cewa in yana ganin bakin mutun.
an yarda tuni an rattaba sunan Saifuddeen a jerin sunayen masu amsar talla,
yasa hannu shaidu sun saka hannu.
daga nan suka juya Baba Bello ya tasa Saifuddeen a gaba duk inda yasan yana kai ledodi saida ya nuna musu Saifuddeen yana ce musu jikanshi ne, kuma shi zai rink'a kawo musu Leda cikin azumi har sai bayan sallah shi zai dawo,
to dama duk kostomominshi sun san da baya kawo musu leda cikin azumi to sai sukaji dad'in wannan ci gaban koda sukaje shagon Alhaji Ibrahim baban Hisham yaji dad'in abun sosai ya sanya albarka haka dai duk wunin wannan ranar kam sukayi shi ranar bag d'in pure water takwas kawai ya saida sai dai ya saida su Coca-Cola sosai.
Sun bari akan sai ana gobe azumi zai fara tallan ledan tunda ranar Baba Bello zayi zuwan k'arshe sai kuma bayan sallah.
Anayin sallan magrib Salisu yazo ya d'aukeshi kamar kullum,
yau wurin mai shayi sukaje kwai aka soya musu da indomi kana sai ruwan tea,
bayan sunci ne sukayi sallan isha, kana suka kama hanyar Dukku.
Koda suka isa Saifuddeen na sauk'a Salisu ya zaro dubu biyar d'in balance ya mik'ashi,
amsa yayi kana ya zare 2k ya bashi yace yaje ya sayawa Mamanshi sugar da Lipton baiso karb'a amman dole ya amsa,
shi kuwa Saifuddeen yana shiga gida kai tsaye d'akin Umminshi ya shiga inda ya sameta ita da Aunty Nina suna hirarsu.
Bayan sun gaisane ya mik'e tare da yiwa Ummi alamun bari yaje yayi wonka.
To tace mishi kana sukaci gaba da hira,
shi kuwa solle jikinshi yayi suk'al kana ya shafa mai tare da fesa turare,
canza kaya yayi sannan ya nufi tsank'aya wurin Bappa Ali duk da yasan yau al'hamis ne ba karatu so ya kuma san canne wurin zaman Bappa Ali ko yaushe bayan sun gaisane ya mishi bayanin canjin sana'ar da zaiyi da tsarin kasuwancin da dokokinshi,
sosai Bappa Ali ya gamsu da hakan addu'a yayi da fatan al'khairi.
Koda ya tashi tafiya sai ya kwaso cinikinsa na yau duka da riban da jarin duk dubu 3 ne.
sai ya kuma zaro da sauran dubu ukun balance d'in ya had'asu inda suka bashi dubu shida kenan.
Cikin nitsuwa ya mik'awa bappa Ali.
Cikin tsuke fuska da fad'a bappa Ali yace.
"Me zanyi dasu? shin ba nacema Ka dena bani kud'iba in dai ban bakaba to ai baici ka baniba,
fatana Allah ya bud'a maka yadda zakayi kaci gaba da rik'e marayun k'annenka dani bappanku na gaza rik'ewa."
da sauri ya girgiza mishi kai kana ya rubuta mishi.
"Dan Allah Bappa Ali ka amshi kud'innan in dai ba rainawa kayiba, meyasa kullum in na baka abu baka amsa,
to in ban makaba waye zanyiwa kainefa uba a garemu ka sanya al'barka a lamarinmu in bani dashi zan baka ne?."
to ganin ranshi ya b'acine yasa Bappa Alin amsar tare da samishi al'barka.
Har ya tashi sai ya kuma zauna ganin Bappa Alin ya rik'o hannunshi bayan ya zaunane yake shaida mishi wannan mutumin daya kad'e Nuruddeen ya kawo musu kayan azumin.
Kama daga shinkafa, taliya, doya, Couscous, indomi, mai, manja, magi, gishiri, onga, kwai madara da Milo sugar Lipton, da kud'i 10k.
wani irin tsuke fuska Saifuddeen yayi tare had'e rai sai ya kuma yiwa bappa Ali alamun tambayar sun karb'ane?.
kai bappa Ali ya gyad'a mishi alamar eh sun amshi kayan,
cikin takaici ya...
By
*GARKUWAR FULANI*
8/
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 5*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
_Wannan shafi gaba ɗayanshi tukuicine da saudaukarwa ga Umar ibrahim Wambai, Allau rabbi ya baka lafiya!_
Free page🤝🏻
haka yasa ya wuce shagonsu Jabeer yana zuwa suka zauna dan lokacin mata sun d'an tsagaita,
rubutu yayi na neman shawarar sana'ar da zai fara saida ya gama rubutawa kana ya mik'awa Jabeer takardar dai-dai lokacin daya karb'a dai-dai lokacin kuma baba Bello ya iso wannan dottijon.
karantawa Jabber yayi kana ya kalli Saifuddeen da yake mik'o mishi banduran ledodin daya amsa a hannun Dottijon cikin yanayinshi na wasa da dariya yace.
"Yoh balarabe ga sana'ar da zakayi a hannunka ai kawai ka fara saida leda, gashi dama Baba bello bai saida leda a Ramadan kaga sai ka karb'eshi bayan salla in an dawo sai ka bashi sana'arshi kai ka koma pure waternka ko?."
Ido suka zuba mishi baki d'aya,
shi kuwa ba tare daya bi ta kan kallon da duk suke mishiba ya matso kusa da Dottijon cikin nitsuwa yace.
"Kana ji ko baba Bello shi Balarabe ruwa yake sedawa da kayan zak'i irin namu na yara,
to kuma kaga ga Ramadan yana zuwa to duk abin saidawa in dai na cine cinikinshi ya mutu da rana sai dai in darene,
to kaga ita kuma kasuwa da rana takeci,
shi kuma d'an dukkune kullum zuwa yake da safe bayan sallan isha yake komawa,
toh shine yaketa nazarin wani abu zai fara saidawa cikin azumin,
da yayi zaton zaike saida dabino da kwakwa to gsky itana sana'ar yawace kuma kada yaje garin talla ya tsalli dabino ya afa a baki."
Ya k'arishe mgnar cikin tsokana da wasa,
k'eyarshi Saifuddeen ya bugi tare zare mishi irin yadda akewa yara masu surutu,
dariya sukayi baki d'aya ganin yadda Jabeer ya tura baki tare da cewa.
"To nayi shiru."
shi kuwa ogansu Jabeer gyara zama yayi tare da cewa.
"Baba Bello bananma da wuri zaka shiga itikafin ne?."
cikin kauda zancen Dottijon yace.
"Waya ce da kai itikafi nake shiga,
kawai dai ina ajiye kasuwancin ne da ramadan sabida tsufa yazo kuma azumi na wahaldani."
Murmushi kawai Alhaji Adamu yayi sabida yasa Baba Bello itikafi yake shiga shi kuma yana b'oyewa sabida gudun riya,
shiyasa yake ce musu hutun Ramadan kawai yakeyi.
shiko Dottijon cikin kulla ya kalli Saifuddeen kana murya a tausashe yace.
"Yaro na zaka iya yawon bin shago layi-layi kana raba musu ledodi, suna yi maka biyan bashin daddawan k'auye?."
murmushi yayi tare da gyad'a mishi kai alamar zai iya.
Shiko Dottijon sauk'owa yayi daga kan keken nashi kana ya zauna kusa da Saifuddeen cikin tattausan lafazi yace.
"Kullum in azumi yayi ina barin kasuwa duk costomomina sai dai suyi ta kame-kamen sayan leda wurin wasu,
anayin salla kuma da kwana biyu zan dawo to duk masu kawo musu sai su bari inci gaba da kawo musu kamar kullum to amman tunda gashi bana Allah ya had'ani da kai, in dai ka amince kayi al'k'awarin rik'e amana to zan kaika wurin babban dilanmu da yake bamu talla bisa farashi mai sauk'i,
zaike baka kaya ba tare da ka bashi ko asiba,
sai kai kuma ka tallata ka d'ora ribarka,
misali yau in ka kawo bazasu baka kud'iba sai gobe in ka kawo musu sai su baka kud'in na yau,
na yau kuma sai ka kawo musu na gobe.
to wasu ba ruwansu kana kai musu zasu biyaka,
wasu kuma dole sai goben,
to anan amanar da nakeso ka rik'e zan kaika gaban dilanmu amatsayin kai jikanane dan in baisan wani nakaba bazai bakaba,
in ya amince zai baka kuma zan had'aka da costomomina baki d'aya, nasan duk masu amana da gsky ne, suma kuma zan basu amanarka kada su ganka bakaji su cuceka, nasan zaka iya kasuwancin kam tunda kayi karatu zaku rink'ayin komai a rubuce."
cikin lumshe ido Saifuddeen ya had'e hannunsu wuri d'aya kana ya jinjina mishi sannan ya zaro biro ya fara rubutu a tafin hannunshi saida ya gama kana ya nunawa Jabeer nan Jabeer ya fara karanta abinda ya rubutan.
"In sha Allah Baba bazan kasance mara gsky ba a cikin had'akarmu,
nayi alk'awarin rik'oda gsky da amana bazan kunyataka ba,
ga Oga Adamu da abokina Jabeer da sauran maikatan shagon nan su zama shaida, Allah kuma ya bamu sa'a ngd matuk'a Allah ya k'ara lfy da wadata."
Murmushi sukayi baki d'aya,
daga nan Dottijon nan yayi gaba Saifuddeen na binshi a baya har shagon babban dilansu na leda,
nan ya gabatar dashi ga Alhaji Babayo,
ba wani dogon bincike Alhaji Babayo ya aminta da Saifuddeen sabida ganin Baba Bello ne ya kawoshi Dottijon da sunfi shekaru 20 suna tare a harkar leda.
shi kuwa Baba Bello ya musu bayanin Saifuddeen kurmane amman yana gane duk abinda ake cewa in yana ganin bakin mutun.
an yarda tuni an rattaba sunan Saifuddeen a jerin sunayen masu amsar talla,
yasa hannu shaidu sun saka hannu.
daga nan suka juya Baba Bello ya tasa Saifuddeen a gaba duk inda yasan yana kai ledodi saida ya nuna musu Saifuddeen yana ce musu jikanshi ne, kuma shi zai rink'a kawo musu Leda cikin azumi har sai bayan sallah shi zai dawo,
to dama duk kostomominshi sun san da baya kawo musu leda cikin azumi to sai sukaji dad'in wannan ci gaban koda sukaje shagon Alhaji Ibrahim baban Hisham yaji dad'in abun sosai ya sanya albarka haka dai duk wunin wannan ranar kam sukayi shi ranar bag d'in pure water takwas kawai ya saida sai dai ya saida su Coca-Cola sosai.
Sun bari akan sai ana gobe azumi zai fara tallan ledan tunda ranar Baba Bello zayi zuwan k'arshe sai kuma bayan sallah.
Anayin sallan magrib Salisu yazo ya d'aukeshi kamar kullum,
yau wurin mai shayi sukaje kwai aka soya musu da indomi kana sai ruwan tea,
bayan sunci ne sukayi sallan isha, kana suka kama hanyar Dukku.
Koda suka isa Saifuddeen na sauk'a Salisu ya zaro dubu biyar d'in balance ya mik'ashi,
amsa yayi kana ya zare 2k ya bashi yace yaje ya sayawa Mamanshi sugar da Lipton baiso karb'a amman dole ya amsa,
shi kuwa Saifuddeen yana shiga gida kai tsaye d'akin Umminshi ya shiga inda ya sameta ita da Aunty Nina suna hirarsu.
Bayan sun gaisane ya mik'e tare da yiwa Ummi alamun bari yaje yayi wonka.
To tace mishi kana sukaci gaba da hira,
shi kuwa solle jikinshi yayi suk'al kana ya shafa mai tare da fesa turare,
canza kaya yayi sannan ya nufi tsank'aya wurin Bappa Ali duk da yasan yau al'hamis ne ba karatu so ya kuma san canne wurin zaman Bappa Ali ko yaushe bayan sun gaisane ya mishi bayanin canjin sana'ar da zaiyi da tsarin kasuwancin da dokokinshi,
sosai Bappa Ali ya gamsu da hakan addu'a yayi da fatan al'khairi.
Koda ya tashi tafiya sai ya kwaso cinikinsa na yau duka da riban da jarin duk dubu 3 ne.
sai ya kuma zaro da sauran dubu ukun balance d'in ya had'asu inda suka bashi dubu shida kenan.
Cikin nitsuwa ya mik'awa bappa Ali.
Cikin tsuke fuska da fad'a bappa Ali yace.
"Me zanyi dasu? shin ba nacema Ka dena bani kud'iba in dai ban bakaba to ai baici ka baniba,
fatana Allah ya bud'a maka yadda zakayi kaci gaba da rik'e marayun k'annenka dani bappanku na gaza rik'ewa."
da sauri ya girgiza mishi kai kana ya rubuta mishi.
"Dan Allah Bappa Ali ka amshi kud'innan in dai ba rainawa kayiba, meyasa kullum in na baka abu baka amsa,
to in ban makaba waye zanyiwa kainefa uba a garemu ka sanya al'barka a lamarinmu in bani dashi zan baka ne?."
to ganin ranshi ya b'acine yasa Bappa Alin amsar tare da samishi al'barka.
Har ya tashi sai ya kuma zauna ganin Bappa Alin ya rik'o hannunshi bayan ya zaunane yake shaida mishi wannan mutumin daya kad'e Nuruddeen ya kawo musu kayan azumin.
Kama daga shinkafa, taliya, doya, Couscous, indomi, mai, manja, magi, gishiri, onga, kwai madara da Milo sugar Lipton, da kud'i 10k.
wani irin tsuke fuska Saifuddeen yayi tare had'e rai sai ya kuma yiwa bappa Ali alamun tambayar sun karb'ane?.
kai bappa Ali ya gyad'a mishi alamar eh sun amshi kayan,
cikin takaici ya...
By
*GARKUWAR FULANI*
8/
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 5*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
_Wannan shafi gaba ɗayanshi tukuicine da saudaukarwa ga Umar ibrahim Wambai, Allau rabbi ya baka lafiya!_
Free page🤝🏻