Sashe 4
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bayan anyi sallan azaharne, Seyo ya biya wurin mai kayan miya ya sayi naman miya dasu tattasai. al'basa, atraruhu. sannan yakuwa da alaiyahu da ganyen al'basa. Kana ya nufo gida a tsakiyan gida ya samu Ummi da Aunty Nina matar Bappa Ali,
nan yazo ya zauna yana dariya cikin yanayinshi na raha yace.
"Yau kam Ummi na k'uruciya takeji, kalli yadda tasha duma."
dariya sukayi baki d'aya kana yaje ya d'auko wuk'a da tire da babban roba ya debo ruwa a ciki kana yasa gishiri sannan yazo ya zauna gefenta ya fara wonke ganyen.
Bayan ya gama wonke ganyen ya tsanesu ya sakasu bisa tiren kana ya mik'e tsaye hannunshi dak'e jik'e har yana d'igar da ruwa, ne ya kallesu kana ya nunawa Ummi su sannan yayi mumurshi kana ya fara yarfasu yana watsar da ruwan yana barin jikin hannun nashi, still yana murmushi ta tare da tonk'oshe kanshi bisa kafad'unshi ya kalli Saifuddeen daya shigo yanzu hannunsa rik'e da carbi,
k'ara yarfa hannun nashi yayi a karo na bakwai sannan ya kallesu dukansu kana cikin yanayinshi na mai matuk'ar fara'a yace.
"Na gama! Ummi na gama!! Na gama!!! Nawa aikin na kammale komai saura kuma Saifuddeen zai k'arisa, kada ku tab'a komai ku barshi da wannan aikin zaiyi komai yadda ya kamata fiyema da yadda ni zanyi ko yadda zakuyi."
Zurui Ummi tayi tare da zuba mishi idanu,
Rahma kuwa murmushi tayi kana tace.
"Kai Ya Seyoji gani ni mace ga Raihana ga Ummi ga Raliyya duk bamuyi aikinba sai Saifuddeen namiji."
matsowa yayi kusa da Saifuddeen Kana ya had'e hannayensu wuri d'aya ya rik'e hannun Saifu gam cikin nasa kana ya kalli Rahma sannan yace.
"Wannan aikin nashi ne daga yau, ai ba aikin mata bane na mazane, shi zai iya ke bazaki iyaba."
Ummi kuwa ajiyan zuciya ta sauk'e kana tace.
"Yau kam bazaka je Gombe bako?."
sakin hannun Saifuddeen yayi kana ya gyara tsayuwarshi sannan yace.
"Zanje Ummi yanzuma zan tafi."
shiru sukayi baki d'aya kana Saifuddeen ya tsuguna a gabanshi yayi rubutu kamar haka.
"Ya Seyoji ka bari mana tunda bakayi sammako ba ka bari kawai sai gobe."
dafa kafad'unshi yayi kana yace.
"Saifuddeen ai tafiyar yau dolece a kaina dolen dole sai naje.
Dan ina son samo maka kud'in hidimar karatunka.
kana ga Faruq ma an kusa neman school fees,
ga Rahaina tace min auren k'awarta ya kusa zasuyi anko kaga dole in dage in isarmuku.
Gashi naga Leda carpet d'in Ummi na ya fara yagewa."
cikin kula Ummi tace to.
"Allah ya kiyaye hanya ya kaika lfy ya dawo da kai lfy, Allah ya baka sa'a."
"Amin Amin ya rabbil izzati." ya amsa kana ya juya ya shiga d'aki inda Abbansu yake, ya dade a cika sannan ya fito,
yana isewa inda suke ya kama hannun Saifuddeen yajashi suka nufi gaban Ummi sannan yace.
"Kin ganshi Ummi yaron kin nan ko yanada wata baiwa ta musamman a jikinshi, kuma ki kula zaki iya ganowa,
shiyasa ni bama zan fara yin aureba sai na fara yi mishi aure."
dariya sukayi baki d'aya kana yace.
"To Ummi na tafi."
Aunty Nina ce matar Bappa Ali wanda tun d'azu batayi mgnaba sai yanzu tace.
"Allah ya bada sa'a in kana dawowa ka siyo min a gwalima."
har ya juya zai fita sai ya kuma juyowa tare da zaro ido kana ya tab'e baki sannan yace.
"Kawai Aunty Nina kice mun kusa mu zama mu bakwai."
kai kawai ta kauda dan ta sanshi da iya zolaya,
daga nan basu kuma cewa komai ba,
yaja hannun Saifuddeen suka fita,
sun dad'e suna tsaye a bakin masallacin dake k'ofar gidansu.
bisa dukkan alamu mgna mai mahimmaci yakewa k'anin nashi,
har ya tada mashin d'in sai ya kuma kashewa ya sauka da sauri kana yayi cikin gida.
Yana shiga gaban Ummi ya d'an rusuna kana yace.
"Na manta Ummi bance miki kada kiyi kukaba shiyasa na dawo,
dan Allah Ummina kada kiyi kuka dukkan tsanani yana tare da sauk'i."
kai ta jinjina tare da cewa.
"To Nuruddeen insha Allah bazanyi kukaba."
mik'ewa yayi tare da cewa.
"To na tafi, hankalina a kwance tunda nasan bazakiyi min kukaba."
yana fita ya kuma tasa Saifuddeen da Hayatudden a gaba yai ta musu nasiha,
kana ya kuma hawa mashin d'in ya kunna,
still ya kuma kashewa ya sake komawa cikin gida kawai sai ya tsaya yayi ta kallon cikin gidan nasu baki d'aya, kana ya kuma dawo da hankalin shi da dubanshi kan Ummi, ya kai 5 minutes yana kallonta tana kallonshi amman babu wanda yayi mgna cikinsu,
hakama yayi da Raihana da Raliya,
Rahma kuwa tana ganin yadda yaketa binsu da kallo sai kawai taji hawaye na kwaranyo mata,
kuma ta kasa cewa komai,
shima Nuruddeen hawayen ne yaji suna zubo mishi, sanin in Ummi taga hawayenshi hankalinta zai tashi,
sai yayi maza ya fita.
Hannun Hayatuddeen ya kamo ya saka cikin na Saifuddeen kana yace.
"Ka rik'eshi fiye da yadda uwa zata rik'i d'anta, ka hanashi kukan maraici, ka hana Ummi kukan k'unci, ka zamewa su Rahma Garkuwa kada ka bari yaranta suyi maraici."
sai ya kuma kalli Hayatuddeen kana yace.
"Autanmu kaga Hamma Saifunka ko to ba Yaya bane kawai a wurinka ubane a wurinka, kayi mishi dukkan biyayyan da d'a zaiwa ubanshi ku had'a kanku, ku had'a hannu ku share hawayen Ummi da yan uwanmu matannan. Ni kam Addu'a kawai nakeso daga gareku."
Duk sun kasa motsi domin shi dai Saifuddeen kalaman Yayanshi ya sakar mishi kasala, shiko Hayatuddeen, ido kawai ya zubawa fuskokinsu ya kalli wannan kana ya juyo ya kalli wannan.
Shi kuwa Nuruddeen, tada mashin d'in nashi yayi sannan ya takata,
ya k'ara masowa gab da Saifuddeen suka kalli juna kana yayi murmushin da yasa hawayen shi kwaranyowa a idanunshi ,cikin zubda hawaye murya na rawa yace.
"Saifuddeen babu nakasasshe sai rago, kuma nasan kai ba rago bane,
Saifuddeen kasa a ranka Nakasa ba kasawa bace."
yana fad'in haka ya ja mashin d'inshi ya tafi, yana woiwoyosu, Hayatuddeen kuwa sai hannu yake d'aga mishi, shiko Saifudddeen addu'a ya rink'a mishi a ransa.
A cikin Gombe kuwa, Nuruddeen yana shiga gari yana bisa babban titin tashan Dukku yana isowa dai-dai Tashan Dukku yazo dai-dai bakin tashar kenan shi yana shirin wucewa, kana wata mota ta fito cikin tashan dai-dai lokacin da Nuruddeen yazo bakin wurin, wannan motar birkinta ya d'an kubcewa matuk'inta.
Cikin rashin sa'ar takan birkin tayi kan Nuruddeen.....!!!
By
*GARKUWAR FULANI*
8/
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 3*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
_Wannan page ɗin nakune gaba ɗayanshi ƴan Hukuncin Allah fans Especially Mom Asas, Zee Ya'u, Jannart Salis, ina muku fatan al'khairi._
~Gareku masu buƙatan biyan kuɗin littafin ,turo katin mtn na ɗari uku, ta wannan layin 09097853276 ko transfer ta nan 0005388578 jaiz bank Asha Aliyu Garkuwa~
Cikin tsananin razana da tsoro jiki na rawa mai jan motar ya fara kiciniyar taka birki.
Amman ina abin ya gagara, tuni birkinta ya kubce mishi, ido ya zaro da sauri lokacin da yaga motar tashi ta nufi kan Nuruddeen gadan-gadan
ji kakeyi k'uuuuuiyyyyhh.
motarnan ta bugu machine d'in Nuruddeeen bugu mai tsanani wanda yasa, Nuruddeen yayi tsalle yayi sama kana ya fad'o kan bump d'in tsakiyar titin,
"Innalillahi'wa'illaihi rajiun. Hasbunallahu wani'imal wakil."
Shine abinda tarin mutanen dake zageye da Nuruddeen suke fad'i,
yayinda wasu suka ma kasa mgna sai d'aura hannu sukayi a kai, kana wasu sai jujjuya kai sukeyi.
mai mota kuwa da ker ya samu ya fara sarrafa motar har ya samu ta tsaya,
yana fitowa da gudu ya nufi inda dandazon mutanen suke,
kutsawa yayi tayi tsakiyar mutanen har ya samu ya isa,
ido ya rumtse da k'arfi cikin tsananin fargaba ya sunkuyo kan Nuruddeen da yake konce lib bisa titi, ida nunshi a rufe kirib sai numfashin shi dake korar juna,
da sauri ya tallaboshi tare dagowa ya kalli mutanen cikin tashin hankali yace.
"Ku taimaka min mana in d'agashi in sashi a mota."
wani k'ak'k'arfan matashi ne,
yayi maza ya sunkuyo ya ciccibi Nuruddeen kana cikin, d'aga murya yace.
"Biyoni."
yana fad'in haka ya juya ya tsallaka titin zuwa d'aya hannun kana ya nufi cikin asibitin MUSABA dake fuskantar tashan Dukkun,
cikin rawan jiki mutumin ya mik'e kana yabi bayanshi.
suna shiga Reception suka nufa,
ganin sun shigo hajaram majaram yasa Nurse's yin kansu da tambayar meke faruwa,
cikin kad'uwa mutumin nan yace,
"Accident ne ku taimaka doctor ya dubashi."
juyawa sukayi suka kalli juna, kana d'aya daga cikinsu tace.
"Ko an gayawa doctor bazai dubashi ba sai an nemo police."
jin haka yasa mutumin nan juyawa da sauri ya fita,
gudu-gudu sauri-sauri ya tsallaka titin kana ya nufi wurin motar tashi, yana shiga ya nufi Gombe division yana zuwa ya musu bayanin abinda ke faruwa,
ba b'ata lokaci suka had'ashi da police d'aya, kana suka tafi tare,
suna zuwa Doctor in ya amsheshi bisa sa hannun hukuma kana fara bashi taimakon gaggawa, sannan daga bisani ya ce su tafi Medical Center.
Ba b'ata lokaci suka amshi shawararshi suka tafi can,
suna zuwa aka amsheshi.
shi kuwa police yasa d'aya police d'in yaje ya d'auki machine d'n nashi ya kaishi officensu.
kana sun samu wayarshi y'ar Nokia dake jikinshi tanan aka kira Bappa Ali aka sanar mishi meke faruwa.
nan yazo ya zauna yana dariya cikin yanayinshi na raha yace.
"Yau kam Ummi na k'uruciya takeji, kalli yadda tasha duma."
dariya sukayi baki d'aya kana yaje ya d'auko wuk'a da tire da babban roba ya debo ruwa a ciki kana yasa gishiri sannan yazo ya zauna gefenta ya fara wonke ganyen.
Bayan ya gama wonke ganyen ya tsanesu ya sakasu bisa tiren kana ya mik'e tsaye hannunshi dak'e jik'e har yana d'igar da ruwa, ne ya kallesu kana ya nunawa Ummi su sannan yayi mumurshi kana ya fara yarfasu yana watsar da ruwan yana barin jikin hannun nashi, still yana murmushi ta tare da tonk'oshe kanshi bisa kafad'unshi ya kalli Saifuddeen daya shigo yanzu hannunsa rik'e da carbi,
k'ara yarfa hannun nashi yayi a karo na bakwai sannan ya kallesu dukansu kana cikin yanayinshi na mai matuk'ar fara'a yace.
"Na gama! Ummi na gama!! Na gama!!! Nawa aikin na kammale komai saura kuma Saifuddeen zai k'arisa, kada ku tab'a komai ku barshi da wannan aikin zaiyi komai yadda ya kamata fiyema da yadda ni zanyi ko yadda zakuyi."
Zurui Ummi tayi tare da zuba mishi idanu,
Rahma kuwa murmushi tayi kana tace.
"Kai Ya Seyoji gani ni mace ga Raihana ga Ummi ga Raliyya duk bamuyi aikinba sai Saifuddeen namiji."
matsowa yayi kusa da Saifuddeen Kana ya had'e hannayensu wuri d'aya ya rik'e hannun Saifu gam cikin nasa kana ya kalli Rahma sannan yace.
"Wannan aikin nashi ne daga yau, ai ba aikin mata bane na mazane, shi zai iya ke bazaki iyaba."
Ummi kuwa ajiyan zuciya ta sauk'e kana tace.
"Yau kam bazaka je Gombe bako?."
sakin hannun Saifuddeen yayi kana ya gyara tsayuwarshi sannan yace.
"Zanje Ummi yanzuma zan tafi."
shiru sukayi baki d'aya kana Saifuddeen ya tsuguna a gabanshi yayi rubutu kamar haka.
"Ya Seyoji ka bari mana tunda bakayi sammako ba ka bari kawai sai gobe."
dafa kafad'unshi yayi kana yace.
"Saifuddeen ai tafiyar yau dolece a kaina dolen dole sai naje.
Dan ina son samo maka kud'in hidimar karatunka.
kana ga Faruq ma an kusa neman school fees,
ga Rahaina tace min auren k'awarta ya kusa zasuyi anko kaga dole in dage in isarmuku.
Gashi naga Leda carpet d'in Ummi na ya fara yagewa."
cikin kula Ummi tace to.
"Allah ya kiyaye hanya ya kaika lfy ya dawo da kai lfy, Allah ya baka sa'a."
"Amin Amin ya rabbil izzati." ya amsa kana ya juya ya shiga d'aki inda Abbansu yake, ya dade a cika sannan ya fito,
yana isewa inda suke ya kama hannun Saifuddeen yajashi suka nufi gaban Ummi sannan yace.
"Kin ganshi Ummi yaron kin nan ko yanada wata baiwa ta musamman a jikinshi, kuma ki kula zaki iya ganowa,
shiyasa ni bama zan fara yin aureba sai na fara yi mishi aure."
dariya sukayi baki d'aya kana yace.
"To Ummi na tafi."
Aunty Nina ce matar Bappa Ali wanda tun d'azu batayi mgnaba sai yanzu tace.
"Allah ya bada sa'a in kana dawowa ka siyo min a gwalima."
har ya juya zai fita sai ya kuma juyowa tare da zaro ido kana ya tab'e baki sannan yace.
"Kawai Aunty Nina kice mun kusa mu zama mu bakwai."
kai kawai ta kauda dan ta sanshi da iya zolaya,
daga nan basu kuma cewa komai ba,
yaja hannun Saifuddeen suka fita,
sun dad'e suna tsaye a bakin masallacin dake k'ofar gidansu.
bisa dukkan alamu mgna mai mahimmaci yakewa k'anin nashi,
har ya tada mashin d'in sai ya kuma kashewa ya sauka da sauri kana yayi cikin gida.
Yana shiga gaban Ummi ya d'an rusuna kana yace.
"Na manta Ummi bance miki kada kiyi kukaba shiyasa na dawo,
dan Allah Ummina kada kiyi kuka dukkan tsanani yana tare da sauk'i."
kai ta jinjina tare da cewa.
"To Nuruddeen insha Allah bazanyi kukaba."
mik'ewa yayi tare da cewa.
"To na tafi, hankalina a kwance tunda nasan bazakiyi min kukaba."
yana fita ya kuma tasa Saifuddeen da Hayatudden a gaba yai ta musu nasiha,
kana ya kuma hawa mashin d'in ya kunna,
still ya kuma kashewa ya sake komawa cikin gida kawai sai ya tsaya yayi ta kallon cikin gidan nasu baki d'aya, kana ya kuma dawo da hankalin shi da dubanshi kan Ummi, ya kai 5 minutes yana kallonta tana kallonshi amman babu wanda yayi mgna cikinsu,
hakama yayi da Raihana da Raliya,
Rahma kuwa tana ganin yadda yaketa binsu da kallo sai kawai taji hawaye na kwaranyo mata,
kuma ta kasa cewa komai,
shima Nuruddeen hawayen ne yaji suna zubo mishi, sanin in Ummi taga hawayenshi hankalinta zai tashi,
sai yayi maza ya fita.
Hannun Hayatuddeen ya kamo ya saka cikin na Saifuddeen kana yace.
"Ka rik'eshi fiye da yadda uwa zata rik'i d'anta, ka hanashi kukan maraici, ka hana Ummi kukan k'unci, ka zamewa su Rahma Garkuwa kada ka bari yaranta suyi maraici."
sai ya kuma kalli Hayatuddeen kana yace.
"Autanmu kaga Hamma Saifunka ko to ba Yaya bane kawai a wurinka ubane a wurinka, kayi mishi dukkan biyayyan da d'a zaiwa ubanshi ku had'a kanku, ku had'a hannu ku share hawayen Ummi da yan uwanmu matannan. Ni kam Addu'a kawai nakeso daga gareku."
Duk sun kasa motsi domin shi dai Saifuddeen kalaman Yayanshi ya sakar mishi kasala, shiko Hayatuddeen, ido kawai ya zubawa fuskokinsu ya kalli wannan kana ya juyo ya kalli wannan.
Shi kuwa Nuruddeen, tada mashin d'in nashi yayi sannan ya takata,
ya k'ara masowa gab da Saifuddeen suka kalli juna kana yayi murmushin da yasa hawayen shi kwaranyowa a idanunshi ,cikin zubda hawaye murya na rawa yace.
"Saifuddeen babu nakasasshe sai rago, kuma nasan kai ba rago bane,
Saifuddeen kasa a ranka Nakasa ba kasawa bace."
yana fad'in haka ya ja mashin d'inshi ya tafi, yana woiwoyosu, Hayatuddeen kuwa sai hannu yake d'aga mishi, shiko Saifudddeen addu'a ya rink'a mishi a ransa.
A cikin Gombe kuwa, Nuruddeen yana shiga gari yana bisa babban titin tashan Dukku yana isowa dai-dai Tashan Dukku yazo dai-dai bakin tashar kenan shi yana shirin wucewa, kana wata mota ta fito cikin tashan dai-dai lokacin da Nuruddeen yazo bakin wurin, wannan motar birkinta ya d'an kubcewa matuk'inta.
Cikin rashin sa'ar takan birkin tayi kan Nuruddeen.....!!!
By
*GARKUWAR FULANI*
8/
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 3*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
_Wannan page ɗin nakune gaba ɗayanshi ƴan Hukuncin Allah fans Especially Mom Asas, Zee Ya'u, Jannart Salis, ina muku fatan al'khairi._
~Gareku masu buƙatan biyan kuɗin littafin ,turo katin mtn na ɗari uku, ta wannan layin 09097853276 ko transfer ta nan 0005388578 jaiz bank Asha Aliyu Garkuwa~
Cikin tsananin razana da tsoro jiki na rawa mai jan motar ya fara kiciniyar taka birki.
Amman ina abin ya gagara, tuni birkinta ya kubce mishi, ido ya zaro da sauri lokacin da yaga motar tashi ta nufi kan Nuruddeen gadan-gadan
ji kakeyi k'uuuuuiyyyyhh.
motarnan ta bugu machine d'in Nuruddeeen bugu mai tsanani wanda yasa, Nuruddeen yayi tsalle yayi sama kana ya fad'o kan bump d'in tsakiyar titin,
"Innalillahi'wa'illaihi rajiun. Hasbunallahu wani'imal wakil."
Shine abinda tarin mutanen dake zageye da Nuruddeen suke fad'i,
yayinda wasu suka ma kasa mgna sai d'aura hannu sukayi a kai, kana wasu sai jujjuya kai sukeyi.
mai mota kuwa da ker ya samu ya fara sarrafa motar har ya samu ta tsaya,
yana fitowa da gudu ya nufi inda dandazon mutanen suke,
kutsawa yayi tayi tsakiyar mutanen har ya samu ya isa,
ido ya rumtse da k'arfi cikin tsananin fargaba ya sunkuyo kan Nuruddeen da yake konce lib bisa titi, ida nunshi a rufe kirib sai numfashin shi dake korar juna,
da sauri ya tallaboshi tare dagowa ya kalli mutanen cikin tashin hankali yace.
"Ku taimaka min mana in d'agashi in sashi a mota."
wani k'ak'k'arfan matashi ne,
yayi maza ya sunkuyo ya ciccibi Nuruddeen kana cikin, d'aga murya yace.
"Biyoni."
yana fad'in haka ya juya ya tsallaka titin zuwa d'aya hannun kana ya nufi cikin asibitin MUSABA dake fuskantar tashan Dukkun,
cikin rawan jiki mutumin ya mik'e kana yabi bayanshi.
suna shiga Reception suka nufa,
ganin sun shigo hajaram majaram yasa Nurse's yin kansu da tambayar meke faruwa,
cikin kad'uwa mutumin nan yace,
"Accident ne ku taimaka doctor ya dubashi."
juyawa sukayi suka kalli juna, kana d'aya daga cikinsu tace.
"Ko an gayawa doctor bazai dubashi ba sai an nemo police."
jin haka yasa mutumin nan juyawa da sauri ya fita,
gudu-gudu sauri-sauri ya tsallaka titin kana ya nufi wurin motar tashi, yana shiga ya nufi Gombe division yana zuwa ya musu bayanin abinda ke faruwa,
ba b'ata lokaci suka had'ashi da police d'aya, kana suka tafi tare,
suna zuwa Doctor in ya amsheshi bisa sa hannun hukuma kana fara bashi taimakon gaggawa, sannan daga bisani ya ce su tafi Medical Center.
Ba b'ata lokaci suka amshi shawararshi suka tafi can,
suna zuwa aka amsheshi.
shi kuwa police yasa d'aya police d'in yaje ya d'auki machine d'n nashi ya kaishi officensu.
kana sun samu wayarshi y'ar Nokia dake jikinshi tanan aka kira Bappa Ali aka sanar mishi meke faruwa.