Sashe 34
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ita kuwa Rahma da sallama ta shiga d'akin Aunty Nina wacce take yiwa Abba nabkin cikin kula ta zauna gefenta tare da karb'an yaron taci gaba da sa mishi kayan sanyin dake gefensu cikin sanyinta tace.
"Anty Nina Saifuddeen ke son mgna da Bappa Ali,."
mik'ewa tayi tare da cewa.
"To bari in gaya mishi."
to tace sannan ta fara kiciniyar sawa Abba hula shi kuwa sai zillewa yakeyi.
Ita kuwa Aunty Nina tana zuwa turakan Bappa Ali tace.
"Malam,
Saifuddeen ke son Magna da kai."
kai ya jinjina tare da cewa.
"To gani nan zuwa."
daga nan ta juya taje ta gayawa Rahma da tuni ta gama kimtsa Abba,
mik'ewa tayi tare da bata yaron sannan ta fita ta tafi.
Tana shiga ba jimawa shima bappa Ali ya shigo da sallamarshi,
kan kujera ya zauna yayinda suna fuskantar juna dasu Saifuddeen,
pepar da biro Saifuddeen ya matso dashi kana yayiwa Rahma nuni data zauna ta harhad'a kan kudad'en asusun da suka farfasa shida Ummi suka juyesu bisa k'aramin sallayar Hayatuddeen.
Gyara zama yayi sannan ya fara rubuta mishi abinda yasa ya kirashi.
"Bappa Ali kar dai har kayi bacci na tasheka?."
kai ya jujjuya tare da cewa.
"A a banyi bacciba Saifuddeen dama nima inason mu tattauna."
murmushi yayi tare da rubuta mishi.
"To dama tun last two weeks nace ma maggi yayi tsada ko yayi ma fiye da yadda aka zata,
to shine nake son in sanar maka muyi shawarar yadda zamu saida,
sai kuma batun ribar ledodin da nike saidawa ina sawa a asusu to shine wannan yanzu muka fasa asusun."
ita dai Ummi tana saurarinsu yayinda ita kuwa Rahma taketa had'a kud'ad'en in ta had'a dubu tara sai tayi musu d'amara da cikon na goma kana sai ta ajiyesu.
Shi kuwa bappa Ali cikin nitsuwa yace.
"Eh lallai farashin Maggi ya k'aru sosai, ga kuma na kayan abinci ma ya k'aru matuk'a buhunan wake da na saya kan dubu 12 yanzu ya zama 30k ake saidashi, masara dubu 8 na sassaresu gashi yanzu sun koma dubu 15 ,
Kalwa na sayeshi buhu dubu tara-tara to gashi yanzu buhu dubu ashirin da biyar,
gero na sayeshi buhu dubu bakwai yanzu ya koma buhu dubu sha hud'u.
Gaba d'aya kayan abinci sun tsefe sunyi tsananin tsada talaka na fama da yunwa manoma sun saidashi tun yana araha gashi yanzu zasu dawo suna sayanshi da tsada kuma a yanzun suke fama da noma damuna tayi zurfi sama ruwa k'asa ruwa,
to dama na ajiyeshi ne kan haka yanzu zamu san yadda zamuyi mu sakeshi da araha yadda talaka zai samu sauk'in saya."
cikin jin dad'i Ummi tace.
"Madallah da mai zuciyar imani inama ace duk masu dama da kud'i suna haka to tabbas da masu sayanshi dan muguntar sai yayi tsada su fiddashi da sun bari."
shima Saifuddeen murmushi yayi cikin jin dad'in yanaga zasu samu damar taimakawa marasa k'arfi ya rubuta musu.
"Yauwa Bappa Ali wannan abu yayi kyau,
Magging ma dole zamu sake fara shinsa dan talaka ya samu yadda zaiyi."
jinjina kai bappa Alin yayi tare da cewa.
"Yauwa to muga ya lissafin zaiyi,
kaga lokacin dana sai wake ana saida mudun akan d'ari da goma,
kaga yanzu kuma ana saida mudun akan d'ari biyu da saba'in,
to Alhamdulillahi dama ana kasuwa dan ribane,
dan haka mu zamu rink'a saida mudun wake akan d'ari da talatin, mudun gombe kenan mudun kano da sauran garuruwa masu amfani da kwanon sha kuwa in munyi kiyasti da kud'in mudunmu zamu saida musu mudun akan d'ari biyu da settin
sab'anin sauran mutane dake saida mudun akan d'ari biyu da saba'in a mudun gombe mai cin gongoni takwas zuwa tara
kaga ko wanne mudu minbi ribar naira ishirin kacal fatanmu Allah ya musu al'barka ya kuma sa kasuwar ta d'aure."
wasu zafafan hawayen farin cikine ya rufe Ummi dan tana ji a jikinta ahlinta masu cikar imanine da zarra.
Shima Saifuddeen murmushi yakeyi da godewa Allah da tsarkake mishi zuciyarshi data ahlinshi,
shi kuwa bappa Ali ciga yayi da cewa.
"Lokacin dana sarin kayan mudun masara naira 100 ne yanzu kuma mudun ya koma d'ari da tamanin,
to mu zamuke saidashi bisa d'ari da ashirin munyi ragin naira sattin akan farashin sauran mutane munbi ribar naira ishirin."
sai ya kuma gyara zamanshi tare yi mishi lissafinsu dalla-dalla gaba d'aya sun karya farashin kayan abincin nasu inda suka rink'a bin ribar naira ashirin-ashirin kacal,
sai a buhunan kalwa da rid'ine, sukaci ribar naira hamsin-hamsin a kan ko wanne mudu,
dan shi ba kayan abinci bane baya zama dole sai mutun ya saya musammam rid'i wanda shi kamfanunnuka ne ke sayanshi ana fiddashi k'asashen k'etare.
inda suka tsaida farashin sari kuma akan buhun shinkafa sharshera sun sayeta dubu tara to yanzu ana saidata dubu sha shida to su dubu goma sha d'aya suke saidata sukanbi ribar dubu biyu a cikin ko wanne buhun shinkafa.
Rahma da kanta ajiye irgen kud'in tayi ta zuba musu idanu domin tabbas tasan k'anin mahaifinta ya cika adalin malamin d'an kasuwa,
shi kuwa bappa Ali gyara zama yayi yaci gaba da cewa.
"Gero da dawa duk ribar dubu bibbiyu zamubi akan ko wanne buhu sab'anin sauran mutanen dake bin ribar dubu bakwai da d'ari biyar-biyar.
Sosai sukaci gaba da lissafin inda a cikin ko wanne buhun rid'i da kalwa suka bi ribar dubu biyar-biyar sab'anin wasu dake bin ribar dubu goma sha d'ad'd'aya.
Saida suka gama lissafin kab sannan ya gaya mishi yawan buhunan ko wanne abu inda buhunan masaransu kawai sun kai d'ari da biyar
sai buhun gyararriyar shinfaka mai cin mudu tamanin inda ake saidashi dubu talatin so su kuma sun barshi kan dubu sha bakai sunci ribar dubu uku cikin ko wanne buhu,
nan suka kiyasta komai,
sannan ya karb'i takardar da Saifuddeen ke mik'o mishi inda yake ce mishi.
"Duk cikin katon d'in maggi akwai ribar da ta kusa uwar kud'in,
sabida MAGGIN naira goma ya koma d'aya rak za'a k'ara ya koma ashirin,
to ribar tayi yawanda talaka shine da wuya,
dan haka sai nayi tunanin mai zai hana mu mu rink'a saidawa uku goma tunda dama hud'u gomane mu rink'a bin kwaya d'ad'ad'aya,
sannan ana saida ledan akan d'ari biyu da hamsin a da can wota bakwai baya yanzu kuma ledan ya koma d'ari hud'u dai-dai shine nace to nawa ya kamata muke sakin ledan?."
murmushi Bappa Alin yayi dan ganin umarninshi Saifuddeen ke jira cikin nitsuwa yace.
"Kabi riba kad'an mai al'barka kabar ko wanne leda akan d'ari biyu da saba'in kaga ai dama can hamsin d'in sama ribar tasuce a company a d'ari biyu ake basu.
Kaga kuma kai a kasuwane in ka sakeshi da yawa abokan kasuwancinka zasuji haushinka zasuga zaka kashe musu kasuwane hakan kuma zai iya jaza maka matsala shiyasa badon hakaba da d'ari biyu da hamsin d'in zaka saidashi ko ya kuka gani Hajia Ummi."
kai ta jujjuya mishi cikin jin dad'i tace.
"Allah dai yasa Alhaji Ali Allah ya sa munada ranon zuwa makka da madina birnin ma'aiki."
Amin Amin sukace baki d'aya sannan taci gaba da cewa.
"Wannan ai mgnar ta uba da d'anshi ne ni saidai in sanya al'barka ina kuma nema muku tsari a wurin rabbil izzati."
gyara zama Saifuddeen yayi tare da rubuta musu.
"Eh hakanma yayi Bappa Ali amman kada ka damu ni zanbi hamsin d'in a cikin ko wanne leda,
shagunan zanbi in musu talla in zasu sara zan basu a farashin da d'in amman suyi min al'kawarin saidawa shida ashirin sab'anin biyar ashirin d'in da suke saidawa,
kaga zai zama uku goma kenan,
ni zanbi k'aramar ribar,
a dai wannan sarin in yaso a sari na gaba in naga hakan bazai yuwuba sai inbi sahunsu tunda nima dole da tsadan zan sara."
sosai suka gamsu da wannan shawarar suka k'ark'are komai aka gobe in yaje zaiwa su Alhaji Kabirun tallan.
Shi kuwa bappa Ali cikin nitsuwa yace.
"Dole zaka ci gaba da rik'e shagon nan da aka ajiye maggin,
lokaci yayi da zaka samu sauk'in wahala,
zamuje a gyara kayayyakin in an samu wasu sun sara to sai a samu akori kura a cikata da kayayyakin abincin ta kai shagon sai a fara saidawa."
cikin gamsuwa Saifuddeen ya rubuta musu.
"Hakan yayi shike nan kuma nasan Warisu zai kular mana da komai,
zan kuma yiwa ba mishkila talla nasan zai sara kuma zai bari a farashin da zamu bari dan nasan shi adalin d'an kasuwane mai imani".
sosai sukaji dad'in wannan zaman nasu,
yayinda tuni Rahma taketa famam irga kud'in ganin ta kusa gamawa ne yasa duk suka zuba mata ido dan suna jiran suji nawane kud'in.
"Anty Nina Saifuddeen ke son mgna da Bappa Ali,."
mik'ewa tayi tare da cewa.
"To bari in gaya mishi."
to tace sannan ta fara kiciniyar sawa Abba hula shi kuwa sai zillewa yakeyi.
Ita kuwa Aunty Nina tana zuwa turakan Bappa Ali tace.
"Malam,
Saifuddeen ke son Magna da kai."
kai ya jinjina tare da cewa.
"To gani nan zuwa."
daga nan ta juya taje ta gayawa Rahma da tuni ta gama kimtsa Abba,
mik'ewa tayi tare da bata yaron sannan ta fita ta tafi.
Tana shiga ba jimawa shima bappa Ali ya shigo da sallamarshi,
kan kujera ya zauna yayinda suna fuskantar juna dasu Saifuddeen,
pepar da biro Saifuddeen ya matso dashi kana yayiwa Rahma nuni data zauna ta harhad'a kan kudad'en asusun da suka farfasa shida Ummi suka juyesu bisa k'aramin sallayar Hayatuddeen.
Gyara zama yayi sannan ya fara rubuta mishi abinda yasa ya kirashi.
"Bappa Ali kar dai har kayi bacci na tasheka?."
kai ya jujjuya tare da cewa.
"A a banyi bacciba Saifuddeen dama nima inason mu tattauna."
murmushi yayi tare da rubuta mishi.
"To dama tun last two weeks nace ma maggi yayi tsada ko yayi ma fiye da yadda aka zata,
to shine nake son in sanar maka muyi shawarar yadda zamu saida,
sai kuma batun ribar ledodin da nike saidawa ina sawa a asusu to shine wannan yanzu muka fasa asusun."
ita dai Ummi tana saurarinsu yayinda ita kuwa Rahma taketa had'a kud'ad'en in ta had'a dubu tara sai tayi musu d'amara da cikon na goma kana sai ta ajiyesu.
Shi kuwa bappa Ali cikin nitsuwa yace.
"Eh lallai farashin Maggi ya k'aru sosai, ga kuma na kayan abinci ma ya k'aru matuk'a buhunan wake da na saya kan dubu 12 yanzu ya zama 30k ake saidashi, masara dubu 8 na sassaresu gashi yanzu sun koma dubu 15 ,
Kalwa na sayeshi buhu dubu tara-tara to gashi yanzu buhu dubu ashirin da biyar,
gero na sayeshi buhu dubu bakwai yanzu ya koma buhu dubu sha hud'u.
Gaba d'aya kayan abinci sun tsefe sunyi tsananin tsada talaka na fama da yunwa manoma sun saidashi tun yana araha gashi yanzu zasu dawo suna sayanshi da tsada kuma a yanzun suke fama da noma damuna tayi zurfi sama ruwa k'asa ruwa,
to dama na ajiyeshi ne kan haka yanzu zamu san yadda zamuyi mu sakeshi da araha yadda talaka zai samu sauk'in saya."
cikin jin dad'i Ummi tace.
"Madallah da mai zuciyar imani inama ace duk masu dama da kud'i suna haka to tabbas da masu sayanshi dan muguntar sai yayi tsada su fiddashi da sun bari."
shima Saifuddeen murmushi yayi cikin jin dad'in yanaga zasu samu damar taimakawa marasa k'arfi ya rubuta musu.
"Yauwa Bappa Ali wannan abu yayi kyau,
Magging ma dole zamu sake fara shinsa dan talaka ya samu yadda zaiyi."
jinjina kai bappa Alin yayi tare da cewa.
"Yauwa to muga ya lissafin zaiyi,
kaga lokacin dana sai wake ana saida mudun akan d'ari da goma,
kaga yanzu kuma ana saida mudun akan d'ari biyu da saba'in,
to Alhamdulillahi dama ana kasuwa dan ribane,
dan haka mu zamu rink'a saida mudun wake akan d'ari da talatin, mudun gombe kenan mudun kano da sauran garuruwa masu amfani da kwanon sha kuwa in munyi kiyasti da kud'in mudunmu zamu saida musu mudun akan d'ari biyu da settin
sab'anin sauran mutane dake saida mudun akan d'ari biyu da saba'in a mudun gombe mai cin gongoni takwas zuwa tara
kaga ko wanne mudu minbi ribar naira ishirin kacal fatanmu Allah ya musu al'barka ya kuma sa kasuwar ta d'aure."
wasu zafafan hawayen farin cikine ya rufe Ummi dan tana ji a jikinta ahlinta masu cikar imanine da zarra.
Shima Saifuddeen murmushi yakeyi da godewa Allah da tsarkake mishi zuciyarshi data ahlinshi,
shi kuwa bappa Ali ciga yayi da cewa.
"Lokacin dana sarin kayan mudun masara naira 100 ne yanzu kuma mudun ya koma d'ari da tamanin,
to mu zamuke saidashi bisa d'ari da ashirin munyi ragin naira sattin akan farashin sauran mutane munbi ribar naira ishirin."
sai ya kuma gyara zamanshi tare yi mishi lissafinsu dalla-dalla gaba d'aya sun karya farashin kayan abincin nasu inda suka rink'a bin ribar naira ashirin-ashirin kacal,
sai a buhunan kalwa da rid'ine, sukaci ribar naira hamsin-hamsin a kan ko wanne mudu,
dan shi ba kayan abinci bane baya zama dole sai mutun ya saya musammam rid'i wanda shi kamfanunnuka ne ke sayanshi ana fiddashi k'asashen k'etare.
inda suka tsaida farashin sari kuma akan buhun shinkafa sharshera sun sayeta dubu tara to yanzu ana saidata dubu sha shida to su dubu goma sha d'aya suke saidata sukanbi ribar dubu biyu a cikin ko wanne buhun shinkafa.
Rahma da kanta ajiye irgen kud'in tayi ta zuba musu idanu domin tabbas tasan k'anin mahaifinta ya cika adalin malamin d'an kasuwa,
shi kuwa bappa Ali gyara zama yayi yaci gaba da cewa.
"Gero da dawa duk ribar dubu bibbiyu zamubi akan ko wanne buhu sab'anin sauran mutanen dake bin ribar dubu bakwai da d'ari biyar-biyar.
Sosai sukaci gaba da lissafin inda a cikin ko wanne buhun rid'i da kalwa suka bi ribar dubu biyar-biyar sab'anin wasu dake bin ribar dubu goma sha d'ad'd'aya.
Saida suka gama lissafin kab sannan ya gaya mishi yawan buhunan ko wanne abu inda buhunan masaransu kawai sun kai d'ari da biyar
sai buhun gyararriyar shinfaka mai cin mudu tamanin inda ake saidashi dubu talatin so su kuma sun barshi kan dubu sha bakai sunci ribar dubu uku cikin ko wanne buhu,
nan suka kiyasta komai,
sannan ya karb'i takardar da Saifuddeen ke mik'o mishi inda yake ce mishi.
"Duk cikin katon d'in maggi akwai ribar da ta kusa uwar kud'in,
sabida MAGGIN naira goma ya koma d'aya rak za'a k'ara ya koma ashirin,
to ribar tayi yawanda talaka shine da wuya,
dan haka sai nayi tunanin mai zai hana mu mu rink'a saidawa uku goma tunda dama hud'u gomane mu rink'a bin kwaya d'ad'ad'aya,
sannan ana saida ledan akan d'ari biyu da hamsin a da can wota bakwai baya yanzu kuma ledan ya koma d'ari hud'u dai-dai shine nace to nawa ya kamata muke sakin ledan?."
murmushi Bappa Alin yayi dan ganin umarninshi Saifuddeen ke jira cikin nitsuwa yace.
"Kabi riba kad'an mai al'barka kabar ko wanne leda akan d'ari biyu da saba'in kaga ai dama can hamsin d'in sama ribar tasuce a company a d'ari biyu ake basu.
Kaga kuma kai a kasuwane in ka sakeshi da yawa abokan kasuwancinka zasuji haushinka zasuga zaka kashe musu kasuwane hakan kuma zai iya jaza maka matsala shiyasa badon hakaba da d'ari biyu da hamsin d'in zaka saidashi ko ya kuka gani Hajia Ummi."
kai ta jujjuya mishi cikin jin dad'i tace.
"Allah dai yasa Alhaji Ali Allah ya sa munada ranon zuwa makka da madina birnin ma'aiki."
Amin Amin sukace baki d'aya sannan taci gaba da cewa.
"Wannan ai mgnar ta uba da d'anshi ne ni saidai in sanya al'barka ina kuma nema muku tsari a wurin rabbil izzati."
gyara zama Saifuddeen yayi tare da rubuta musu.
"Eh hakanma yayi Bappa Ali amman kada ka damu ni zanbi hamsin d'in a cikin ko wanne leda,
shagunan zanbi in musu talla in zasu sara zan basu a farashin da d'in amman suyi min al'kawarin saidawa shida ashirin sab'anin biyar ashirin d'in da suke saidawa,
kaga zai zama uku goma kenan,
ni zanbi k'aramar ribar,
a dai wannan sarin in yaso a sari na gaba in naga hakan bazai yuwuba sai inbi sahunsu tunda nima dole da tsadan zan sara."
sosai suka gamsu da wannan shawarar suka k'ark'are komai aka gobe in yaje zaiwa su Alhaji Kabirun tallan.
Shi kuwa bappa Ali cikin nitsuwa yace.
"Dole zaka ci gaba da rik'e shagon nan da aka ajiye maggin,
lokaci yayi da zaka samu sauk'in wahala,
zamuje a gyara kayayyakin in an samu wasu sun sara to sai a samu akori kura a cikata da kayayyakin abincin ta kai shagon sai a fara saidawa."
cikin gamsuwa Saifuddeen ya rubuta musu.
"Hakan yayi shike nan kuma nasan Warisu zai kular mana da komai,
zan kuma yiwa ba mishkila talla nasan zai sara kuma zai bari a farashin da zamu bari dan nasan shi adalin d'an kasuwane mai imani".
sosai sukaji dad'in wannan zaman nasu,
yayinda tuni Rahma taketa famam irga kud'in ganin ta kusa gamawa ne yasa duk suka zuba mata ido dan suna jiran suji nawane kud'in.