Sashe 105
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
K'arfe uku ta dawo daga billiri kai tsaye gidan radio nasu ta nufa,
a nan tayi sallan la'asar, sannan ta zauna jiran lokacinta,
tana zaune anan Bilkisu ta shigo ita da Manager d'insu tana ganin Zaleeha ta kwashe da dariyar shak'iyanci cikin ingizarwa tace.
"Hajiyar nakasassu ina mutanen naki ne? Koda yake amaryar nakasashen gurgu kurma zance ko."
cikin tsananin takaici Zaleeha ta watsa mata harara tare da cewa.
"A a uwar nakasashe zakice ba amryar nakasashe ba wlh mai gado bana so ki daina had'ani da wannan musakin."
cikin Shek'iyanci bilkisu ta iso gareta tare da cewa.
"Sorry baza k'araba, amman mutanen nakine da abin dariya."
juyawa tayi ta fita tabi bayan Manager ita kuwa Zaleeha Raveel ta kalla wanda yake mik'o mata sweet amsa tayi tare da cewa.
"Ngd."
kai ya gyad'a mata tare da cewa.
"Kada ki sake aibata nakasassu dan duk wanda bai mutuba ba'a gama mishi halittaba.
da kullum haka kike gaya min to meyasa kawai dan nakasasshe yace yana sonki sai ki juye daga Mai kakkyawar alaƙa i zuwa mummunar ɗabi'a, kada ki bari imaninki ya samu rauni."
kai ta gyaɗa mishi sannan ta juya ta nufi ɗakin gabatar da shirin nata ganin lokacinta yayi.
Mama kuwa da Zahira sosai zugar Ruda yayi tasiri a kwanyarsu da yake dama zuciyar ba inganci.
Ƙarfe huɗu dai-dai suka dawo daga doho,
suna shiga gidan kai tsaye side d'in Baba malam suka nupa,
a parlour suka sameshi shida Ya Ahmad da Ya Habu, sai Mamy dake haɗa musu tea a kofuna.
sannu da hanya sukayi musu, fuskarnan kamar zatayi ruwan jini Mama ta amsa musu kana ta gaida Baba malam,
sannan Ahmad da Habu suka gaidata,
Zahira kuma duk ta gaidasu sannan ta wuce cikin gidan tayi shashin maman.
Ita kuwa Mama a hankali ta mik'e ta fita ganin duk basubi ta kantaba,
to wazai kulata yadda taketa harare-harare,
tana fita ta nufi Side d'inta da yake tsab Maryam da Aunty Lubna sun gyarashi jiya da dare.
A parlour ta zauna,
dai-dai lokacin kuma Zahira ta fito daga bedroom d'in Maman a guje,
ganin Maman a parlour yasata tsayuwa cikin rawan jiki da halin fitina tace.
"Mama zo zo zo kiga wani abu a bedroom naki."
tsaki ta d'an ja tare da cewa.
"Menene kike wani zaro idanu haka?."
hannun uwar ta kamo tare da cewa.
"Mama zo ki gani mana an cika miki d'aki da akwatuna dasu buhunan gishiri dasu goro."
ido ta zaro gaba d'aya tare da cewa.
"Akwa tuna kuma to na meye."
cikin hatsabibanci tace.
"To waya sani ko lefen Anty Zaleeha aka kawo."
ai kafin ta rufe bakima Mama ta kutsa kai cikin bedroom ɗin.
wani irin wawan birki taja tare da cewa.
"To wanna kuma daga ina, to ko Abdussalam ne da tace mishi a turo komanshi Zaleeha ta yarda dashi, tuni ya turo ɗin,
sai kuma ta girgiza kai ina sam ba shi bane ai in shine zai gaya mata, shida kuma ɗazu suka gama mgna,
cikin tafasan bala'i tace to waye.
Sai kuma ta dawo parlour da sauri cikin karad'i da kware murya baki d'aya ta fara rabkawa Habu kira.
"Habu! Habu!! Habu!!! Habuuuu!."
da sauri ya iso cikin parlourn a tsorace yace.
"Na'am Mama ganifa nazo."
A hatsale tace.
"To dan ubanka meyasa bazaka amsa da kyau ba."
cikin had'e fuska yace, "Na'am." cikin yamutsa fuska tace.
"Wancan kayan fa na meye ne."
Kai tsaye yace.
"Lefen Zaleeha aka kawo jiya."
cikin ɗaga sauti tace waye kawo lefen?."
A dake yace.
"Wasu mata ne."
zaburowa tayi kanshi tare da cewa.
"Dan ubanka ba wanda suka kawo nake tambaya ba wanda aka kawowa nake nufi."
cikin kauda kai yace.
"Zaleeha aka kawowa."
wani dogon tsaki taja tare da jawo hannunshi tace.
"Kai mahaukacin inane wanne saurayin ne ya aiko lefen."
Cikin dakiya da rashin tsoro yace.
"Saifuddeen."
wani irin zabura tayi tare da buga tsalle tace.
"Inji uban waye ya basu damar kawo banzayen lefen wanna musakin d'an nasu?."
Yana fita yace.
"Inji Baba Malam mana Baban Zaleeha shine ya basu dama."
wani irin kware murya tayi tare da yin sauri ta nufi parlour Baba malam tana shiga parlour tare da masifa murya a hargitse tace.
"Lallai yau za'a sabunta yaƙin duniya....!
*Dan Allah da manzonsa ku dena fitarmin da littafi,*
By
*GARKUWAR FULANI*
8/
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 30*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
"Lallai yau za'a sabunta yaƙin duniya na biyu".
Fuska ta ƙara haɗewa tamkar wacce akayiwa bushara da mummunan al'kaba'in rayuwar duniya.
Ido suka zuba mata baki ɗayansu, tare da maida hankalinsu gareta.
Cikin takaici da tashin hankali tace.
"Meyasa! Meyasa haka ne malam? Ina dalilin kullum sai an sani baƙin ciki kan aurar da ƴaƴana?."
Kauda kanshi yayi daga kallon mummunar fuskarta tare da maida dubanshi ga al'ƙiblah, a hankali yaci gaba da tasbihi da yakeyi.
"Subahallahi, walhamdulillahi, wa la'ilahalillahu, wallahu akhbar."
haka yaketa mai-maitawa tare da motsa yatsun hannunshi na dama, kana yana ɗan karkaɗa ƙafafunshi dake miƙe bisa table ɗin dake gabanshi a hankali a hankali.
idonshi ya rumtse da ƙarfi jin Mama na cewa.
"Wallahi-Wallahi bazan taɓa yarda a zalumunci Zaleeha irin yadda aka zalumci Maryam ba, akan wani dalili zai sa baza'a sakarmin rayuwar yarana ba, suma su auri wanda sukeso sai ayi ta musu cushe da auren dole ina dalili? to Wallahi muddin ina raye, Wallahi bazan taɓa lamunta Zaleeha ta zauna da wannan banzan nakasasshen kurma kuma gurgun, da kuka yayibo zaku liƙa mata ku kashe mata rayuwa ba,
haka kawai dan an iya min kisan mummuƙe, shine za'a nunamin wariyar launin fata, a nuna min ni bare ce to Wallahi ban amince ba!."
Cikin gajiya da ihu da hayagagar da take musu Ya Ahmad ya ɗan tanƙwashe sawunshi tare da cewa.
"Mama ai Zaleeha ita ta kawo shi, zaɓinta ne ita ta amince dashi babu wanda ya mata dole,
itace ta amince tasa ya turo iyayenshi."
Cikin tsawa tace.
"Rufe min baki, kaima ae munafuki ne, ban nemi jin ta bakinka ba, da ubanka nake magana,
karka wani karkace kace zaka meda laifin kan Zaleeha, munafurcin banza kawai."
Rumtse idanu Ya Ahmad yayi, cikin takaicin abinda Mama'n kewa mahaifin nashi yace.
"Allah ya huci zuciyarki."
A hasale tace.
"Wannan karon dai zuciyar tawa ba zata huce ba, Wallahi bazan taɓa lamunta da batun ƴata ta auri musakiba,
dan rainin hankalin yarinya da kyawunta da ƙimarta tanada masoya gabas da yamma kudu da arewa amman a rasa wanda za'a zaɓa mata sai nakasasshe, wulaƙantacce wanda ko magana bayaji!."
Tafaɗa ranta amatuƙar ɓace domin sosai zuciyarta ke tafasa.
Duk ihu da hargowan da takeyi Baba Malam bai sake ɗaga ido ya kalleta ba, sai ma tasbihi da yakeyi ga mahaliccinsa da ya jarabceshi da auran wanna mata mai munanan al'adu.
Mamy kuwa wayarta ta jawo kana ta fara karanta Dua Azkar.
Ganin haka shima Ahmad sai yasa hannu ya ɗauki ɗan madai-daicin Qur'Ani'n dake gefenshi ya buɗe ya fara karatu ahankali cikin suratul. Kahf kasan cewar yammacin Jummu'a ne.
Habu ne ya shigo parlour'n a hankali ya nufi gefen mahaifin nasu ya zauna kusa da ɗan uwan shi Ahmad,
ido ya rumtse da ƙarfi yana mai jin takaicin hali irin na mahaifiyar tashi,
cikin sanyin sauti yace.
"Ya salam! Dan Allah Mama kiyi haƙuri ki bar yin ihun nan, kowa yanayin abinda zai samar mishi lada ke kuma kinzo kina tarawa kanki zunubi kina ɗaga harshenki sama dana mijink..."
Da sauri ya haɗiye rogowar maganar tashi, sakamakon jin Maman ta kai mishi wani uban bugu kan bakinshi.
"Habu kayi asara Wallahi, kai dai ka banunka da baka da kishin mahaifiyarka!." Takuma faɗa a hasale.
Baba Malam ne ya miƙe tsaye, tare da kallon yaran nashi cikin kamala da cikar haiba yace.
"Kuyi al'awala mu tafi masalaci lokacin sallah ya gabato."
Da sauri suka mimmiƙe tare da cewa.
"To."
Haka duk sukaje suka sabunta al'wala kana suka tafi zuwa masallaci.
Mamy ma tuni tayi side ɗinta, inda ta samu Aunty Lubna a parlour tana sawa ƴarta hijabi alamun zatayi salla ne.
"Barka da shigowa Mamy."
cikin nitsuwa da mutuntaka Mamy tace.
"Barka dai Lubna ya gajiyar kitchen? na tafi na barki ke ɗaya da aiki niƙi niƙi ko."
Kai ta rausayar tare da cewa.
"Tun ɗazu na gama ai Mamy aikin ba yawa."
"Masha Allah! Allah Ya saka da al'khairi, ya baki surkai masu miki fiye da abinda kike min."
"Amin Amin" Aunty Lubna ta amsa cikin jin daɗi, kana tayi side ɗin da nanne masauƙinsu duk lokacin da sukazo Gombe dan ita da Mamy tamkar uwa da ƴarta haka suke.
Ita kuwa Mama ta cika tayi tam sai ihu da haushi takeyi ita kaɗai kamar karya.
"Watoma mahaukaciya suka medani? sun watse sun barni wato inyi ta haushi ni ɗaya ko, tam zanyi maganinku, Wallahi gaba ɗaya saikunji aranku cewa inama da ace bakuyi ganganci ƙulla wannan haɗin ba, saina sanya baƙinciki acikin zuciyoyinku, kuma sannan saina saku danasani marar yankewa, badai dani kuke wasan ba, hmmm Wallahi zakusan kun taɓo cikakkiyar ƙaɓila Batangali da surkin bateriya, akan auren nan babu wanda zan ɗagawa ƙafa!!."
Tana gama faɗin haka ta juya fuuuuu kamar kububuwa tafice daga cikin falon na Baba Malam.
Tana shigowa falonta ta soma afkawa Zahira ƙira,
da sauri Zahira ta fito daga cikin ɗakinsu tana cewa.
"Na'am Mama."
A harzuƙe tace.
"Zo zonan mu kwashi ƴan iskan kayayyakin nan mu watsasu waje, Wallahi bazasu kwanar min a ɗaki ba gayyar tsiya!."
Da sauri Zahira tace "To."
Nan suka shiga cikin ɗakin, haka suka dinga ibo akwatunan nan masu kyaun gaske, suna watsasu a tsakiyar farfajiyar gidan,
wai don ma kasancewar Mama ƙaƙƙarfar mace ce shiyasa kab ta iya jidon manyan akwatunan, tanayin waje dasu harda su gishiri da goron bata bari ba, ranta yakai ƙololuwa wajen tafasa, jin kanta take dai-dai da uban kowa, jira take wani yace mata cass tuni zata sullesa tas.
Saida ta gama watsasu a tsakiyar gidan, sannan ta koma cikin ɗakinta tana haki tamkar wacce tayi dambe ta gaji.
Al'wala tayi sannan tazo ta kabbara niyar sallan magriba, wanda tuni lokaci ya ƙure mata, don har an riga da anƙirayi sallan isha.
a nan tayi sallan la'asar, sannan ta zauna jiran lokacinta,
tana zaune anan Bilkisu ta shigo ita da Manager d'insu tana ganin Zaleeha ta kwashe da dariyar shak'iyanci cikin ingizarwa tace.
"Hajiyar nakasassu ina mutanen naki ne? Koda yake amaryar nakasashen gurgu kurma zance ko."
cikin tsananin takaici Zaleeha ta watsa mata harara tare da cewa.
"A a uwar nakasashe zakice ba amryar nakasashe ba wlh mai gado bana so ki daina had'ani da wannan musakin."
cikin Shek'iyanci bilkisu ta iso gareta tare da cewa.
"Sorry baza k'araba, amman mutanen nakine da abin dariya."
juyawa tayi ta fita tabi bayan Manager ita kuwa Zaleeha Raveel ta kalla wanda yake mik'o mata sweet amsa tayi tare da cewa.
"Ngd."
kai ya gyad'a mata tare da cewa.
"Kada ki sake aibata nakasassu dan duk wanda bai mutuba ba'a gama mishi halittaba.
da kullum haka kike gaya min to meyasa kawai dan nakasasshe yace yana sonki sai ki juye daga Mai kakkyawar alaƙa i zuwa mummunar ɗabi'a, kada ki bari imaninki ya samu rauni."
kai ta gyaɗa mishi sannan ta juya ta nufi ɗakin gabatar da shirin nata ganin lokacinta yayi.
Mama kuwa da Zahira sosai zugar Ruda yayi tasiri a kwanyarsu da yake dama zuciyar ba inganci.
Ƙarfe huɗu dai-dai suka dawo daga doho,
suna shiga gidan kai tsaye side d'in Baba malam suka nupa,
a parlour suka sameshi shida Ya Ahmad da Ya Habu, sai Mamy dake haɗa musu tea a kofuna.
sannu da hanya sukayi musu, fuskarnan kamar zatayi ruwan jini Mama ta amsa musu kana ta gaida Baba malam,
sannan Ahmad da Habu suka gaidata,
Zahira kuma duk ta gaidasu sannan ta wuce cikin gidan tayi shashin maman.
Ita kuwa Mama a hankali ta mik'e ta fita ganin duk basubi ta kantaba,
to wazai kulata yadda taketa harare-harare,
tana fita ta nufi Side d'inta da yake tsab Maryam da Aunty Lubna sun gyarashi jiya da dare.
A parlour ta zauna,
dai-dai lokacin kuma Zahira ta fito daga bedroom d'in Maman a guje,
ganin Maman a parlour yasata tsayuwa cikin rawan jiki da halin fitina tace.
"Mama zo zo zo kiga wani abu a bedroom naki."
tsaki ta d'an ja tare da cewa.
"Menene kike wani zaro idanu haka?."
hannun uwar ta kamo tare da cewa.
"Mama zo ki gani mana an cika miki d'aki da akwatuna dasu buhunan gishiri dasu goro."
ido ta zaro gaba d'aya tare da cewa.
"Akwa tuna kuma to na meye."
cikin hatsabibanci tace.
"To waya sani ko lefen Anty Zaleeha aka kawo."
ai kafin ta rufe bakima Mama ta kutsa kai cikin bedroom ɗin.
wani irin wawan birki taja tare da cewa.
"To wanna kuma daga ina, to ko Abdussalam ne da tace mishi a turo komanshi Zaleeha ta yarda dashi, tuni ya turo ɗin,
sai kuma ta girgiza kai ina sam ba shi bane ai in shine zai gaya mata, shida kuma ɗazu suka gama mgna,
cikin tafasan bala'i tace to waye.
Sai kuma ta dawo parlour da sauri cikin karad'i da kware murya baki d'aya ta fara rabkawa Habu kira.
"Habu! Habu!! Habu!!! Habuuuu!."
da sauri ya iso cikin parlourn a tsorace yace.
"Na'am Mama ganifa nazo."
A hatsale tace.
"To dan ubanka meyasa bazaka amsa da kyau ba."
cikin had'e fuska yace, "Na'am." cikin yamutsa fuska tace.
"Wancan kayan fa na meye ne."
Kai tsaye yace.
"Lefen Zaleeha aka kawo jiya."
cikin ɗaga sauti tace waye kawo lefen?."
A dake yace.
"Wasu mata ne."
zaburowa tayi kanshi tare da cewa.
"Dan ubanka ba wanda suka kawo nake tambaya ba wanda aka kawowa nake nufi."
cikin kauda kai yace.
"Zaleeha aka kawowa."
wani dogon tsaki taja tare da jawo hannunshi tace.
"Kai mahaukacin inane wanne saurayin ne ya aiko lefen."
Cikin dakiya da rashin tsoro yace.
"Saifuddeen."
wani irin zabura tayi tare da buga tsalle tace.
"Inji uban waye ya basu damar kawo banzayen lefen wanna musakin d'an nasu?."
Yana fita yace.
"Inji Baba Malam mana Baban Zaleeha shine ya basu dama."
wani irin kware murya tayi tare da yin sauri ta nufi parlour Baba malam tana shiga parlour tare da masifa murya a hargitse tace.
"Lallai yau za'a sabunta yaƙin duniya....!
*Dan Allah da manzonsa ku dena fitarmin da littafi,*
By
*GARKUWAR FULANI*
8/
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 30*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
"Lallai yau za'a sabunta yaƙin duniya na biyu".
Fuska ta ƙara haɗewa tamkar wacce akayiwa bushara da mummunan al'kaba'in rayuwar duniya.
Ido suka zuba mata baki ɗayansu, tare da maida hankalinsu gareta.
Cikin takaici da tashin hankali tace.
"Meyasa! Meyasa haka ne malam? Ina dalilin kullum sai an sani baƙin ciki kan aurar da ƴaƴana?."
Kauda kanshi yayi daga kallon mummunar fuskarta tare da maida dubanshi ga al'ƙiblah, a hankali yaci gaba da tasbihi da yakeyi.
"Subahallahi, walhamdulillahi, wa la'ilahalillahu, wallahu akhbar."
haka yaketa mai-maitawa tare da motsa yatsun hannunshi na dama, kana yana ɗan karkaɗa ƙafafunshi dake miƙe bisa table ɗin dake gabanshi a hankali a hankali.
idonshi ya rumtse da ƙarfi jin Mama na cewa.
"Wallahi-Wallahi bazan taɓa yarda a zalumunci Zaleeha irin yadda aka zalumci Maryam ba, akan wani dalili zai sa baza'a sakarmin rayuwar yarana ba, suma su auri wanda sukeso sai ayi ta musu cushe da auren dole ina dalili? to Wallahi muddin ina raye, Wallahi bazan taɓa lamunta Zaleeha ta zauna da wannan banzan nakasasshen kurma kuma gurgun, da kuka yayibo zaku liƙa mata ku kashe mata rayuwa ba,
haka kawai dan an iya min kisan mummuƙe, shine za'a nunamin wariyar launin fata, a nuna min ni bare ce to Wallahi ban amince ba!."
Cikin gajiya da ihu da hayagagar da take musu Ya Ahmad ya ɗan tanƙwashe sawunshi tare da cewa.
"Mama ai Zaleeha ita ta kawo shi, zaɓinta ne ita ta amince dashi babu wanda ya mata dole,
itace ta amince tasa ya turo iyayenshi."
Cikin tsawa tace.
"Rufe min baki, kaima ae munafuki ne, ban nemi jin ta bakinka ba, da ubanka nake magana,
karka wani karkace kace zaka meda laifin kan Zaleeha, munafurcin banza kawai."
Rumtse idanu Ya Ahmad yayi, cikin takaicin abinda Mama'n kewa mahaifin nashi yace.
"Allah ya huci zuciyarki."
A hasale tace.
"Wannan karon dai zuciyar tawa ba zata huce ba, Wallahi bazan taɓa lamunta da batun ƴata ta auri musakiba,
dan rainin hankalin yarinya da kyawunta da ƙimarta tanada masoya gabas da yamma kudu da arewa amman a rasa wanda za'a zaɓa mata sai nakasasshe, wulaƙantacce wanda ko magana bayaji!."
Tafaɗa ranta amatuƙar ɓace domin sosai zuciyarta ke tafasa.
Duk ihu da hargowan da takeyi Baba Malam bai sake ɗaga ido ya kalleta ba, sai ma tasbihi da yakeyi ga mahaliccinsa da ya jarabceshi da auran wanna mata mai munanan al'adu.
Mamy kuwa wayarta ta jawo kana ta fara karanta Dua Azkar.
Ganin haka shima Ahmad sai yasa hannu ya ɗauki ɗan madai-daicin Qur'Ani'n dake gefenshi ya buɗe ya fara karatu ahankali cikin suratul. Kahf kasan cewar yammacin Jummu'a ne.
Habu ne ya shigo parlour'n a hankali ya nufi gefen mahaifin nasu ya zauna kusa da ɗan uwan shi Ahmad,
ido ya rumtse da ƙarfi yana mai jin takaicin hali irin na mahaifiyar tashi,
cikin sanyin sauti yace.
"Ya salam! Dan Allah Mama kiyi haƙuri ki bar yin ihun nan, kowa yanayin abinda zai samar mishi lada ke kuma kinzo kina tarawa kanki zunubi kina ɗaga harshenki sama dana mijink..."
Da sauri ya haɗiye rogowar maganar tashi, sakamakon jin Maman ta kai mishi wani uban bugu kan bakinshi.
"Habu kayi asara Wallahi, kai dai ka banunka da baka da kishin mahaifiyarka!." Takuma faɗa a hasale.
Baba Malam ne ya miƙe tsaye, tare da kallon yaran nashi cikin kamala da cikar haiba yace.
"Kuyi al'awala mu tafi masalaci lokacin sallah ya gabato."
Da sauri suka mimmiƙe tare da cewa.
"To."
Haka duk sukaje suka sabunta al'wala kana suka tafi zuwa masallaci.
Mamy ma tuni tayi side ɗinta, inda ta samu Aunty Lubna a parlour tana sawa ƴarta hijabi alamun zatayi salla ne.
"Barka da shigowa Mamy."
cikin nitsuwa da mutuntaka Mamy tace.
"Barka dai Lubna ya gajiyar kitchen? na tafi na barki ke ɗaya da aiki niƙi niƙi ko."
Kai ta rausayar tare da cewa.
"Tun ɗazu na gama ai Mamy aikin ba yawa."
"Masha Allah! Allah Ya saka da al'khairi, ya baki surkai masu miki fiye da abinda kike min."
"Amin Amin" Aunty Lubna ta amsa cikin jin daɗi, kana tayi side ɗin da nanne masauƙinsu duk lokacin da sukazo Gombe dan ita da Mamy tamkar uwa da ƴarta haka suke.
Ita kuwa Mama ta cika tayi tam sai ihu da haushi takeyi ita kaɗai kamar karya.
"Watoma mahaukaciya suka medani? sun watse sun barni wato inyi ta haushi ni ɗaya ko, tam zanyi maganinku, Wallahi gaba ɗaya saikunji aranku cewa inama da ace bakuyi ganganci ƙulla wannan haɗin ba, saina sanya baƙinciki acikin zuciyoyinku, kuma sannan saina saku danasani marar yankewa, badai dani kuke wasan ba, hmmm Wallahi zakusan kun taɓo cikakkiyar ƙaɓila Batangali da surkin bateriya, akan auren nan babu wanda zan ɗagawa ƙafa!!."
Tana gama faɗin haka ta juya fuuuuu kamar kububuwa tafice daga cikin falon na Baba Malam.
Tana shigowa falonta ta soma afkawa Zahira ƙira,
da sauri Zahira ta fito daga cikin ɗakinsu tana cewa.
"Na'am Mama."
A harzuƙe tace.
"Zo zonan mu kwashi ƴan iskan kayayyakin nan mu watsasu waje, Wallahi bazasu kwanar min a ɗaki ba gayyar tsiya!."
Da sauri Zahira tace "To."
Nan suka shiga cikin ɗakin, haka suka dinga ibo akwatunan nan masu kyaun gaske, suna watsasu a tsakiyar farfajiyar gidan,
wai don ma kasancewar Mama ƙaƙƙarfar mace ce shiyasa kab ta iya jidon manyan akwatunan, tanayin waje dasu harda su gishiri da goron bata bari ba, ranta yakai ƙololuwa wajen tafasa, jin kanta take dai-dai da uban kowa, jira take wani yace mata cass tuni zata sullesa tas.
Saida ta gama watsasu a tsakiyar gidan, sannan ta koma cikin ɗakinta tana haki tamkar wacce tayi dambe ta gaji.
Al'wala tayi sannan tazo ta kabbara niyar sallan magriba, wanda tuni lokaci ya ƙure mata, don har an riga da anƙirayi sallan isha.